Skip to content

Chapter 28

Chapter 28

Kallon Kitse Book One Complete Hausa Novels 1,199 words 0 views Progress saved
Download Book

cikin da ku ma da ke yan uwana ba ku ba ni shi ba kafin zuwan ta rayuwa ta, dan haka in dai har ku na son zama da ni to dole harshenku ya san me zai dinga fad'a akan mata ta." Ya na fita Hajia ma ta mu su fad'a sosai tare da tuna mu su baya, daga ranar kuma ba su sake yarda sun b'ata Khadija ba a gaban iyayen su bare kuma Usman, amma abin takaicin shine k'iyayyar da su ke ma Khadija sai ta shafi har Bilal, dan yanda su ke ganin Bilal na wahalar da mahaifin shi, yaro ya zama saurayi amma kamar k'aramin yaro, ba ma in sun had'u da shi gidansu Hajia, ya kan zo da kayan ciye ciye ma su tsada da kyau da dad'i, duk abincin da za'a mi shi tayi ba zai ci ba, haka mahaifin su malam Ali zai dinga biyewa yaron ya na siyo mi shi duk abin da ya ke son ci, to fa ana hakane har Allah ya had'a Usman da Haseenah, lokacin ya na yawan zuwa wajen wani shago da ke can wajen filin kokawa saboda wasu kaya da ya ke kawowa mai shagon, a nan ya had'u da Haseenah wacce a lokacin ta samu exam (brève) d'in ta ta na zaune gida, baban ta ne ya tilasta mata komawa makarntar islamiyya dan ta k'ara samun ilimin addini, a lokacin har nik'abi take sakawa da dogon hijab, wannan nutsuwa da hankalin na tane su ka sa Usman jin kamar ya samu wata Khadija, fatan shi shine ta zama kamar yanda ya ke tunani, bayan ya yi tambaya a kan ta an fad'a mi shi yarinyar kirki ce daga gidan mutanen k'warai, sai kawai ya gabatar da kan shi a matsayin yana son auren ta, duk da bai cika magana akan matar shi ba, amma ya fad'a mata ya na da mata d'aya da yaro d'aya, kuma ya na matuk'ar son su, a lokacin da su ka fara soyayya Usman na bata lokaci wajen waya da Haseenah har dare, sannan duk abin da ta yi ya kan yaba hakan kamar d'abi'ar shi ce, amma a tunanin Haseenah matar shi ba ta da kulawa ne shi ya sa har za ta yarda ya na waya da ita tsawon dare ko ya na gari, abin da kuma ba ta sani ba shine duk lokacin da ya ke wayar da ita to ba ya gida, Khadija kuma ba ta damuwa saboda ta san in baya gida yana tare da su Murtala, ta na ba shi lokaci sosai da ya ke jin dad'in rayuwar shi shima kamar yanda ya ke wuni tare da ita da safe har zuwa yamma, ko kwalliya ta yi taji yana kod'ata sai tace wai uwar gidan shi ba ta yi shi ya sa idan ya ganta da kwalliya kamar ya ga matar aljanna, hakan ya sa ta sawa ranta ta na zuwa gidan za ta cinye yak'in ba tare da tasha wahala ba, amma kuma gashi Mariya ta kawo mata wani labari da ya sa har ta fara had'awa da malamai. _Toh, ko tunanin Usman ya fad'a mi shi daidai? Shin Haseenah za ta zama kamar yanda ya d'auka? Ko kuma dai *kallon kitse ne ya ma rogo*?_ *Mu koma labari* Ko da ya dawo daga kan Bilal kai tsaye falon shi ya wuce, sak'o ya turowa Khadija ta same shi falo haka ma Haseenah da ke d'akin ta, hakimcewa ya yi ya na jiran zuwan su, (da alama Usmanu yan mulkin sun motsa, yau kam duk wacce ta yi wasa za ta gane shayi ruwa ne 😉), kusan a tare su ka shigo falon sai Khadija da ta k'ara da sallama, zaune su ka yi su na fuskantar shi su na kallon shi, d'ago kan shi ya yi ya kalli Haseenah ya kalli Khadija kafin yace "Kun gaisa ne da safen nan?" Khadija da tasan waye mijinta ne ta yi saurin cewa "Sosai ma, har falo ta same ni ai, mun gaisa da ita." "Da kyau." Ya fad'a ba annuri kafin ya d'ora da "Ku zuba mana abinci mu ci." Satar kallon shi Khadija ta yi dan tasan ya same ta tana karin kummalon ta, amma jin haka daga bakin shi da kuma ganin yanayin shi ya sa tasan yau ba ya yanayin wasa, dan haka ta mik'e tare da Haseenah da ke ta wani yauk'i kamar za ta karye, murmushi ta mata tace "Kinga amarya zauna, ki zauna zan zuba." Ci gaba ta yi da zuba ma kowa har ta gama ta aje farantin a gaban shi kafin ta matso kujerar ta kusa da shi, sai da ya fara saka hannu tare da bismillah sannan su ma suka saka, Haseenah dama haushi ne kamar ya kashe ta, Khadija kuma a k'oshe take neman agaji take, a tare su ka cire hannun su suna kallon shi, shi ma kallon su ya yi yace "Me ku ke nufi?" Cikin wata shegiyar shagwab'a Khadija tace "Mun k'oshi." Duk daba kuzari a tare da shi sai da ya murmusa yace "Ku na nufin ni kad'ai za ku bari? Ai ba ku isa ba, dan haka ku mayar da hannuwan ku." Kamar za ta fashe da kuka ta shafa cikin ta tace "Ciki na fa zai fashe, ka ci kawai sai ka had'a da nawa ka ci." Sama da k'asa ya harare ta yace "Sannu mai wayo, kenan ni na cika cikin nawa? To na k'i wayon." Mik'ewa ta yi tace "To bari na je na amaye wanda na ci sai na dawo mu ci gaba ko?" Da gayya Khadija ta dinga tafiya ta na wani juya k'ugunta, mazaunan ta na kad'awa yanda su ke so, sai da ta kai k'ofar fita ta juyo ta kalle shi dan dama a sanin da tawa mijinta ba ta ba da baya bai bita da kallo ba, su na had'a ta ga ya wani saki baki ya na kallon ta, cije leb'e ta yi ta kashe ma sa ido d'aya ta fice da murmushi, Haseenah Usman ta bi da kallo ganin ya wani wagale baki har da rumgume hannaye ya na kallon ta, sai da yaga ficewar Khadija ya sauke wata sayayyar ajiyar zuciya da murmushi a fuskar shi wanda shi kad'ai ya san ma'anar shi, a hankali ya zuro hannun shi cikin farantin da nufin ci gaba da cin abincin shi sai ya lura da Haseenah da ta kafe shi da ido, saita nutsuwar sa ya yi yace "Ya dai?" Ita ma had'e abin da ke ran ta tayi tace "Ranka shi dad'e, wai me ya sa aunty Khadija ke jin dad'in anfani da gilashi a kowane lokaci? Ba ta tsoron ta samu matsala a idon ta." Kallon ta ya yi ya na tunani, bayan gamsuwa da zuciyar shi sai kawai yace "Haseenah kema yanzu iyalin gidan nan ce, ba wani abu da za'a b'oye mi ki, Umman Bilal na fama da larurar ido ne, kuma anyi neman maganin amma har yanzu shiru ba labari, sai dai har yanzu ba mu cire rai da rahamar ubangiji ba, mu na sa rai wata rana za ta samu lafiya da yardar Allah." D'auke idon ta ta yi daga kan shi ta kalli

Table of Contents

Chapters

117 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115
  116. 116 Chapter 116
  117. 117 Chapter 117