Chapter 10
Chapter 10
nufi masallaci, Khadija na gama sallah da azkar d'in ta kwace ta koma ta yi dan bacci ta ke ji wanda ba ta yi ba, sai da gari ya waye Bilal su ka dawo tare da baban shi, d'akin amarya ya fara wucewa tun da ba ta san tsarin gidan na su ba, kwance ya same ta a kan sallaya ta na bacci, a hankali ya juya ya fita ya koma d'akin *Dije*, ita ma kwancen ya same ta ta na bacci, k'arfin hali ya yi ya tashe ta, ta na bud'a ido ta ya sakar mata murmushi yace "Ammien Bilal, ashe bacci ki ke? Na d'auka ki na madafa ai." Sai da ta d'auki gilashin ta kafin tace "Yin me a madafa?" Cikin murmushi yace "Yin girki mana, ko ba za ki mana abin karin kummalo ba? Kinsan fa bak'uwa ce da mu a gidan, watak'ila ita ta na karyawa da wuri ba kamar mu ba." Gyara zama ta yi tace "Sai kuma aka ce wannan ya zama matsala ta? Me ka ke so na yi? Na je na dafa mata abinci kenan ta ci? To ka yi hak'uri, ban da ra'ayin shiga madafa yau." Ta na fad'a ta tashi ta shiga ban d'aki, wanka ta yi dan baccin ma ya fita idon ta, Usman kam na fita ya wuce d'akin Haseenah ya d'auko makullin mota dan ya siyo abinci, a farfajiyar gida ya samu mai gadi ya bud'ewa k'anin shi k'ofa ya shigo, musabaha su ka yi kafin k'anin yace "Ango abinci fa Hajia ta ce na kawo mu ku." "Da gaske *Nura*? Kai amma Hajia ta kyauta wallahi, dan dama duka mutanen gidan a gajiye su ke." Dariya Nura ya yi yace "Lallai kam, to ko dai za ka d'auke ni ina dafa mu ku abinci har lokacin da za ku huta?" Hannu ya sa ya karb'i kwanukan ya na fad'in "Dallah ni bani nan ba na son shiririta." Mik'a mi shi ya yi yace "Dama ba na son shiga ciki saboda ban sanyo manyan kaya ba, kasan halin Dijen nan da son girma." Kai ya girgiza yace "Allah ya shirya da wannan son girman na ka, wai matar da ta zo gidan nan ka nada shekara biyar a duniya, tun fa ka na yawo ba wando ta ke tare da kai, amma yanzu har ka ke son bud'e mata ido." "Ni fa matsala ta da kai kenan, yanzu dai sai anjima, sai na zo cin tuwon amarya." Wucewa kawai ya yi ya shige ciki, ya na shiga a teburin cin abinci ya aje ya d'auko farantai ya jera sannan ya shiga ya taso Haseenah, tare su ka fito ta na sake k'arewa falon na shi kallo, ganin za su wuce teburin abincin ya sa ta tsaya ta na kallon shi, juyowa ya yi shi ma yace "Muje mana." Binshi ta yi su ka wuce, k'ofar falon Khadija ya bud'a ta shiga, saboda yawan turaren da akewa d'akin ya sa har ya kama d'akin sosai, a hankali Haseenah ta lumshe ido ta bud'e kai tsaye, rarraba ido ta fara ta na kallon ikon Allah, wai, masha Allah, tabbas ba k'arya falon ya had'u kuma ya tsaru sannan ya ga kaya, ba had'i kam nata falon da wannan falon, ta na ganin kyawun falon Usman, amma sai ta ga ashe na shi ma somin tab'i ne, takawa ta fara yi ta ji k'afafun ta ta lumewa cikin shinfid'add'en tappi da ke kai, ta na kallo ya k'wank'wasa k'ofar d'akin tun da ba shi kad'ai bane, amma a wajen Haseenah kawai mulkin da Khadija ke yi a gidan ne ya sa ba ya iya shiga d'akin sai ya nemi izinin ta, jin shiru ya sa ya bud'a a hankali ya lek'a, ganin ta ya yi zaune bakin madubi ta na shafa hoda (powder), "Mu shigo?" Shine abin da ya fad'a, ta na jin haka ta san ba shi kad'ai bane, dan haka ma ta saki murmushi tace "Ku shigo mana." K'arasa shiga su ka yi Haseenah na d'ard'ar da satar kallon d'akin, ko dan na ta d'akin sabbin kaya ne a ciki sai warin sabintaka su ke, hakan ya sa taji kamar ta yi kwance a d'akin Khadija, zaune ta yi kujerar da ke gefen kwabar saka kaya (wadrob) kanta k'asa, shi kuma tsaye ya yi gaban Khadija yace "Wannan kwalliya haka matar, wa ake ma ne?" Tsaye ta mik'e ta na gyara d'an kwalin ta ta juyo ta kalli Haseenah da fara'a tace "Amarya ke da kan ki?" Ita ma murmushin ta yi tace "Ina kwana?" "Lafiya lau amarya, kin tashi lafiya?" "Lafiya lau." Ta fad'a a tak'aice, da murmushi Khadija ta d'ora da "Ya kwanan bak'unta kuma? In ce dai kinyi bacci?" A birkice Haseenah ta kalli maganar Khadija, hakanne ya sa ta d'an d'ago ta kalle ta ido tsaye tace "Ai Abban Bilal bai barni na yi bacci ba, kin san shi da rigima." Kallon ta Khadija ta yi ta na wani murmushi irin na babba da yaro tace "Ke ma kenan da ki ka zo jiya, yanzu na san za ki fahimci k'ok'ari na akan mijin ki." Haseenah kam a zuciyar ta tsaki ta yi, Usman ne yace "To na ji, yanzu dai ai nine rigimammen ko? To nagode, yanzu ku wuce muje mu ci abinci." Cikin zolaya Khadija tace "Wai har ka gama girkin? Amma gaskiya ka yi sauri." Hararan wasa ya aika mata yace "Kin d'auka ke kad'ai ce gwana a fannin girki? To ni har lambar yabo aka ban, nuna miki ne ban yi ba saboda tsaro." Dariya ta yi tace "Ko dai saboda tsoron girki ba." Takawa ta fara yi tace "Muje to." Da sauri ya rik'o hannun ta ya mayar da ita gaban madubi ya bud'a ya d'auko wani k'aramin akwatin gilashi yace "Ki saka wannan ya na miki kyau." Da kan shi ya saka mata kafin suka wuce, Haseenah kuma kamar zuciyar ta za ta harba saboda bak'in kishi na banza da wofi, haka su ka zauna tare da Bilal a faranti d'aya su ka saka hannu dukan su, sai dai Khadija da Haseenah ba sosai su ke cin abincin ba, dan kowa da abin da ke ran shi, haka dai su ka gama ango ya shirya ya fita, amarya ta koma b'angaren ta. *Yau* ma dai sosai aka gwangwaje walimar damu, mutane sun sha anko gwanin ban sha'awa, haka aka yi abin da ya tara mutane sai dai sisin kwabo ko k'wayar gero Usman bai karb'a ba a hannun iyayen Haseenah, daga k'arshe dai tsofaffi da iyaye sun sake had'a kan Khadija da Haseenah sun mu su nasiha da jan kunne tare da gargad'i, a k'arshe kuma su ka bisu da addu'ar fatan zaman lafiya da kuma zuri'a mai albarka, haka yau ma taro ya watse in da kowa ya koma gefe dan a kalli kalar na su zaman, da dare ma Usman ya shigo tare da manyan aminan shi Alhaji *Murtala* da Alhaji *Adamu* mijin Salamatu, suma dai nasihar su ka sake mu su tare da fatan alkairi daga bisani su ka tafi. *Allah ya bada hak'urin zama da juna.* 05/01/2020 à 22:11 - 💋😘💋: 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ 💑💑💑💑💑💑💑💑💑💑 _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1*
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117