Chapter 43
Chapter 43
sunkuyowa ya yi ya lek'a fuskar ta yace "Iyeee! Kunya ce wannan? Kin tuna amarcin kenan? To shikenan bara ki gani." Tsakiyar maman ta ya tusa mata kud'in tare da sumbatar goshin ta yace "Ni na tafi sai na dawo." Sai da ya ksa kaiwa ga k'ofar fita ta d'ago tace "A dawo lafiya, godiyar kuma na mik'o ta zuwa wani lokacin." Yanda ta k'arashe maganar da fari ya sa ya saki murmushi yace "Ina jira, dan nasan abun zai k'ayatar tunda ke ce za ki yi shi." Ya na fita ta tashi ta k'arasa shirin ta, tare da Uwani su ka tafi a motar ta gidan kitso da lalle da ma sauran gyaran jiki, kasancewar babu mutane a wurin ya sa aka fara mata abin da ya kai ta, sun jima sosai a wajen, dan sai kusan k'arfe biyar na yamma su ka koma gida ita da Uwani, tun a hanya ta tsaya ta siye salade dan ta ci, su na zuwa gida Uwani ta shiga gyaren shi ita kuma ta shiga wanka, ko da ta gama shiri Uwani har ta fara yankawa, zaune ta yi su na hira su na aiki har magriba, kuma har lokacin ba ta ga Haseenah sai motsin ta da su ke ji a madafa, a haka duka suka gama aiyukan gaban su suka koma d'aki. Tunda wuri ta yi shirin baccin ta yau saboda ta huta dan gobe ita ce da aiki, doguwar rigar bacci ce a jikin ta da ta sauka har k'asa haka ma hannayen rigar, sanin Usman zai shigo ya sa ta k'i saka komai daga cikin rigar, ma'ana dai babu komai daga ciki bayan rigar, ai kam ta na jin motsin shi ta yi sauri ta mik'e ta fara kai da kawon iska, ya na bud'a k'ofar da sallama a bakin shi, da sauri ya d'ora da "Wai wai wai, kar dai na shigo lokacin da bai dace ba?" Juyowa ta yi da murmushi tace "Wane lokaci ne bai dace Abban Bilal ya ga Umman Bilal ba?" Takowa ya yi zuwa gaban ta ya na kallon ta yace "Ba na tunanin akwai lokacin gaskiya." "Kuma ka fad'a?" Ta fad'a da kafe shi da ido. Hannu ya kai zai kamo ta ta janye ta zauna kan gado ta na fad'in "Dama ina son magana da kai." Zaunawa ya yi ya na fad'in "Uhum, akan me?" Satar kallon shi ta yi tace "Akan maganar kwana ne dama." Da sauri ya kalle ta yace "Me ya faru da kwanan ki? Ina ce gobe ne ko?" Ajiyar zuciya ta sauke tace " Eh gobe ne, amma kuma da matsala." Gyara zama ya yi ya na kallon ta yace "Matsalar me? Ki yi magana mana dan kinsa hankali na ya fara tashi." Mik'ewa ta yi tsaye kamar marar gaskiya ta na kallon shi ta na wasa da yatsunta tace "Eh to, gaskiya dai ba na sallah, shi ya sa na barwa amarya kwanan na wa." "Me?" Ya fad'a ya na tashi tsaye, janyo ta ya yi jikin shi yace "In dai ba b'ata na yi ba ai tunani na lokacin zuwan bak'on ki baiyi ba, me zai sa ya canza lokacin zuwa yanzun? Saboda ya san ina buk'atar ki ne a kusa da ni kome? Ko shi ma haushi na ya ke ji ya na taya ki kishi ne?" Da sauri ta janye daga jikin shi ta yi baya ta na fad'in "A'a ba ko d'aya, gaskiya na ke fad'a ma ka fa, ka yarda mana." Had'e fuska ya yi yace "Naga tafin hannun ki." Da sauri ta mayar da hannayen baya tace "Um um." Murmushi ya yi yace "Wata kala ce kawai ki ke so ki min kuma na gano ki, dan haka ki ci gaba da min shirye shirye kawai." Juyawa ta yi ta nufi ban d'aki ta na fad'in "Ni fai na fad'a ma ka na barwa amarya kai, dan yanzu har na saba da bacci ni kad'ai." Har da gudu ya had'a wajen janyo ta jikin shi ya na shafa ta ya na fad'in "Kenan ba ki yi kewata ba ko kad'an?" Cikin narkakkun idon ta ta kalle shi ta gilashi tace "Idan ma na yi ko banyi ba, idan ka shigo hannu na za sani." A hankali ya matso kan shi ya na son had'e bakin su da sauri ta fizge daga gare shi, juyawa ta yi ta nufi ban d'aki ta na juya mazaunai da gayya, lumshe ido ya yi ya d'an cije lab'en k'asa ya bita da kallo, ta na shigewa ya matsa bakin k'ofar yace "Ni zan wuce sai da safe, ki kula min da kan ki dan Allah." Shiru ta yi har ya fice daga d'akin, ta na jin ya fita ta fito dan dama ba komai ta ke yi ba, kashe wuta ta yi ta zauna bakin gadon ta yi addu'o'in da ta saba yi kafin ta cire gilashin ta ta kwanta abin ta. ************** Bilal na zaune tare da duka iyayen shi yan uwan mahaifiyar shi da kuma kakar shi, dan har yanzu ba su daina had'uwa a falon mahaifiyar su ba suna hira, hira ce ta yi hira har ta sa Bilal fad'a mu su fad'an da mahaifiyar shi ta yi da kuma auntyn shi, rashin jin dad'in abun ya sa Naseer cewa "Ni wallahi dama nasan sai anyi haka, dan tun ranar da suka samu sab'anin nan nasan yarinyar nan ba ta da kunya, in ba rainin hankali ba taya za ki bud'e baki ki ce wai ina anfanin yaro a cikin gidan uban sa? Wallahi ta yi wasa ni sai na ci uban wanda ya d'aure mata gindi ma." Mama ce ta katse shi da cewa "Kamar ya ka ci uban ta? Matar mutane za ka daka har gidan ta? To ba na son sake ji daga yau, ku na so ace ku na taya 'yer uwar ku kishi ne?" Naseer d'in ne dai ya d'ora da "Hajia ba ki san me ta ke mata bane, ranar fa har kuka ta saka ta da hawaye, ce mata ta yi wai makauniya, ki ji fa Hajia, ni tunda na ke ban tab'a jin wanda ya kira ta da makauniya ba." Ashir ne yace "Makauniya fa? Khadijar ce makauniya?" "Wallahi haka ta fad'a mata shegiyar figaggiya." Habeeb da Bilal ke kwance kan k'afafun shi ne yace "Wallahi ni tun ran kan amarya da na ga idon yarinyar nan a tsaye da kuma k'awayen ta masu ido tsakar ka nasan dama za ayi haka, amma dai ta kiyaye b'atawa auta rai, dan ba lallai mu d'auka ba." Bashi ne ya karb'e da "Ba maganar ba lallai bane, magana ce ta ba zamu d'auka ba ko kad'an, wallahi ba za ta shiga gidan ta ba kuma ta nemi ta raina ta, dan haka dole Usman ya sake zagewa wajen tsayawa akan gidan shi, in ba haka ba kuma to zamu ziga ta ta dinga jibgar ta mu kuma a shirye mu ke da mu tsaya mata a kowace kotun duniya." Tsaki Mama ta yi ta mik'e ta nufi d'akin ta ta na fad'in "Saida safen ku, tunda naga dukan ku babu mai hankalin da zaiyi magana ta hankali har kai da ke babba a
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117