Chapter 30
Chapter 30
ni da kyau, daga yau ba na son sake ganin k'afar a madafar nan in har aiki na ne, in ba haka ba kuma zan ci uwar ki a gidan nan sannan na sa mai gida ya yi waje da ke, kinji ni ko?" Kai Uwani ta d'aga alamar ta ji, da hannu ta mata alama tace "Fitar min daga nan, k'azama kawai 'yar matsiyata." Kasancewar Uwan irin mutanen nan ne masu jin zafin magana, wanda da ka zage su yafi sauk'i ka yanke su da wuk'a, hakanne ya sa ta fito tana kuka tana jin k'una na kalmar 'yar matsiyata da ta yi da cewa za ta ci uwa ta, ta na nufowa falon Khadija ta tsinkaye ta, dan haka ta tashi da sauri ta nufe ta, sai da ta rumgume ta a jikin ta ta fara tambayar ta lafiya? Cikin kuka ta ke fad'in "Aunty amarya ce tace wai kar na sake shiga madafa in ta na aiki." Shiru Khadija ta yi tana sauke huci kafin ta d'ago Uwani daga jikin ta tace "Haka ta fad'a mi ki?" Kai kawai ta d'aga mata, d'orawa ta yi da "Shikenan Uwani yi hak'uri, yanzu ina indomien da na saki dafawa?" "Ta na can ta zube." Ta fad'a tana share hawaye da hijabin ta, da k'arfi tace "Ta zube kamar ya?" "Lokacin da ta mareni ne faranti ya sub'uce a hannu na ta zube." Da k'arfi ta dafe k'irji tace "Mari kuma? Ta mare ki fa ki ka ce?" Kai Uwani ta d'aga alamar eh, share mata hawayen fuskar ta ta yi tace "Wuce d'aki Uwani ina zuwa, zanji dalilin marin ki, in ba ta san darajar mutane ba ni na sani." Za ta wuce madafar Uwani ta rik'o hannun ta tace "Dan Allah aunty Khadija ki yi hak'uri, na yafe mata wallahi, ba na so saboda ni ku samu matsala." Fincike hannunta ta yi tace "Uwani kin tab'a ganin b'acin rai na?" "A'a." Ta fad'a har da girgiza kai, "To ki wuce d'aki kamar yanda na ce." Ta na fad'a ta nufi madafar a matuk'ar hassale, daidai lokacin kuma mai gadi ya bud'e k'ofa da motar Usman da ta motar Ashir ta danno ciki, Ashir na kusa da gidan ya ga motar usman, dan haka ya kira shi ya fad'a mi shi ya na tare da Bilal dan haka ya juyo su ka dawo. Khadija kam na shiga ta samu Haseenah ta wanke naman zabbi ta zuba a tukunya za ta kunna wuta, sai da ta tsallaka indomie da ke zube k'asa kafin ta isa gare ta, cikin gadara ta tsaya bayan ta tace "... _Wata yau za ta gane kuren ta fa._π *Allah ka sa mufi k'arfin zuciyar mu.* 21/01/2020 Γ 13:34 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *14* "Haseenah, Uwani ta fad'a min abin da ya faru, kuma har ta fad'a min ma wai kin mare ta, shin hakane?" Juyowa Haseenah ta yi cike da rainin wayo tace "Ki cire wai, gaskiya ne abin da ta fad'a, ko za ki rama mata ne? Sai ki tabbatar min yar aikin gida tafi matar gida." Wani murmushin gefen labb'a Khadija ta yi kafin tace "Ko kinsan kin mana b'arin abincin da yarima zai ci?" Ba tare da ta juyo ba tace "Ban san wani yarima ba a gidan nan, sai Bilal kawai, wanda na ke da tabbatacin ba shi kad'ai bane yaron da zai rayu a gidan nan, k'annan shi na nan zuwa duniya nan gaba kad'an." Wata dariya Khadija ta saki har da rik'e ciki kafin tace "Nagode Allah da ki ka iya tuna Bilal shine babban yaron da ya fara zuwa duniya kuma a gidan nan, hakan ya tabbatar min da mai hankali na ke zaune." Kallon ta ta yi sosai tace "Kasancewar Bilal d'an farko a gidan nan ba shi ke nuna zaifi sauran yaran da za su zo daraja ba, kamar yanda jimawar mahaifiyar shi a gidan bai sa matsayinta yafi nawa ba, dukan mu mata ne kuma matan Usman a gidan nan, aljanna ki ke nema haka nima ita na ke nema." Juyawa ta yi ta d'auki wuk'a hakan ya sa Khadija fizgo wuyan rigar ta da ko hijabi babu a jikin ta, sosai ta shak'e ta tace "Dama abu d'aya na zo fad'a mi ki, Uwani ba wai yar aiki ba ce a gidan nan kamar yanda ki ka d'auka, kuma mai gidan ma yasan da haka, ko shi bai isa ya mata abin da ki ka mata ba, dan haka ya zama na k'arshe da kalma marar dad'i za ta shiga tsakanin ki da ita bare duka, na yarda ki mata fad'a idan har ta yi ba daidai ba, amma banda cin zarafi a ciki, ki kiyaye nan gaba." Sakin rigar ta ta yi za ta fita kawai Haseenah ta ja tsaki tace "Idan shi tsoronki ya hana ya mata magana, ni nan Haseenah zan iya, kuma ki sani shigowa ta gidan kamar shigowar rahama ne da sauyi." Murmushi Khadija ta yi tace "Ina fatan dai ki na da kud'in biyan bokan na ki, dan in ba ki shirya ba za ki sha wahala wajen karb'ar gidan nan a hannu na." Juyawa ta sake za ta fita Haseenah ta kuma cewa"Aikin banza, ai ba boka ba malam wallahi zan karb'i gidan nan, makauniyar banza makauniyar wofi, ai ba a banza Allah ya hana ki idon gani ba." Wannan maganar ta makauniya ita ce ta tsayawa Khadija a rai, da k'arfi ta juyo ta matso daf da ita tace "Me ki ka ce?" Yanda taga idon Khadija sunyi ne ya sa ta kasa cewa uffan, lumshe ido ta yi ta bud'e ta sauke su a kan ta tace "Haseenah ina da yak'inin ban tab'a yin fad'a ba tun da k'uruciya ta har zuwa girma na, sai dai ina ji a jiki na cewa fad'a na zai yi matuk'ar muni, dan haka ina so ki kiyaye, ba na so na yi abin da zai b'ata min suna ko kuma zuri'a ta." Cikin rashin gamsuwa da abin da ta fad'a tace "Wai ke Khadija me ki ke d'aukar kan ki? Mummuna ko me? Akan komai sai kin nuna ke dabance, to ba zan d'auka ba wallahi, kar ki k'ara cewa za ki nuna min izzar ki dan ba ta shafe ni ba." Matsowa Khadija ta yi ta sa hannu ta ture ta baya ta na fad'in "So ki ke kisan me na d'auki kai na? Na ce ki na so ki sani ne?" Hankad'ar da ta mata ce ta sa ta yi baya sosai har ta bige tukunyar da ke kan wuta ruwa da naman ciki ya watse, lokacin da hannun Haseenah ya bugi tukunyar ta ji zafi, hakanne ya tilasta mata sakin razananniyar k'ara har duk gidan na amsawa, Usman, Naseer da su Rabi'a da ke zaune su ka hanzarto su ka nufo
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117