Chapter 78
Chapter 78
Mama, amma fa akwai matsala." "Matsala kuma? Tame?" Cikin sanyin jiki tace "Mama wannan layun da aka aje na duba su ban gansu ba, kuma gashi har yanzu ana tsorata ni a cikin dare." Da al'ajabi dattijuwar tace "Toh! Amma abun da mamaki, to ina suke? Kuma kin tabbatar an aje su in da ki ka duba?" "Wallahi Mama wajen ne, su aunty Mariya fa da kan su su ka aje su, amma da na duba babu komai a wajen." "Toh." Ta fad'a ta na girgiza kai kafin tace "Lallai wannan abu ya wuce duk in da ake tunanin shi, amma bari Baban ku ya shigo sai na fad'a mi shi komai." Sosai ta ji dad'in wannan wunin da ta yi a gida, gashi ana ta bata kulawa a matsayin ta na mai k'aramin ciki, sai abin da take so ake bata ta ci, har mahaifin ta ya zo aka fad'a mi shi abin da ke faruwa, a cewar shi ta kwantar da hankalin ta zai sake karb'o mata wasu, sannan ta ci gaba da addu'a komai zai wuce. A b'angaren Khadija kam ganin jikin ya k'i kyau ya sa Mama cewa "Khadija." "Umm." Ta fad'a ta na d'an gyara kwanciyar ta, "Khadija ba ki da ciki kuwa?" Murmushi ta yi tace "Ciki Mama? A'a, ba na da komai wallahi, kawai dai zazzab'in wahala ne." "To Allah ya tabbatar da alkairi." Cewar Mama, Bilal ne ya shigo da sallama ya na cire jakar makarantar shi, kusan maman shi ya je ya sumbace ta da fad'in "Mummy ya jiki? Kinji sauk'i?" "Na ji sauk'i yarima, har kun taso?" Saida ya fara cire rigar shi yace "Eh Mummy, kawu Ashir yace na mi ki sannu da jiki ba zai shigo ba ya na sauri." Mama ce ta katse shi da cewa "Kai d'auki tarkacan kayanka ka wuce da su d'akin ka, kar ka kuskura ka min tsirara a tsakiyar falo." Matsowa ya yi kusan ta ya yi tsaye yace "K'arasa cire min kayan ma in ki na son samun lada." Rufe fuska ta yi tace "Kai b'ace min da gani kaji ko." Fad'awa ya yi jikin ta ya sumbaci kumcinta ya na fad'in "Ina son ki Hajia ta." Rumgume shi ta yi ita ma tace "Ni kuma ba na son ka yau, dan nasan akwai abin da ka ke so waje na." Kallon ta ya yi yace "Me ki ka dafa yau?" Hararan shi ta yi tace "Uhum, nifa na san za'a rina dama, ina ka fito ci ina zaka ci, to wake na dafa." Dariya Khadija ta yi tace "Mama ta na so ta sake kumbura ma ka ciki ne." Juyowa ya yi ya kalle ta yace "Kema kin zama aunty amarya muguwa?" Daruya suka saka sai Mama ce tace "Ai ni mugunta ta ma sai tafi ta ta, dan kuwa idan ka gama ci ba ruwa zan baka kasha ba, sai dai na ba ka kwanan nan fura ka kora da ita." D'aukar kayan shi ya yi ya nufi d'aki ya na fad'in "Kuma idan na mutu ke ce za ki fara zubar da hawaye." "To ba dole ba, na rasa miji na uban 'ya'ya na, idan kai ma na rasa ka ai zan shiga cakwakiya." Usman ya je gida bayan ya aje Haseenah, Hajia kad'ai ya samu dan rana ta take sosai zaiyi wuya ka samu namiji gida a wannan lokacin, bayan sun gaisa ne Hajia tace "Amma me ya hana ka zuwa tun jiya da aka kira ka?" Cikin rashin gaskiya yace "Wallahi Hajia wani d'an aiki ne ya taso min, kuma yarinyar nan ba ta ji dad'i ba, saida ma na kai ta asibiti aka rubuto mana magani." _Daga cikin bala'in da asiri ke iya jawa mutum akwai k'arya, zai iya k'arya dan ya kare kan sa ko kuma wanda ya ke so, akwai rashin kunya ga wanda baya hayyacin shi, abune mai sauk'i miji ya tub'ewa mata kayan ta ya mata wulak'anci a gaban 'ya'yansu, kad'an ne daga aiki sihiri daina ganin girman wanda ka ke ganin girman shi, akwai wasa da addini wanda za ka ga wani ya na sakaci da shi, illolin fa dayawa yan uwa, fatan mu Allah ya k'ara tsarkake mana zuk'atanmu._ Take Hajia ta fahimci k'arya ya fad'a, amma saboda kunya ta dake tsakanin uwa d'an fari sai kawai ta share tace"Allah ya sawak'e, gashi kuma yanzu malam d'in har ya fita, sai dai in za ka same shi can shagon." Cikin sunne kai yace "Ba damuwa sai na je can d'in ai." Ba tare da ta kalle shi ba tace "To ya maganar Nura, ya fad'a min sunyi magana da Khadija kuma tace ka amince, amma a bari sai ka dawo, gashi kuma ka zo ba ka ce komai ba." "Eh Hajia, ya na ina ne Nuran?" "Ya na shago mana." "Shikenan zan kira idan na fita saiya same ni ko can shagon Murtala ne." Cikin had'e tafukan hannayenta tace "Hakan ma ya yi." Kallon ta ya yi yace"Hajia me zai hana ku je ku d'auko Bilal?" Sai lokacin ta kalle shi tace "Ban gane na je ba? Kai me zai hana ka tafiya? Kuma ma ka na nufin ba za ka je ka dawo da mahaifiyar shi ba kenan?" Cikin b'acin ran an ambaci sunan Khadija yace "Hajia ni babu in da zanje, ita ta tafi saboda ta na so, dan haka taje can ta k'arata, ni yaro na ne kawai matsala ta." Karo na farko a rayuwa da Hajia ta iya d'agawa Fodio murya, cikin jin haushi tace "To ba zan je ba, ranar da ka shirya ganin d'an na ka sai kaje ka d'auko shi da kan ka." Kallon ta ya yi shima, amma saboda ran shi a b'ace ya ke da maganar Khadija sai kawai ya mik'e cikin kumburo baki yace "Ni zan wuce, sai anjima." Da kallo kawai ta bi shi har ya fita daga gidan, girgiza kai ta yi ta na mamakin wannan canjin daga Fodio, mik'ewa ta yi ta shiga d'aki ta na fad'in "Ai kuwa da alama gaskiya malam ya fad'a, amma koma menene zan wa tubkar hanci." Daga nan wajen malam ya zame, k'ofar shagon ya samu malam zaune akan bacci shi da wani suna hira, har k'asa ya durk'usa ya gaishe su kafin malam ya sallami waccen, mayar da kallon sa ya yi kan Usman da ke durk'ushe yace "Fodio sai yanzu ka zo kiran nawa? To nagode." "Wallahi Baba..." D'aga mi shi hannu ya yi alamar ba ya son ji kafin ya d'ora da "Jiya na je gidan su Khadija, kuma naji duk abin da ya faru, Fodio ka bani mamaki sosai da na ji ance wai ka d'aga hannu ka daki Khadija, wannan abun kunyar har yaushe da irin shi, duka! Kai a matsayin ka na mai hankali da ilimi, a shekarun ku na k'uruciya haka ba ta faru ba sai yanzu da girma ya fara riskar ku, wanda ya kamata ace yanzu ne soyayya take da tausayin juna, amma ace ka dake ta akan abin da ma k'arya ake mata da sharri, kawai rud'in zuciyar ka ne ka biyewa da kuma wata banzar hud'uba da wasu sakarkari suka ma ka, kasan me ya sa ta karb'i makullin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117