Chapter 14
Chapter 14
Abban Bilal, na k'arar da rayuwa ta wajen killace ma ka kai na da mutunci na, amma kai a dare d'aya tak ka kusanci wata mace, zuciya ta bugawa take, ji na ke kamar zan mutu dan bak'in ciki wallahi." Usman kam jikin shi ne ya yi sanyi sosai, tunawa da yanda auren su ma ya kasance, duk da kusan had'a su ne akayi amma ko sau d'aya duk da matsayin Khadija na mace, ba ta tab'a nuna ma sa k'iyayya ba ko a idon ta, amma yau gashi ta na fad'in ba ta son yana zuwa kusa da ita, a hankali ya d'ago ta ya share mata hayawen fuskar ta ya na girgiza mata kai, hannayen ta ya had'e ya rufe idon shi ba tare da ya had'a ido da ita ba yace "Ki yi hak'uri Khadija, ki gafarce ni idan hakan da na yi ya b'ata mi ki rai, har zuciya ta banyi haka dan muzguna mi ki ba, ba kuma na yi bane saboda wani kaso daga cikin kason da ki ke da shi a zuciya ta ya ragu ba, babban k'arfin gwiwa ta akan auren nan shine, Nana Khadija mai halin girma da hak'uri za ta taya ni kare hakk'in da ke kai na, sannan a lokacin da aka d'ora min nauyin Haseenah a kai na wallahi zuciya ta ta fad'a min cewa Khadija na tare da kai, da izinin ubangiji za ta taimaka maka wajen ganin ba ka k'untatawa yarinyar mutane ba, amma kash! Shed'an na ta k'ok'ari sai ya kutso cikin gida na ya tarwatsa min kan su, babban abun bak'in cikin shine, ya na so ne ya shigo ta hanyar mata ta Khadija abar so da k'auna ta kuma abar alfahari na." Tafin hannun ta tasa ta goge hawayen, murmushi ta masa mai d'aukar hankali, matuk'a tasan mijin ta na son ta, kalaman shi kullum suna k'arfafa mata gwiwa da kuma sace mata gwiwa, ganin wannan murmushi ya sa ya kama kumatunta yana murmushi yace "Dariya a fuskar ki shine abin da Usman ke son gani a kullum, murmushin ki kuma shi ne silar nawa murmushin, ki ci gaba da murmushi irin haka har lokacin da zamu koma ga ubangijin mu." K'asa ta yi da kan ta tace "Kalaman ka su na sani jin kunya." Tallabo fuskar ta ya yi yace "Ke ce sarauniya, na baki zuciya, ke ce guda d'aya duniya ta masoya." Yanda ya rera mata baitin ya sa ta sake fad'awa kan kirjin shi ta na murmushi, d'agota ya yi yace "To a bani sumbata kafin na fara zanga-zanga a gidan nan." "Me ya yi zafi? Ba sai an kai ga haka ba, bani bakin ka nan." Sai da su ka gama lobayyar su kad'ai su ka fito, Haseenah da ta ji shigowar shi ta gaji da jiran shigowar ta shi kasa jura ta yi, falon Khadija ta shigo sai Bilal kad'ai ta samu ya na karatun shi, tun ta na zaune har ta fara kai da kawowa tsakiyar falon kamar za ta had'e zuciya ta mutu, ta na jin bud'a k'ofar ta juya da k'arfi, taushe b'acin ran ta tayi ta tafi a guje dama ba nauyi ba kamar ni😉, ai kuwa sai ta d'ane a jikin shi ta na fad'in "Rabin rai na, na yi kewar ka sosai, har zan fara kuka." Bilal da Khadija kallon su suke da ido, a hankali ya d'ago ta daga jikin shi da nufin mata magana, sai kawai Haseenah ta fashe da kukan shagwab'a ta na fad'in "Wallahi da k'yar na iya riskar wannan daren saboda kewar ka, a gaskiya ba za ka sake bari na gidan nan ni kad'ai ba." Sake fad'awa ta yi jikin shi, Khadija da ta ji wasu hawayen na neman taho mata ne ta juya ta kamo hannun Bilal su ka bar falon, lallab'a ta ya yi su ka koma na su falon, duk k'ok'ari Haseenah ta yi shi ta saka shi kalar nata farin ciki, wanka ta mi shi ta saka mi shi kaya marar nauyi, har uwar d'akin ta kai mi shi abinci a bakin gado ta aza akan k'aramar kujera, sam bai iya tuna su Khadija ba haka Haseenah ta dinga yanka masa loma ta na aika masa a baki ya na wucewa da ita ta mak'ogoro, ita kam dad'i ne ke kashe ta saboda ya na sake cin abincin da ta zuba garin maganin da malam ya bata, sai da ya k'oshi kad'ai ta bar shi ta ci nata a zuwan ta k'osar da wanda yafi mahimmanci a gare ta, falo ya koma ya na kallo ita kuma ta na d'aki ta d'auko garin maganin matan ta wanda sai za'a kwanta ake sha, duk da madara ta sha su kafin ta shiga ban d'aki ta sake zaunawa a cikin tafasashen ruwan bagaruwa, sai da su ka huce ta fito ta d'auki wani arnan magani na matsi emergency, k'anana ne fari kamar k'wayar magani, matsawa ta yi haka ma miski sannan ta fito ta saka kayan bacci ta shek'a kwalliya, minti sha biyar ta koma ta kama ruwa da ruwan zafi k'a'idar maganin kenan, fitowa ta yi cikin sand'a ta rufe mi shi ido ta baya, murmushi ya yi yace "K'amshin nan da na ke ji ya sa babu abin da na ke son gani sai ke." Bud'e mi shi idon ta yi cikin karairaya ta dawo gaban shi, k'are mata kallo ya yi yace "Iyeh! Wow, wane irin kyau ne wannan? Tabarakalla ahsanul-kalik'ine, Allah abun godiya." Janyo hannunta ya yi ya zaunar da ita akan cinyar shi, k'amshin humrar ta ne ya tafi da imanin shi, tuni ya fara aika mata da wasu sak'onni wanda take ta ke karb'ar su, dan magungunan da tasha masu k'arfi ne sosai, da k'yar dai su ka iya kai kan su uwar d'aki su ka kashe wuta, surukina gyara kimtsi mana, ina fa taya 'yata kishi.😎 Abunka ga ba saban ba, sosai Haseenah ta yabawa aya zak'inta, amma dai tun da taji Usman na gurnani ya na sambatu da surutai har ya na neman shid'ewa, hakan ya sa ta ji kwalliya ta biya kud'in sabulu, dama kuma *ado gwanja* yace "Rai ba'a bakin komai ya ke ba wajen biyan buk'ata."😂 Haka dukansu su ka yi baccin gajiya rumgume da junan su, washe gari kam bai bari Haseenah ta shiga madafa ba, kuma ba ya so yace Khadija tayi, fita ya yi ya samo mu su soyayyen k'wai da dankalin turawa, ya na zuwa kuma ya samu Khadija har ta had'a abin karin da ta san d'an ta ya fi so, falon ta ya same ta suna karyawa da yaron ta, gaisawa su ka yi kafin yace "Yarima har ka shirya ne?" "Eh Abba." "To idan ka kammala sai ka fito mu wuce." Kallon shi Bilal ya yi yace "Abba yau ina so na je da d'an moto na, kaga ba sai na jira ka je d'auka ta ba." D'an b'ata rai ya yi yace "Kai Bilal, mahaukaci ne ni da zan barka ka tafi a hanyar ababen hawan nan kai kad'ai akan moton ka, bana so, kuma na fad'a maka hawan moton ka kar ya wuce cikin unguwar nan, duk da cazashi ne ake amma ba na
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117