Chapter 31
Chapter 31
madafar, ganin Khadija tsaye ta na kallon Haseenah da ke rik'e da hannu ta na kuka ne ya sa Usman saurin k'arasawa, rik'o hannun Haseenahr ya yi yana kallon abin da ya zube ya kalli Khadija yace "Lafiya? Me ya faru ne?" Cikin tafasar zuci tace "Kallon me ka ke min? Ka tambaye ta mana, ni ce za ka tambaya?" Rabi'a ma matsawa ta yi kusan Haseenah tace "Haseenah me ya faru ne wai? K'onewa ki kai?" Girgiza kai ta yi cikin zubar da hawaye tace "A'a, ba k'onewa na yi ba." Usman ne ya d'ora da "To me ya faru?" Fashewa ta yi da wani kukan, hakan ya sa Usman mayar da kallon shi ga Khadija yace "Khadija me ya faru, naga ai daga ke sai ita ne a madafar ko? Me ki ka mata haka?" Kallon shi ta yi cikin ido da niyyar fad'in abin da ya faru, amma ta na kallon shi sai wannan kwarjinin da haiba da rashin sabo na rashin samun matsala da ba su tab'a yi ba ta yi k'asa da kan ta, cire gilashin ta tayi ta fashe da kukan da babu sauti, ai tuni sai hankalin Naseer ya tashi, da gaggawa ya matso kusanta shima ya kalli Haseenah yace "Wai me ya faru ne? Ke ki fad'a mana." Cikin kuka Haseenah ta kalli Naseer d'in tace "Ni ban san me ya faru ba, na dai san na yiwa mai aikin nan magana kan cewa kar ta sake shigowa madafar nan in ina aiki, banji shigowar aunty Khadija sai ji na yi ta tura ni gaba kawai, shi ne na..." Sai kumata fashe da kuka. Da tsantsar mamaki Khadija ta kalle ta, kallon ta Usman ya yi yace "Gaskiya ne abin da ya faru kenan?" Mayar da gilashin ta yi ta kalli Usman tace "Babu abin da zan fad'a ma ka, ka d'auki mataki kawai." Kallon Haseenah ta yi tace "Ba zan ce ki ji tsoron Allah ba, amma zan mi ki kashedi da kar ki sake kira na da makauniya, in ba haka ba kuma wallahi zan mugun sab'a mi ki fiye da tunanin ki." Juyawa ta yi ta kama hannun Bilal da na Naseer da nufin fita, k'yam Naseer ya tsaya ya kalli Haseenah yace "Kamar k'anwa na ke kallon ki, dan Allah kar ki bari wani abu na rashin kyautatawa ya shiga tsakanin ki da yer uwa ta, ita d'in kamar rayuwar mu ce, ban tab'a jin wanda ya yi k'ok'arin kiranta da makauniya sai yau, dan haka ki kiyaye dan Allah, ku zauna lafiya sai mijinku ya yi farin ciki da ku." Juyawa ya yi su ka fita, a daidai k'ofar shiga falon Khadijar su ka tsaya, dafa kan ta ya yi yace "Ki yi hak'uri kinji yar autar mu, ina tabbatar mi ki hakan ba zai sake faruwa ba, ki daina kuka kinji ko." Cikin shashek'ar kuka tace "Shikenan yaya na, kar ka damu na dain, ka tafi gida kawai, amma dan Allah kar ka bari kowa ya ji a gida, wannan matsalar gidan nan ce." "Shikenan zanyi, amma ki min alk'awarin hakan ba zai sake faruwa ba." "Nayi." Ta fad'a da murmushi, shafa kan Bilal ya yi yace "Yaro na sai anjima ko, yaushe za ka shigo wajen matar?" Ba walwala a tare da shi yace "Tonton (uncle) da Momy za ta yarda da na bika gida, gaba d'aya yanzu gidan nan ba dad'i, Abba ma ya daina cin abinci da mu kuma ba ya..." "Bilaaaal." Khadija ta kira sunanshi, wucewa kawai Naseer ya yi su ma suka koma ciki, d'akin Bial su ka nufa dan ta taimaka masa ya canza kaya Uwani ta yi sallama, juyowa ta yi ta kalle tace "Uwani ki je gida kawai, ki bari sai gobe ki dawo." "To aunty, amma Abban Bilal yace wai ki same shi a d'akin shi yanzu." Sai da ta d'an kawar da kai kafin tace "Shikenan, ina zuwa." Kallon Bilal ta yi tace "Ka je ka cire wannan kayan sai ka watsa ruwa ka canza wasu, ina zuwa yanzu ka ji." Ciki ya shiga ita kuma ta wuce d'akin Usman, a falon shi su ka ci karo da su Rabi'a za su tafiya, amma ko kallon ta Rabi'a ba ta yi ba saboda a tattaunarwa da su ka fara da Usman sai kare Khadijar ya ke, Jauza'u ce tace "Sai anjima aunty Khadija." "Ki gaida gida Jauza'u." Cewar ta ta na shiga d'akin, zaune ya ke akan kujera da ke gaban madubi in da Haseenah ke zaune bakin gado, ita ma bakin gadon ta zauna kamar yanda ya nuna mata, ya na kallon fuskokin su ya gyara zama yace "Baiwar Allah, a gaskiya yau d'in nan na ji kunyar abin da ya faru a gidan nan, sai da zuciyata ta wahala kafin na yarda Khadijata ce ta aika abin da ta aika ta, saboda ni dai nasan tawa Khadijar mai hak'uri ce da kawar da kai, amma ban san ya akayi wannan karan hak'urin ta ya gaza ba, ni da na ke mata fatan ta kai k'adamin da za ta dafa dutse har ma ta shanye romonsa, amma gashi shaid'an na san min yawo da hankalin ta wajen tilasta ta yin abin da bai dace ba, Khadija, ya haka? Ya akayi ki ka bari haka ta faru? Me ya tunzura ki haka?" Tabbas a kowane lokaci kalaman mijinta su na tasiri a kan ta fiye da yankan wuk'a, hakanne ma ya sa ta kalle shi a ladabce tace "Ka yi hak'uri Abban Bilal, ni ma sai yanzu na ke jin kunyar abin da na aikata, amma insha Allah hakan ba zai sake faruwa ba, wannan alk'awari ne." Sai da Usman ya lumshe ido saboda tsabar jin dad'i, ji ya yi kamar ya rumgumota jikin shi, sai dai a yanayin da ake ciki hakan bai kamata ba saboda tsaro, murmushi ya yi yace "Hakan ya yi kyau, Allah ya ba ki ikon cika alk'awarin nan da ki ka d'auka, kuma sai a ci gaba da kiyaye saboda gudun b'acin rana, wata rana ba'a san me zai faru ba a irin haka." "Insha Allahu za'a kiyaye." Ta sake fad'a a ladabce, mayar da kallon shi ya yi ga Haseenah yace "Ke kuma Haseenah, ba wai zan tambaye ki me ya faru ko kuma waye mai laifi ba, a'a, zan fad'a mi ki wani abu ne da na ke ganin ya kamata ace tun farko kin san shi kafin ki shigo gidan nan, Haseenah." Yanda ya kira sunan ta yasa ba ta da zab'in da ya wuce d'agowa tace "Na'am." D'orawa ya yi da "Khadija dai matata ce tsawon shekara goma sha uku, shekara sha uku ba kwana goma sha uku bane Haseenah, kinga kenan k'arshen sanin juna munyiwa kan mu shi ni da ita, a wannan shekarun da mu ka d'auka Haseenah, wallahi, wallahi na rantse mi ki da Allah ba zan iya tuna ranar da zan ce mi ki wannan baiwar Allahr ta min ko da kallon raini ne bare tsaki ko bak'ar magana, Haseenah, kin ganta nan ki tambaye ta kiji yanda auren mu ya kasance, amma sau d'aya ba ta tab'a nuna min k'iyayya ko tsana ba, idan har na ce eh, to eh ne
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117