Chapter 114
Chapter 114
dan Allah ban..." Bai k'arasa ba saboda ganin *Saif* (jarumin littafin *Ba so bane*) sai dokan uban murmushi yake ya na kallo na, ajiyar zuciya na sauke dan nasan ba matsala, da dai sauran mazan hajjajan ne da ban san me zai faru ba, kafin ya yi magana *Zeinab* tace "Lah aunty Meera ke ce? Me ki ke anan?" Izuwa yanzu kam na fara gajiya wannan tambayar da kowa ke min ta me ya kawo ni, amma sai na dake na ce "Ni ma na zo bikin Khadija ne." Da wannan murmushi Saif yace "Ko kuma suma idon ki ka saka mu su ba kamar yanda ki ke wa kowa." Kallon shi na yi na ce "Haba Saif ya za ka ce haka, kaine fa na ke gani mai hankali a cikin sauran." Waro ido ya yi yace "Au! Wai ki na nufin sauran duk mahaukata ne?" Kau da kai na yi na ce "Ka ga ni dai bance ba kar ka ja min sharri." Juyawa ya yi bayan shi yace " Bara na ga ina zanga aboki na na fad'a mi shi kin ce mahaukata ne su." Da sauri na bar wajen ina fad'in "Shi ma dai ya lalace kamar sauran, nasan kuma ba zai rasa nasaba da wannan bigaggen *Salman* (jarumin littafin *Auren had'i*) d'..." Ai dole naja birki domin kuwa karo na yi da Salman d'in, wani kallo ya min yace "Ni ne ma bigaggen?" Murmushin dole na yi na ce "Ah haba dai, ni na isa na kira ka da bigagge, dama da Saif na ke." Dafe k'irji ya yi yace "Abokin nawa ne bigagge kenan?" Zanyi magana naji andafa ni ta baya ance "Aunty Meranmu dan Allah rabu da su, wahalar da ke kawai za su yi." Baki na.saki saboda ganin *Ummi* ta zama wata babba kuma hamshak'iyar mace, kallon Salman na yi a raina ina raya koya yake ya na iya d'aukar ta ma yanzu? Hum, kallon ta na yi na ce "Ummi na ina 'yan biyu?" Da murmushi a fuskarta tace "Yan biyu su na wajen su lamama, amma ya na gan ki anan? Me ki ke yi?" Salman ne ya juya ya zauna kan kujerar da suka tashi ya na fad'in "Me fa zai kawota da ya wuce d'aukar rahoton da ta saba, ta na nan kullum ta k'i canzawa sai tsukewa take, Allah ya sa wayar taki ta fad'i sai mu ga ta tsiya." Wata dariyar rainin hankali na mi shi na ce "Ka ji malam Salmanu, wato so ka ke na zuma b'ukekiya kamar matar ka, to ni mijina ba ya buk'atar na yi k'iba haka yake son gani na, sannan da ka ke fatan wayata ta fad'i to in fad'a ma ka ta na fad'uwa wallahi sai ka biya ni, in kuma ba haka ba zansa Ummi ta ma bore har sai an sake ma ka tiyata, ai dai ka gane tiyatar da na ke nufi ko?" Ta fad'a ta na kashe mi shi ido d'aya, baki ya saki ya na kallo na har na wuce na bar shi, saida na b'acewa ganin shi ya kalli Ummi yace "Kuma ke sai kiyi idan ta saki?" Cike da tabbatarwa tace "Sosai kuwa, me zai hana ni?" Gyad'a kai kawai ya yi ya cije leb'en k'asa, har na wuce na yi saurin dawowa baya cike da tsoro, murza ido na yi ina so na ga wai tabbas shine wanda na ke zato ko kuma dai gizo ne, da mamaki na ce " *Abbas* (jarumin littafin *Sanin masoyi*), ai kam da sauri ya juyo, amma abun mamaki ya na gani na saiya had'e rai ya sake juya min baya, har zan shiga tunanin dalilin da ya sa ya min haka sai kawai na ji andafa ni, juyowa na yi sai kuwa na ga takwarata, cike da farin ciki mu ka rumgume juna ta na fad'in "Takwarata me ki ke anan?" Raba jikina na yi da nata na sake kallonta ta yi kyau sosai, murmushi na yi na ce "Na zo biki ne ni ma." Tsaki naji Abbas yaja hakan ya sa mu ka kalle shi a tare, *Sameera* ce tace "Jarumi na lafiya ka ke tsaki?" Da k'yar yake maganar saboda miskilanci yace "Kinsan ba na son hayaniya, wannan kuma ta tsaya min a kai ta na zuba kamar 'ya'yan kurna." Tabbas raina ya b'ace yanda Abbas ya nuna ni kamar ya nuna kashi, tab'e baki na yi na ce "Da ace banga lokacin da ka ke wa takwarata 'yar murya ba da sai ka zare min ido, amma tunda har na ga komai to magana ta k'are, wannan shan kunun duk birga ce wallahi." Kallon Sameera na yi na ce "Takwara idan kun koma gida lafiya ki gaishe min da su Bashir da su Abba da Mama." Da murmushi a fuskar ta tace "Za su ji aunty Meera." Har zan wuce na ji Abbas yace "Ta na nan har yanzu yanda take kamar za ta fad'i ta na fama da bibiyar rayuwar mutane." Wucewa na yi na barshi da takwarata tace mi shi "Ba fa na son haka uban yara, duk abin da za ka fad'a mata kamar ni ka ke fad'awa." Wani kallo kawai ya bita da shi kamar zaiyi bacci, ni kam ina barin nan na shiga neman mutuniya ta, ai kam bansha wahalar ganin ta ba, da gudu na k'arasa na rumgumeta ta baya ina fad'in "Ohhh, my Hajiata." D'ago kai ta yi ta kalle ni tace "Lah! aunty Meera, ke ce anan? Me ki ka zo yi wurin nan?" Saida na taushe zuciya ta kafin na ce wani abu *Umar Faruk* (jarumin littafin *Jihadi*) ya fizgoni na yi baya ya na fad'in " Dallah malam sake ta, me ye haka kin wani zo sai kin karya ta." Ba dan Umar ne ba da sai na mi shi rashin mutumci, amma saina k'yale na ce "To cinye ta zanyi da ka wani taso min haka?" A tsaurare yace "Ki yi baya ki daina tab'a jikin matata shine kawai abin da na sani." Rik'e hab'a na yi na ce "Ikon Allah, beby mijin beby, wato wai kai mai kishi ko? To Allah ya kyauta." "Ya ma kyauta." Ya fad'a ya na kallo na, *Khairat* na kalla na ce "Hajiata ina *Zubaida* ne? kinsan fa fan's sunyi kewarta." Murmushi ta yi tace "Ta na gida bata jin dad'i ne, kuma ga tsohon ciki da ke jikinta, shi ya sa ta zauna gida tunda tafiya ce mai nisa." Juyawa na yi na kalli Umar ina dariya, shi kam sai ya had'e rai ya na harare na, saida na fara takawa na ce "Lallai Umar ba dama, wato har yanzu ka na nan ka na tsula tsiyarka, daga wannan ta sauke wannan za ta d'auka, humm." Juyawa na yi zan wa Khairat magana amma sai Umar ya ciro takalman shi zai jefe ni, da gudu na bar wajen ina dariyar mugunta, kujera na samu na zauna ina sauke numfashi kamar saukar aradu daga gefena aka ce "Aunty Meera ya ki ke?" Da murmushi na juyo dan na gane mai muryar, da farin ciki na d'aga mu su hannu na ce " *Falmata* (d'aya daga jaruman littafin *Itace k'addarar mu*), lafiya lau, ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117