Chapter 68
Chapter 68
gida ranta ba dad'i ta na ji a ranta Khadija ta bata kunya, *Khadija baiwar Allah* ba ta san ma tsiyar da suke ba, dan ita abincin Haseenah ma idan ta aiko kullum saidai ta kira mak'wabtanta azo a d'auka, ita kuma haka za su yi ta yan dubaru ita da d'an ta. *Yau sati biyu* kenan da tafiyar Usman, kuma jibi ne komawa makaranta, hakan ya sa Usman kiran Khadija a wayar ta, ta yi mamaki dan abu ne da bata tab'a gani ba tunda ya tafi, ta na d'auka suka gaisa a gajarce ya d'ora da "Na ga yara na ta shirin komawa makaranta, amma saboda banda girma da mutumci a idon ki ban isa ki fad'a min ba ko da wani abu da ku ke buk'ata." Murmushi kawai ta yi tace "Allah huci zuciyar ka ranka shi dad'e, ai akwai hikima sosai a cikin hallitar kowane bawa da iyaye biyu, naga ba ka gari ne kuma kullum cikin aiki ka ke, ba ka da lokacin waya dani bare har mu yi magana da ta shafi d'an ka, shi ya sa ni kuma na mi shi duk wani abin da zai buk'ata, har kud'in makarantar ma na biya." Duk da ya ji wani abu a zuciyar shi a game da ita, amma basarwa ya yi yace "Uhum." Kashe wayar kawai ya yi, take ya durmiya cikin tunani, Khadija kud'in da ya bata babu abin da za su mata, amma da su take buk'atunta har ta biyawa yaro kud'in makaranta, amma kuma Haseenah daya lodawa masu yawa yanzu haka zaije ya tura mata kud'i ne dan tace suna buk'atar kud'i, dan haka ya kasa nutsuwa ya kira Aziza ya tambaye ta da gaske Haseenah ta na bata kud'in adaidaita, bud'ar bakin ta cewa ta yi "Eh yah Fodio, ta na bani na zuwa da dawowa, har da ma d'an na kashewa, kuma kullum fa sai mun siyi abinci in dai ranar girkin Khadija ne, kuma jiya masu karb'ar kud'in ruwa sun zo dole sai aunty Haseenah ce ta basu." Duk da ya yarda da Aziza dan abu d'aya suka fad'a amma Haseenah ba ta fad'a mi shi suna siyen abinci ba, haka dai ya sa Nura ya kawo mata kud'in sannan ya kira ya tambaye ta K'arin haske akan abin da Aziza ta fad'a, cikin marairaicewa tace "Kawai ba na so ne wani abu ya faru kuma ace ni ce sila." "Shikenan to ya yi kyau." Ya fad'a ya na kashe wayar, wayar Khadija ya kira dan jin dalili, amma suna gama waya ta farko Aishatu ta kira ta tace ga ta k'ofar gida mai gadi na mata iskanci, dariya Khadija ta yi kafin tace ta na zuwa, Bilal ta aika sai gasu sun shigo tare, Aishatu budurwace da ke da larura ta iska, hakan ya sa komai nata daban ne, fad'a da masifa kamar shan ruwa ne a wajen ta, tunda su ka shigo tare da Bilal ta ke zagin mai adaidaitar da ya kawota wai yace sai dai ta bashi arba'in ita kuma ishirin ta bashi, hakan ne ma ya sa sam Khadija ba ta ji kiran Usman ba saboda wayar na (vibration) ne, aifa nan hira ta b'arke suna ta yi kamar wanda aka jonawa lantarki, tunda wuri kamar yanda ta saba suka shiga girkin yamma, kuma yau ta yi niyyar yin waina dan akwai wa abokanan mahaifin ta, saboda sabo ya sa ba wani wahala tasha ba musamman kuma ga mai kamawa, sai salade da shima aka siyo mata suka gyara abinsu, Bilyamin ta kira ya kai wainar in da ta zubawa Haseenah na su tace ya kaii, da sauri Aishatu tace ya jirata su tafi tare ta ga amarya, nan fa gaban Khadija ya shiga dukan uku uku, dan ba lallai ta shiga lafiya ta fito lafiya ba, k'aramin aikinta ne ta k'arewa Haseenah kallo tace au dama wannan ce amaryar? Saida Khadija ta rik'e hannunta tace "Dan Allah idan ki ka je ku gaisa kawai ki juyo ki dawo, ba na son tashin hankali ko kad'an." "Wai amaryar 'yar akuya ce kenan? To ai sai ki fad'a mata ki na da irin mu 'ya'yan busurai, mu za ta wa iskanci?" Cewar Aishatu har tana gaggawar tafiya, rik'e ta Khadija tayi tace "Ni fa ban fad'a mi ki haka ba, kawai dai ku gaisa ki juyo ki dawo, kar ki ce za ki tsaya wani abun da bai shafe ki ba." Saida ta fizge hannunta tace "Naji dallah." "Kinyi alk'awari?" Cewar Khadija ta na binta da kallo, k'ala ba tace ba ta bi bayan Bilal su ka shiga, Bilal ne ya yi sallama amma shiru, bubbuga k'ofar ya yi ya sake jin shiru, sai Aziza ce ta lek'o daga sama ta hangeshi tace "Bilal ga auntyn ka nan sama." Daga nan yace "Abinci ne na kawo mu ku." "Kawo nan." Cewar Aziza, kallon Aishatu ya yi tace "Muje saman na ganta, ai ko saman bakwai take sai na ganta yau." Can suka nufa, Bilal na isa ya aje abincin sai aishatu da ke k'arewa Haseenah kallo ta hakimce akan kujera ta na latsa waya, kallon Aziza ta yi tace "Ke na ganeki k'anwar Usman ce ko?" "Eh, ina wuni." Cewar Aziza wacce ba tun yau ba tasan Aishatu farin sani, mayar da kallonta ta yi ga Haseenah ta na wani murmushi tace "... *Allah fidda A'i daga rogo.* 15/02/2020 Γ 13:58 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *26* "Wai ke ce dama amaryar da ya yi? Kai, amma dai wallahi maza ba su da tabbas, yanzu shi dan Allah rufe mi shi ido ki ke kayi? Ko kuma tallarki aka mi shi?" Bilal ne ya kalle ta yace "Aunty Aishatu mu tafi ko." Bushewa ta yi da dariya tace "Bilal barni na k'are kallon amaryar Baban ka, wannan mace haka sai kace kaza ta ga wuk'ar yankanta." Wata dariyar ta saka mik'ewa Haseenah ta yi da nufin magana sai Aziza ta rik'e hannun ta, girgiza mata kai ta yi alamar a'a ta rabu da ita, ganin hakane ya sa Aishatu cewa "Da kin barta ta fad'i abin da ke ran ta ai kar ta zama ajalin ta, ni ma saboda ba zan iya yin gulmarki bane ya sa na fad'i abin da ke raina tun a gaban ki." Iza k'eyar Bilal ta yi tace "Mu tafi kai yaro ka ji, Allah ya tsigewa Babanka rigar wahala, wannan mata kafin ya sa k'asusuwanta su cika ai sai mai kampanin gidan shinkafa na *oriba* ya san da zaman shi." Ta na wucewa Haseenah tace "Ita kuma wannan mahaukaciyar fa? Wacece ita?" Ajiyar zuciya Aziza ta sauke tace "Hum! Cousine d'in Khadija ce, mahaukaciya ta sawa a gidan gaba, wallahi da kin biye mata ina tabbatar mi ki yau a gidan nan sai kinga motar masu kashe gobara." Tab'e baki ta yi tace "Kin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117