Chapter 11
Chapter 11
_KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_🧕🏼 *(UWAYEN GIDA)* 🇸🇦 *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_🤜🤛 ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *7* Kasancewar Bilal zai koma makaranta yau ya sa Khadija ta shi da wuri ta nufi madafa dan shirya abin kari, (albarkacin kaza k'adangare kan sha ruwan kasko), tun da ta tunkari k'ofar ta gan ta bud'e ta ke mamakin yanda k'ofar ke bud'e, da wannan mamaki ta k'arasa shiga, turus ta ja ta tsaya ganin oga malam yallab'ai kuma alhaji Usman ya d'auki k'atuwar tasa daga kan gas ya na juye tafasashen ruwan da ya dafa a k'aramin bokiti, da sauri ta k'arasa ta na fad'in "Abban Bilal, me ka ke yi haka?" Wani abu ya ji tare da kunya dan baiso ya ganta ba ko ita ta gan shi, d'agowa ya yi bayan ya juye ruwan ya na d'an had'e fuska yace "Um, wallahi, wai wanna ce, ina jin dai, kamar dai ba ta cika wanka da ruwan sanyi bane da safe, to shine na..." Katse shi ta yi da cewa "Uhum! Na gane ma, ka kai mata to kafin su huce." D'auka ya yi cike da kunya ya fice, sai da ya b'ace ma ganin ta taji hawaye sun cika idon ta, cire gilashin ta ta yi ta share k'wallan, ji ta yi ma ba za ta iya komai ba dan haka ta juyo ta fito, ta na zuwa falon ta taga abin mamaki, da sauri ta saki murmushi tace "Wa na ke gani kamar Uwani?" Da dariya matashiyar yarinyar tace "Ni da kai na Maman Bilal." "Uwani yaushe ki ka dawo? Sai kawai na gan ki haka kamar aljana." Dariya Uwani ke yi har tace "Jiya na shigo da magriba, shi ya sa ma ban zo tun jiya ba." "Kai, amma ko na ji dad'in zuwan nan na ki, dan yanzu haka da ki ka ganni wallahi na gaji ne, har na shiga madafar kuma na fito da d'aki ne zan koma ba kwanta kuma sai gaki." Da karsashi Uwani ta mik'e tace "Maman Bilal ba ki da matsala tun da na dawo, yanzu fad'i me za'a dafa sai na shiga da kai na." "A'a ba za ayi haka ba, ai ganin ki karsashi ya k'ara min, kawai muje tare sai mu d'ora, kinga ma daga nan sai ki bani labarin abinda ya tsayar da ke." Dariya ta yi su ka nufi madafar, aiki suke su na hira ta na fad'a mata abin da ya tsayar da ita, da haka su ka kusan kammalawa Khadija ta sakar mata aikin ta tafi d'aki dan yin wanka. Da taimakon Usman Haseenah ta shirya kan ta sai shefiyar shagwab'a take zuba mi shi, shi kam yau ya na jin ya samu sabuwar hanya sai wani biye mata ya ke, ba dan yaji abin da ya saba ji ba, sai dan kawai yau sabuwar hanya ce ya bud'e da kan shi, a k'arshe ma daga d'akin ta zuwa falon shi sai da ya d'auko ta ya fito da ita, ya na zaunar da ita yace "Bara na je na samo mi ki abin da za ki ci ko, na san yanzu ki na jin yunwa." Cike da kissa da salon iskanci tace "Um, amma gaskiya ba komai zan iya ci ba." Sai da ya sumbaci hannun ta yace "Ranar ki ce yau amarya, ki fad'i duk abin da ki ke son ci, za'a kawo mi ki shi gaban ki." Cike da yauk'i tace "Da fari dai ruwan bunu na ke son na fara korawa a ciki na, bayan nan kuma sai na samu tuwon shinkafa." Wani kallo ya mata da murmushi yace "Eyeee, amarsu, ko dai a dare d'aya har na yi nasarar aika sak'on ke kuma kin karb'a hannu bibbiyu." K'asa ta yi da kai ta na murmushi, janyo ta ya yi ya rumgume yace "Allah ya sa haka Haseenah, zan fi kowa farin ciki da faruwar hakan, a karo na biyu Allah ya sake nuna min jini na a duniya." Jin haka ai sai ta shagwab'e tace "Yunwa fa na ke ji sosai rabin rai." Zunbur ya mik'e yace "Shikenan to, yanzu zan dawo, bara na shiga na ga auntyn ki sai na wuce." Kwab'e fuska ta yi alamar za ta yi kuka, da sauri ya dawo ya zauna yace "Me ye kuma na kuka? Ciwo ki ke ji har yanzu?" Kai ta girgiza tace "Ina tausayawa kai na ne dai kawai." "Da me ya faru?" Cikin goge ido tace "Ka ce sai ka fara zuwa wajen aunty na, kuma na san kai da aunty na kamar Roméo da Juliette ne, ban san yaushe za ka fito ba." Murmushi ya yi yace "Yanzu fad'a min ya ki ke so ayi to?" Cikin turo baki tace "Idan ka dawo ai sai ka je ku gaisa, kai kuma cinye kan ku ni dai ina daga nan ina cin abinci na." Dariya ya yi yace "Kenan ba ki damu da ni ba ko?" Hannun shi ta rik'o tana kallon idon shi tace "Da kafin daren jiya ka fad'i haka sai na iya yarda abisa wasu dalilai, amma banda safiyar da ta tabbatar min mun zama d'aya ni da kai." Murmushin jin dad'i ya yi ya sumbaci kumatun ta ya mik'e yace "Sai na dawo, za ki sha zallar ruwan madarar soyayya." Kashe mi shi ido ta yi tare da d'ora k'afa d'aya kan d'aya, Khadija ta fito cikin wata arniyar doguwar rigar shadda, kwanukan abincin ne hannun ta tare da Uwani a bayan ta, abin mamakin da ba ta tab'a ganinshi ba wai Usman ya fita ba tare da ya lek'a in da take ba, Haseenah da ta ga shigowar su ko kallo babu wanda ta ma, sai da ta aje kwanukan daga in da take tace "Amarya sannu da hutawa." "Sannu." Ta fad'a ta na wani yamutsa fuska, Uwani ce tace "Ina kwana aunty amarya." Kallon ta ta yi cikin rashin sanin wacece ita, Khadija ce tace "Sunan Uwani, mai aiki na ce, amma yanzu ta zama mai aikin mu gaba d'aya." K'ala babu wanda ta tanka ma sai ma d'auke kai da ta yi, d'an cije leb'e Khadija ta yi alamar muje zuwa d'in nan, fita su ka yi su ka d'auko sauran kayan abin karin, ta na cikin jera su Bilal ya fito cikin shirin makarantar shi, da fara'a ta kalle shi tace "Yarima har ka shirya?" Sai da ya je gaban ta ya sumbaci kumatun ta yace "Ina kwana sarauniya." Dariya ta yi tace "Ka tashi lafiya?" "Lafiya lau." Ya fad'a ya na jan kujera zai zauna, ido ta zaro mi shi tace "Kai, ba ka ga auntyn ka bane? Ka je ka gaishe ta mana." Tsaye ya mik'e yace "Ki yi hak'uri Ammie, ban lura da ita ba." Wucewa ya yi ya je har in da take, hannun shi ya d'ora a wuyan ta ya kai bakin shi zai sumbaci kumatun ta, ba zato ba tsammani ta ji abun, dan haka ta yi saurin zabura tare da ture shi da k'arfi har
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117