Chapter 98
Chapter 98
sosai akan lamarin na shi, dan har yanzu ba su kwana d'aki d'aya ba, gari na wayewa kuma zai buga sammako yaje gida ya na lallab'ar malam ya je ya dawo da Khadija, sam ba ya da lokacin wata Haseenah yanzun, abinci ma idan ta dafa sai dai ta ci ita kad'ai amma ban da shi, ba ya son zuwa gidan saboda ba ya son ganin Haseenah da idon shi, ya na iya k'ok'arin shi sosai wajen b'oye k'iyayyar da yake mata, ya rasa dalilin da ya sa ya ke sake jin tsanar ta a kullum idan ya ganta, ba ya son jin muryar ta ko ganin giftawarta a gidan, duk da ba ya da kokwanto akan cikin da ke jikin ta cewa na shi ne amma dai ba ya jin ya na k'aunar abin da ke cikin ta kamar yanda ya ke k'aunar wanda ke cikin Khadija, a haka har aka kwashe *sati biyu* babu abin da ya sauya. A sati biyun nan ne Usman ya yi tattaki har k'auyen su Baba Garba mai gadi ya je ya bashi hak'uri akan abin da ya farusannan ya nemi da ya dawo bakin aikin shi, ya hak'ura ya kuma nuna masa komai ya wuce shi dama bai rik'e ba saboda ya san ba laifin shi bane, amma dai ba zai iya komawa aiki ba saboda jiki da jini, amma idan ya amince akwai d'an shi da ke neman kangarewa zai iya had'a shi da shi saiya zauna a mazaunin shi, ya amince ya taho da yaron mai sunan *Rabe*, tabbas ya fara aiki yanda ya kamata sai dai burin Usman akan yaron ba wai ya zama mai kula da pliwoyin (flawers) gidan shi bane da k'ofa, ya na so a gama wannan zagon na karatu sannan ya d'ora shi ya ci gaba da karatun shi tunda ya na yi ya dakatar saboda shirme, duk da haka kuma Usman bai daina bibiyar Khadija ba, yanzu haka har ya gaji da sawa Bilal na rok'on ta akan ta dawo, Hajia da malam dama sun ce ba ruwan su, a k'arshe ya samu da k'yar ya lallab'a Murtala ya je ya mata magana, nuna masa ta yi ba komai za ta koma, amma ya na barin gidan tace ba yanzu sai ya sake shiga hankalin sa, jin shiru shiru ya sa saida ta kai ga Usman ya turo Nura da Kabir da kuma Mannir su ka je bata hak'uri, sai lokacin Mama tasan da irin tsiyar da Khadija ke tsulawa, dan sam babu wanda ya tab'a ce mata ya zo bata hak'uri dan ta koma, Usman kuma idan ya zo ta kan basu wuri ne dan su tattauna, kuma ba ta nuna mata wasu alamu na rashin jituwa, hakan ya sa ba ta san me ke faruwa ba, shi ma Usman ya so ya b'oye mata ne dan yasan za ta iya tirsasata akan ta dawo, duk da ya na matuk'ar so ta koma amma ya fi so ta koma dan ganin damar ta, kuma har yau ba ya ganin laifin ta akan hukuncin da take masa, dan kuwa babu abin da ta rage shi da shi a rayuwa amma ya mata kishiya, sannan ya rasa meya shiga kan shi da ya dinga cin mutuncin ta, dan wasu abubuwan sai yanzu ne idan ya na rarrashin ta take iya fad'a mi shi irin abin da ya mata, bugu da k'ari kuma bata gama hucewa ba ya zo ya bugar mata baki har saida ya kumbura, wanda kullum mitar hakan take masa, nan Mama tace su koma Khadija za ta dawo gidan ta ba jimawa, sun tafi da farin cikin samun nasara amma sam Khadija tace ba yanzu zata koma ba, da Mama ta fara fad'a kuma sai 'yan biyar suka tausheta suka ce tunda ba yarinya ba ce kawai a rabu da ita, hakan ya sa a ranar Usman ke ta zuba idon ganin Dije amma shiru, ko bacci baiyi ba a ranar ya na sak'awa ya na warwarewa, washe gari da dare ya je gidan da kan sa, a falo ya samu duk 'yan biyar d'in da wasu daga cikin yaransu, Mama na d'aki hakan ne ya sa ya zauna suka gaisa sosai, Naseer ne yace "Auta kam ta na ciki, amma kafin ka shiga ciki ka kawo kud'in ganin ta." "To in dai hakane me zai hana ka fad'a min gaba d'aya farashin da zan biya, kaga sai ka d'auke ta da kan ka ka kai min ita gida na." Cewar Usman cikin raha, dariya su ka yi sai Habeeb ne yace "K'anwa ta fa tsada ne da ita, farashin ta baya fad'uwa." Cikin zolaya yace "To kunga, duk cikin kun nan naga babu wanda zai iya taimaka min, dan haka ni zanje na yi yak'i na ni kad'ai, in har k'anwar ku bata koma gida na zuwa gobe ba to ku canza min suna." Cike da cika baki ya mik'e zai nufi d'akin Khadija Naseer ya bushe da dariya yace "Wane sunan za mu saka ma ka to?" Juyowa ya yi ya harare shi yace "Ka zab'a da kan ka mana." Bashir ne ya yi saurin cewa " sai mu saka mi shi *Mani*." Komai baice ba ya wuce d'akin, ko sallama baiyi ba yau dan al'amarin ba sauk'i, kuma cikin sa'a saiya samu Khadija tana ban d'aki, murmushi ya yi kafin ya cire hular kan shi ya aje gefe ya kwanta kan gadon ya yi d'a-id'ai, kusan minti biyu ya d'auka kafin Khadija ta fito daga ciki d'aure da k'irji, kasancewar cikin ta ya sa ya d'age sosai daga sama har ya kan iya hango cinyoyinta, ita kam gilashin ta ne take gogewa ta na k'ok'arin sakawa, ta na sawa ta ja ta tsaya da tsoro fal a idon ta, bud'ar bakin ta cewa ta yi "A'uzu billahi mina shaid'anir-rajim, innahu min Suleimana wa innahu bismillahir-rahamanir-rahim." Ba tare da damuwa ba Usman yace "A kan ki, wato na ma zama shaid'an ko?" Wata ajiyar zuciya ta sauke ta matso kusan shi tace "... *Ina k'aunar ku.* 06/03/2020 Γ 12:54 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *36* "Malam lafiyar shigo min d'aki haka kawai, wa ma ya baka izinin shigowa nan?" Kamar ba dashi take magana ba ma saiya share ta, ta jima tsaye ta na kallon shi ganin bai damu da tsiyar da take ba ya sa ta juya ta isa gaban madubi ta fara shafe shafe kamar yanda ta saba, lokaci lokaci takan juyo ta kalle shi amma abun mamaki shi kuma hankalin na ga waya ya na dannawa, saida ta gama ta nufi wajen kaya ta d'auko riga, ba tare da ta cire d'aurin k'irjin ba ta saka wando da rigar nono kafin ta saka doguwar rigar, juyowa ta yi ta kalle shi tace "To malam, idan ka gama da d'akin sai ka rufe min
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117