Chapter 93
Chapter 93
kan shi saida ya yi atshawa guda hud'u, Usman kam da ya kama atshawa tun ya na yi daga zaune har saida ya bud'e rufar ya tashi zaune, atshawar da ya yi ba iya ka kafin ta tsagaita mi shi, jingina ya yi da kujerar da ke bayan shi ya na dafe da kan shi, da k'yar ya fara furta "Inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, inna lillahi wa'inna ilaihi raju'un, la'ilaha illalah, Muhammadur- rasulillahi sallalahu alaihi wassalam." Matsowa malam ya yi kusan shi yace "Fodio ya ka ke ji yanzu?" Ya na dafe da kan shi cikin yamutsa fuska yace "Gaba d'aya ji na ke kamar ba ni ba, kamar na farka daga wani mummunan bacci na ke ji." "Alhamdulillah, Allah kai ne abin godiya." Cewar malam kafin ya mayar da kallon sa ga Fodio yace "Ka tashi ka saka kayan ka sai ka samu ka je gida ka kwanta ka huta ko, amma dan Fodio a daina wasa da addu'a, ba zance sakaci da addu'a bane ya ja abin da ya faru, saboda kuwa na sanka sosai ba ka wasa da ibada, amma dai ka sake zage damtse ka ji." Mik'ewa ya fara yi da k'yar yace "Insha Allahu Baba, amma wai me ya faru da ni ne?" "Idan ka je gida ka huta mayi magana wani lokacin." Jiki a matuk'ar sanyaye ya sanya kayan shi ya fito daga d'akin wanda ya yi daidai da fara kiran sallah isha'i, haka ya wuce ba tare da ya kula kowa ba saboda abin da ya ke ji, a k'ofar gida ya samu Bilal zaune akan tabarmar malam ya yi alwala, shi ma alwalar ya yi suka nufi masallaci tare, bayan sun fito ne Usman ke tambayar shi "Wai ina sarauniya ne ban gan ta ba?" D'aga kai Bilal ya yi ya kalle shi kafin yace "Mummy na na gida ba ta jima da tafiya ba." Ji ya yi sam babu wani abun da ya ke iya tunawa ma a kan shi a halin yanzu, kallon Bilal ya yi yace "To ni yanzu gidan zan tafi, za ka je ne ko kuma na barka?" "Um um, Mummy tace na zauna nan sai an gama bikin kawu Nura." Shafa kan shi ya yi yace "To shikenan ni zan tafi, ka kula da kan ka kaji ko." Saida ya sunkuya ya sumbace shi kafin ya shiga motar shi ya wuce gidan shi saboda tunanin shi Khadija na can,π tsohon zance, ai kuwa da ya je dai bai samu samu kowa a gidan ba, kiran Khadija ya yi yace "Ki na ina ne?" Da mamaki Khadija tace "... *Lokacin Haseenah fa ya fara fan's, yanzu nasan za ku ji dad'i.* _Ma chΓ©rie *Hakeema* barka da samun k'aruwar 'ya mace, Allah ubangiji ya raya mana ita akan sunna, zafa musha shoki yan uwaπ nasan baku tab'a gani na ina kwaso shoki ba._ 01/03/2020 Γ 14:18 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` _Wannan page ta ki ce ke kad'ai mahaifiya kuma maman mu da tafi kowa, my sweet and lovely ki bayar da wannan page ga *Momy na*, Allah ya k'ara girma da lafiya mai anfani._ _Bismillahir rahamanir rahim_ *34* "Ban gane ina ina ba?" Cikin tausasawa yace" To ranki shi dad'e Hajia uwar yarima ina aka je ne? Saida ta furzar da iska tace "Ka fad'a min abin da ya sa ka kira ni amma ba wannan ba." A hankali yace "Nana Khadija ina k'ofar gida yanzu haka kuma babu kowa a ciki, sannan daga gidan su Hajia na ke ba kya can, yarima yace min kin zo gida amma kuma ban same ki ba, ina ki ka je ki fad'a min?" "To me za ka min da ka damu da sai ka ganni?" Ta fad'i hakane saboda tasan in har cikin jikin ta to fa ta shiga uku, dan sai ya yi mata abin da yace zaiyi, shi kam a cewar shi "Ina son ganin ki ne, ki fad'a min ina ki ka na je na d'auko ki tunda na ga motar ki aje." Haushi ne ya kamata tace "Kaga malam ina d'an wani aiki, sai anjima." Datse kiran ta yi ya bi wayar da kallo, a hankali ya furta "Me ya samu Khadija ta ne haka? Ba ta min irin haka fa." Shawara ya yanke ya kira wayar Hajia, ta na d'auka yace "Hajia Khadija na ce ko ta na nan gidan?" Da mamaki Hajia tace "Khadija kuma, ai ko da ta yi sallahn magriba ta tafi gida." "To Hajia kuma gani a k'ofar gidan ba ta nan, na kira ta kuma ta k'i fad'a min in da take." Yanda ya ke maganar cikin damuwa ya sa Hajia cewa "To ka shiga cikin gidan mana sai ka tambayi Hajiar ta, ita ai ba za ta kasa fad'a ma ka ba, ita ma nasan ba ta fad'a ba ne saboda ta na jin haushin ka." Da mamaki fal a fuskar shi yace "Hushi da ni kuma? Hajiar ta? Hajia wai me ki ke fad'a ne? Ban gane ba sam wallahi." Fahimta da Hajia ta yi akwai abin da ya faru ne ya sa tace "Yanzu dai in ganin ta ka ke so ka yi ka je gidan su, ni kaga ina wasu harkokin." "Hajia wai me ta ke yi a gidan su? Dan Allah ki fad'a min ko na ji sauk'i, wallahi ji na ke kamar na tashi a bacci." Shiru Hajia ta yi ta na tunanin abin da za ta fad'a ma sa, kamar zaiyi kuka yace "Hajia ki taimaka ki fad'a min mana, dan Allah ki ce ba wani mugun abu na yi wa Khadija da har ya sa ta tafi gidan su, Hajia kinfi kowa sanin Nana ita ce rayuwa ta, dan Allah ki cire ni a duhun nan." Cike da k'aguwa Hajia tace"Fodio, na ce ka je godan nasu ka same ta ko." Ikon Allah sai kawai Usman ya ji hawaye a fuskar shi, cikin rawar murya yace "Hajia sakin ta na yi?" Jin muryarshi ya sa Hajia jikinta yin sanyi, tabbas sunyi kuskure a baya da su ka nunawa Khadija k'iyayya, gashi alamu na nuna cewa Khadija dai ita ce rayuwar d'an su, jin shiru ya sa yace "Hajia na shiga uku idan sakin ta na yi, Hajia tun yaushe ta ke gida?" Kashe wayar kawai Hajia ta yi ta aje gefe ta fito waje su ka ci gaba da harkokin gaban su, sai dai kuma hankalin ta ya koma kan Usman da abin da ke faruwa, Haseenah na d'aki zaune ba aikin fari bare na bak'i sai kallon mai bisa ruwa takewa kowa, Usman kam daga nan baiyi k'asa a gwiwa ba wajen wucewa gidan su Khadija ya na addu'a a zuciyar shi "Allah ka sa ba wani abu nayi wa Khadija ba, Allah na rok'e ka kasa ba fad'a mu ka yi ba." Wani lokacin kuma mamakin kasa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117