Chapter 77
Chapter 77
Zan kira Baba na fad'a mi shi ya yi hak'uri zan je anjima, shikenan kinji dad'i?" Dariya ta yi ganin ya cire hular shi da takalma ya fasa tafiyar, ko farfajiyar gida babu wanda ya lek'a a cikin su suna d'aki suna soyayyar su, hatta abinci sai dai ya kira Bilyamin ya siyo ya kawo mu su, haka dare ya yi amma Haseenah na jikin Usman, da ya yi maganar tafiya wajen Baba za ta fara shagwab'a wai zai barta ita kad'ai, haka ya k'arar da wunin na shi bai je kiran Baba ba kuma bai kira shi a waya ba. Tunda malam ya ga shiru ya tabbatar da zargin shi na cewa akwai abin da ke damun Fodio, ganin har dare ya yi anyi shirin bacci ya sa malam samun Hajia a d'aki har ta fara bacci ya tashe ta, saida ta wartsake yace "Bacci fa bai kama ki ba, tashi ya kamata ki yi mu duk'ufa da addu'a, dan shakka babu Fodio ba kan shi d'aya ba." Saida ta k'ara murza ido tace "Malam, ban gane ba, me ya ke faruwa da Fodio kuma?" "Shiga gaba." Ya bata amsa kai tsaye kafin ya d'ora da "Na yi mamakin da ku ka kasa fad'a min gaskiyar abin da ya faru a gidan shi, kun fad'a min ta karb'i makulli da k'arfi, amma ba ku fad'a min ta karb'a bane saboda za ta kai Bilal asibiti, yaron da aka barwa Haseenah ya wahala saboda babu mahaifiyar shi nan, sannan shi kuma Fodio bai fad'a min ya daki Khadija ba, ke ma kuma ba ki fad'a min ba." "Duka malam?" Ta fad'a da dafe k'irji, d'orawa ta yi da "Wallahi ban sani ba ni ma, bai fad'a min ba ko alama." Gyara tsayuwa ya yi yace "Har da duka, kinga yanda ya kumburawa yarinyar nan fuska da kin tausaya mata, tun jiya ta na kwance babu lafiya har zuwa safiyar nan da na je gidan ana k'ara mata ruwa, wannan abun kunya da me ya yi kama? Kinga yanda ran 'yan uwanta ya b'ace su na cewa ba za ta koma ba si in ya zo ya nemi ta koma tare da alk'awarin ba zai sake tab'a lafiyar jikin ta ba, kuma ni banga laifin su ba ko kad'an dan su na da gaskiya." Shiru Hajia ta kasa magana saida malam ya sake cewa "Na fahimci yarinyar nan ta na biyar shi da sharri, ba kuma alkairi bane ya kawota gidan nan, dan haka k'arya take tace za ta cutar da ahalina wallahi, ko da boka take yawo ni nan zanyi maganin ta, Allah ya fi k'arfin ta wallahi." Kallon Hajia ya yi da zufa ta rufe ta yace "Ke ma ki taya d'an ki da addu'a." Fita ya yi daga d'akin ita kuma ta k'ara gudun masuburbud'ar sanyin dake d'akin, ta jima bacci bai sake d'aukar ta ba ta na tunani akan abin da malam d'in ya fad'a, anya kuwa Haseenah za ta iya yin haka? Yarinyar da a zahirance ita ake cutawa, taya za ace kuma ta cutar da wani? Kai da kamar wuya gaskiya. *Da kamar wuyar zata kassara ku.* 21/02/2020 Γ 19:15 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Litattafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_ π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *29* Sai k'arfe *10:25* suka tashi daga bacci, Usman ne ya fara shiga wanka da tunanin ya gaggauta shiryawa dan ya fiya kiran malam, ya sakarwa kan sa ruwa kenan Haseenah ta shigo ban d'akin, bahon wanka ta cika da ruwa ta had'a sabulu a ciki ta cire d'aurin k'irjin ta, da k'arfi ta jashi su ka famtsama cikin bahon su biyu, dama abin da take so kenan, shi ya sa ma ta yi anfani da damar wajen b'ata lokaci suna wanka da 'yar shiriritarsu irin ta amare, sun d'auki lokaci kafin su ka fito haka nan ma wajen shiryawa saida su ka jima, suna fitowa falo cikin shiri ya kalle ta yace "Mummyn beby yau ma ba ki dafa mana komai ba fa, ya za mu yi kenan?" Zaune ta yi akan kujera tare da d'ora k'afa d'aya kan d'aya ta d'auki masarrafar telebijin (remonte) ta kunna tace "To ai ina ganin ba sai na yi girki ba, tunda kaga amarci mu ke ci, ko ba haka ba?" Zaune ya yi kusan ta ya na fad'in "Kuma fa da gaskiyar ki, dan mafiya yawancin lokuta idan na dawo daga tafiya sai dai muje cin abinci kawai." Cike da izza ta na karkad'a k'afa ta kalle shi tace "Oho, kenan aka ake yi, amma shine ni ba za ka iya d'auka ta ba muje?" Waya ya ciro daga aljihu yace "Yanzu dai bara na fara kiran Bilayamin ya kawo mana na karin kumallo, anjima da dare sai muje mu ci ko, hakan ya mi ki?" "Ba damuwa." Ta fad'a cike da k'asaita, ta na ji ya bawa Bilyamin sallahun abin da suke buk'ata su ci, bayan d'an lokaci Bilyamin ya iso da abincin, ya na karb'owa kai tsaye kan teburi ya nufa da shi ya d'auki faranti ya zuba ya kalle ta daga in da ta ke zaune yace "Madame ki taso abinci na jiran ki." Tashi ta yi cikin tako d'aya bayan d'aya ta isa, zaune ta yi akan cinyar shi ya dinga saka mata abincin a baki, saida su ka gama ya tashi zai fita tace "Babban mutum ni fa gida na ke so ka aje ni, idan za ka shigo da dare sai ka biya mu taho tare." "Gida kuma?" Ya tambaya da mamaki, "Eh, gida." Jim ya d'anyi dan gaskiya a tsarin shi ba'a mi shi haka ko kad'an, ace sai yanzu ne kawai za ta fad'a masa ta na so ta fita kuma yanzu yanzu saboda raini, had'e fuska ya d'anyi yace "Ki yi hak'uri mana Mummyn beby, ki bari har gobe sai kije." Yamutsa fuska ta yi tace "Gaskiya yanzu na shirya tafiya, in kuma ka hana ni wallahi kuka zan kwana ina yi a gidan nan." Ta na gama fad'a ta mik'e ta nufi hanyar falon ta, ganin fa da gaske ranta zai b'ace ya sa ya yi saurin rik'o ta ya had'a da jikin shi yace "Shikenan to naji, ran gimbiya ya huce, je ki d'auko hijabin ki sai mu tafi." Cikin farin ciki tace "Da gaske kake?" Cike da tabbatarwa yace "Sosai ma, ai ba na da wani abu da ya fi min ke mahimmanci, zanyi hidimar ki kafin na yi tawa, ki yi sauri ki je." Cikin d'an lokaci ta d'auko hijabi da jaka da takalma duk kala d'aya suka tafi, ba jimawa ya sauke ta gida tare da bata kud'i kafin su ka yi sallama, mahaifiyar ta kad'ai ce a gidan a farfajiyar gida zaune, bayan sun gaisa sosai suka fara tab'a hira, anan ne mahaifiyar ta tambaye ta ko ta na anfani da magungunan ta, bud'ar bakin ta cewa ta yi "Eh, ina sha
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117