Chapter 51
Chapter 51
hawaye tace "Eh." Juyawa ya yi rai b'ace yace "Saida safe." Har ya bud'e k'ofar kuma ya tsaya yace "Baba ba shi da lafiya ya na asibiti,ku yi k'ok'ari da safe ku je ku ga jikin shi." Fuskar ta kad'ai ta nuna mi shi damuwar da ta shiga a lokacin, saida ta matsa kusan shi tace "Me ya samu Baba? Ya jikin na shi yanzu? Ina fata fai da sauk'i?" Sharewa kawai ya yi yace "Da sauk'i." Kamar ansa shi dole, zai fita ta sake cewa "Ka tabbatar ya na lafiya? Gaba d'aya ba na jin dad'in jiki na." Sama da k'asa kawai ya kalle ta ya wuce abin shi, daskarewa ta yi a wajen ta na tunanin abin da ke shirin faruwa da su koma ya faru d'in, ta jima tsaye kafin ta kashe wuta ta wuce d'akin ta, alwala kawai ta d'oro ta zo ta kabbara sallah, tun daga nan ta fara kaiwa Allah kukan ta tana neman agaji da mafita, sai kusan *uku* na dare bacci ya d'auke ta, kuma ana kiran sallah ta farka ta taje ta tashi Bilal shim, Usman da kan shi ya zo ya tafi da shi suka shiga masallaci. Ko da gari ya yi haske Khadija ta shiiryawa Bilal abun kari ya ci, shiryawa ya yi Baban shi ya tafi kai shi islamiyya, daga nan kuma asibiti ya wuce ya samu jikin malam da sauk'i sosai ya na ta hirar shi akan gado, ya na dawowa ya gida ya sake kwanciyar shi , Khadija kuma ta shirya dan zuwa ganin Baba, ganin shiru babu wanda ya mata magana ya sa ta kira wayar shi, a lokacin Haseenah ta gama soya k'wai da dankalin turawa ta shirya cikin ado mai kyau, ta na ganin kiran amma ta yi banza da ita, ta na ji ta na gani ta hak'ura da tafiyar sai Hajia ta kira ta tambayi mai jikin tace za ta shigo anjima. Wani abun haushi shine a lokacin Haseenah ta tashi Usman daga bacci wai sai ya kaita asibiti ta ga Baba, tun ya na cewa bacci ya ke jin har ya wartsake ya tashi ya yi wanka ya shirya, wajen tebur suka nufa su ka cika cikin su kafin yace su tafi, *11:00* cif suka fita daga gidan ba tare da sanin Khadija ba, dan lokacin ita ma har bacci ya d'auke ta daga nan haka ma Uwani saboda shirun ya yi yawa. Da isar su asibiti ta samu su Hassana zaune a bakin wata bishiya akan tabarma su na ta hira, nan ta zauna suka fara gaisawa, Hajia da ke tsaye da buta a hannu ce ta fara cewa "Yo ina Khadija? Ai na d'auka tare za ku taho tunda ta kira ni." Kalar Haseenah ta sani kam sai cewa ta yi "Aunty ai ta na gida bacci ta ke, watak'ila sai da rana ta taho." "Uhum." Cewar Hajiar ta wuce sabgar gaban ta, Rabi'a ce ta fara cewa "Hum! 'Yar hutu ce kinsan, kuma shi ba zai iya tashin ta ba saboda gudun b'acin ran ta." Husseina ce tace "To kinsan da haka ma miye na wahalar da bakin ki wajen fad'a." Hassana ce ta kalli Haseenah tace "Haseenah dai ki dage sosai kinji ko da addu'a, kar a shantake ayi ta bacci, dan matar nan da ki ke gani ba Allah ne a gaban ta ba, ke ma wallahi watak'ila tsananin rabo ne ya shigo da ke gidan, tunda ba tun yau ake mi shi maganar k'ara aure ba, amma da an mi shi maganar yanda ki ka san ka zagi uwar shi da uban shi haka ya ke kallon ka, mufa har saida ta kai ya daina sakar mana fuska." Murmushi Haseenah ta yi tace "Insha Allahu su aunty babu abin da zai faru, Allah ai ba azzalumin bayin sa bane." Husseina ce tace "Allah sarki yar albarka, Allah ya kare ki daga sharrin ta." "Ameen." Ta fad'a da murmushi, mik'ewa ta yi tace "Bara na shiga na ga jikin Baban." Ledar bayan ta ta janyo mai d'auke da kayan marmari kala kala ta d'auka ta wuce, da kallo su ka bita kafin Hassana tace "Wallahi yarinyar tausayi ma take bani, sukuku da ita ba kazar kazar." Rabi'a ce ta yi tsal tace "Ai ba ki ga abun tausayi ba sai randa mu ka je gidan shegiyar nan ta kusa k'ona ta, wallahi inda kinga ta ma bud'e baki ta yi magana kasawa ta yi sai da k'yar." Haka su ka ci gaba da tattaunawa har suka fito su ka mu su sallama suka koma gida, saida ya wuce ya d'auko Bilal dan lokaci ya yi kafin su ka wuce gida, k'arar bud'a k'ofa ne da mai gadi ke yi ya sa Khadija farkawa, ta ga motar Usman ce sai dai ba ta ga tare da wa yake ba, Bilal na shigowa ya tabbatar mata da shine ya d'auko, d'aki ya wuce dan cire kaya Khadija kuma ta kalli Uwani tace "Bara na shiga madafar da kai na idan bata fara aiki ba na d'ora mi shi ko indomie ce." "To." Ta fad'a ta bita da kallo, ba ta samu kowa ba dan haka ta shiga abin da ya kawo ta da gaggawa, saida ta kammala ta fito dan d'auko farantin da za ta zuba, Bilal ta gani ya fito daga d'akin da da ledar bredi a hannu da gwangwanin madara, da sauri ta nufe shi ta karb'e madarar ta na fad'in "Sau nawa zan fad'a ma ka ba na son ka na anfani da madarar nan haka kawai idan ba a cikin shayi ba." Cikin kukan shagwab'a ya biyo bayan ta ya na fad'in "Mummy yunwa na ke ji fa, ki zuba min ko kad'an ce." Juyowa ta yi ta kalli Uwani tace "Uwani taimaka dan Allah d'auko faranti a d'akin can ki juyo indomien da na dafa." "To." Dai ta sake fad'a ta nufi d'akin, Khadija dawowa ta yi ta zauna akan kujera tace "Zauna yanzu Uwani za ta kawo ma ka indomien ka ka ci." Cikin turo baki ya aje bredin ya zauna in da ta nuna masa, Uwani kuma na shiga ta samu Haseenah tsaye ta d'auki indomien nan ta na juyeta wajen da ake zuba ruwan datti, da sauri tace "Kai, aunty amarya Umman Bilal ce ta dafa ta yanzu." A wani gatsine ta juyo ta kalle ta tace "Wacece hakanan kuma?" Shiru Uwani ta yi dan ba ta san me za tace ma ta ba, hakan ne ya sa Haseenah zuwa ta shak'i wuyan rigar Uwani tace "Me na fad'a mi ki? Bance ba na son sake ganin ki a madafar nan ba idan ina girki? K'azama da ke kawai ki dinga cud'anya cikin mu sai kace kema wata matar shi ce, dallah fice min daga nan." Yanda ta tura Uwani da k'arfi sosai ya sa ta yi baya kan ta ya had'u da bango, fitowa ta yi dafe da kan ta ta samu Khadija ta fad'a mata komai, Khadija ta so ta yi magana kan abin da ta yi sai kawai ta share ta sa Uwani ta d'auko gas d'in ta suka kunna, ruwan d'umi ta fara d'orawa Bilal ta had'a mi shi shayi sannan ta sa Uwani ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117