Chapter 33
Chapter 33
ta fahimta shine Haseenah ba ta ji dad'in abin da ta yi ba, ita kuma ta yi ne saboda ita ce silar zubar mata da girkin da ta d'ora, juyawa ta yi ita ma za ta tafi sai kuma ta juyo, idon su ne suka had'u da na Usman da ke kallonta, kamar yanda tasan ba ya iya shirya kansa da kyau in ba ita ta taimaka masa ba, hakan ta ke da yak'inin ba zai iya zuba abincin nan ba in ba wani ya zuba masa ba, dawowa ta yi ta zuba mi shi ta zauna nesa da shi tace "To maza ka bada himma." Kwab'e fuska ya yi yace "In dai ba za ki ci ba ni ma haka." Kallon shi ta yi tace "Gaskiya sai dai ka jira Haseenah ta zo ku ci, wanka yanzu kawai na ke son yi." Rumgume hannaye ya yi a k'irji yace "Da alamar maganar ki ke so." Wata dubara ce ta fad'o mata dan haka ta mik'e tace "Shikenan to ina zuwa, bara na kira Bilal." Ta na fita ta samu Bilal a falo tace "Bilal, tashi mahaifin ka na jiran ka ku ci abinci, ina zuwa yanzu ka ji." "To Mummy." Ya fad'a yana nufa falon, wanka ta shiga shi kuma ya na zuwa Usman ya rumgumo shi jikin shi ya na fad'in "Yarima na ya ka ke?" Baice komai ba ya kalli Usman d'in ya na turo baki, lab'e baki Usman ya yi yace "Ko dai yaro hushi ya ke da baban sa ne saboda bai je d'aukar shi ba?" Sai lokacin ya saki fuska yace "A'a Abba, bacci na ke ji." Duk da girman yaron amma haka ya zaunar da shi akan cinyar shi yace "To idan mun ci abinci sai ka yi baccin ko?" A tare suka saka hannu su na cin abincin su na hira, har sun ida su na nan zaune suna ci gaba da hirar su irin ta d'a da uba Haseenah ta shigo, kallon ta Bilal ya yi yace "Sannu aunty." Da murmushi har kunne ta amsa da "Sannu yarima, ya ka ke?" "Lafiya lau." Ya fad'a ya na saukowa daga k'afafun Usman, fita ya yi daga d'akin Usman bai hana shu saboda ya na so ya yi magana da ita, ya na ganin fitar shi ya kalle ta da kyau lokacin da take shirin zaunawa, riga da siket ne na kanti wanda su ka kama jikin ta sosai, siket d'in ko k'asa bai gama sauka ba, sannan babu d'an kwali a kan ta, sai da ta zauna yace "Haseenah, yanzu ki na ji a jikin ki wannan kayan sun dace ki saka su a yanzu kuma har ki fito da su?" Da mamaki tace "Ban gane ba? Me wannan kayan su ka yi?" Murmushi ya yi yace "Ba fa mu kad'ai bane a gidan nan, wannan kayan da ya dace ki saka ne da dare lokacin da mu ka rage daga ni sai ke." Cike da tsiwa irin ta yan zamani tace "Matsala, wannan ita ce matsalar da ake magana in dai har ka auri me mata, ba ka isa ka sake ka wataya yanda ka ke so ba, yanzu dan Allah me wannan kayan su ka yi? Na ga kai miji na ne, me ye dan na saka wannan kayan a gida na?" Har kas'an zuciya maganar ta ta tsaya mi shi a rai, amma sai ya kawar da kai kawai ya mik'e yace "Zan fita ni sai anjima." Binshi kawai ta yi da harara, dan yau ita zuciyar ta fal take da tarin k'unci, wani faranti ta janyo gaban ta ta bud'a kwanukan, sai da taja numfashi saboda k'amshin da ya daki hancin ta, ai kuwa zubawa ta yi sosai ta kuma ci ta k'oshi ta ma manta waya girka, dan har ga Allah abincin ya mata bala'in dad'i, ko dan ta na jin yunwa ne oho. Khadija ma na gama shiryawa sai da ta yi sallah kafin ta cika cikin ta da kayan marmari da yan dubaru, daga nan kuma bacci ta shiga dan a huta ma rai. Kiran sallah ne ya tashe su duka gidan, Bilal masallaci ya nufa kafin ya dawo ya shirya zuwa makaranta, Usman da kan shi ya zo ya d'auke shi su ka tafi lokacin Haseenah har ta shiga girkin dare. *Mummyn Sultan* *Mamienmu* *My sweet Hawwer* *My lovely Hawwer* *Mummyn Ameer & Khairat* *Sis Alawiyya* *Sis Fusseina* *Momyn Rasil* _Da duk wanda baiji sunan sa ba, zaiji anan gaba insha Allah._ 23/01/2020 Γ 13:43 - πππ: ππππππππππ *KALLON KITSE* _(Ake wa rogo)_ ππππππππππ _SAMIRA HAROUNA_ *Littatafan marubuciyar* *1* _KAUSSAR_ *2* _D'AUKAR FANSA_ *3* _BA SO BANE_ *4* _AUREN HAD'I_ *5* _SANIN MASOYI_ *6* _JIHADI_ *7* _K'ANGIN RAYUWA_ *8* _ITACE K'ADDARARMU_ *9* _KAWU NA NE_ *10* _MAATA_ *11* _KALLON KITSE..._ *SADAUKARWA GA* _MATAN FARKO_π§πΌ *(UWAYEN GIDA)* πΈπ¦ *ZAMAN AMANA WRITER'S* _(Gidan zaman lafiya da amana insha Allah)_π€π€ ```Fatan alkairi masoya``` _Bismillahir rahamanir rahim_ *15* Haseenah dai a shirye take da samu zuciyar mijinta ita ma, hakan ya sa yau ma abinci ware mu su na su ta yi ta kai falon ta, sannan ta zuba maganin saboda ta na so yau ya ci na uku kenan, Bilal ta k'walawa kira tun daga madafar, hankalin shi ya tafi kan kallon da ya ke a *mbc action*, Khadija da ta fito daga d'aki cikin doguwar riga ta shadda ne tace "Bilal ba ka ji auntyn ka na kiran ka ne?" Da sauri ya mik'e ya nufi k'ofar ya na fad'in "Banji ba Mummy." Ganin ya nufi k'ofar falon ta ya sa tace "Ta na madafa ina jin." Da sauri ya nufi can, ya na zuwa ta mik'o mi shi kular abinci tace "Abincin ku kai da maman ka." Jiki a sanyaye ya karb'a ya na kallon ta da mamaki, haka ya juyo ya fito ya kawo abincin maman shi na zaune, aje kwanan ya yi gaban ta ya d'ago ya fad'a kusan k'afafun ta yace "Mummy abincin mu ne wai inji aunty." "Abinci kuma?" Cewar Khadija ta na yamutsa fuska, "Eh." Cewar shima Bilal d'in, gyara zamanta ta yi kamar wata hamshak'iya matar shugaba akan kujerar tace "Ka kaiwa mai gadi shi." Ba musu ya d'auki kwanon ya fita da shi, ya na zuwa ma har ya samu ya na cin na shi abincin, cike da ladabi ya aje kwanon gaban shi yace "Baba *Garba* ga abincin ka." Da mamaki ya kalle shi yace "Abinci na kuma d'an Alhaji? Ai gashi nan har na kusan kai shi k'arshe ma, ko dai makuwa ka yi." Da dariya Bilal yace "A'a Baba, wannan Mummy e tace na kawo ma ka." Jim ya d'anyi kafin ya janyo kwanon gaban shi ya na fad'in "Allah sarki, Hajia ta d'auka ba a aiko min da shi bane ina ga? To ka ce angode ka ji ko, ai ba'a maida abinci ba, ko almajirai na bawa tun da na koshi ma." Juyawa Bilal ya yi Garba ya bi shi da "Sai da safe d'an Alhaji." Duk abin da ya faru akan idon Haseenah wacce ke shirin rufe madafar, k'wafa ta yi tare da mirmushi ta rufe kafin ta wuce d'akin ta, sai da ta gama shirinta tsaf cikin riga da wando masu
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115
- 116 Chapter 116
- 117 Chapter 117