Skip to content

Chapter 92

Chapter 92

Zuciya Kowa Da Irin Tasa Book One Complete Hausa Novels 1,162 words 0 views Progress saved
Download Book

tsohon wanda kowa yake kyararsa sai cimai mutunci akeyi. Nan Ashraf ya taimakamai ka maidashi gefe, wani mutum ne ya jawoka yace " kai yaro ka raba kanka da wannan tsohon maye ne." Ashraf ya kalleshi shikam yarinta baisan ma me ake nufi da maye ba ya koma gunsa tare da d'auko abin sadaka guda biyu ya kaimai. Duk inda Ashraf yai sai mutumin nan ya bishi da kallo wanda hakan yasa muma jikinmu yai sanyi. Bayan kowa ya watse mutumin nan na nan a zaune ya taso dakyar yazo gun mu. Abbas ya kalleshi yace "Baba lafiya?" Tsoho ya kalli Ashraf wanda ke gefe yana alwala ya kalli Abbas yace " kaine babansa ko?" Cikin mamaki Abbas yace " ya akai ka sani?" Tsoho yai danyi dariya sannan ya kara kallan Ashraf ya kuma kalli Abbas yace " kwanakinka basu da tsayi, ko ince kwanakin ka sunzo karshe." Malam cikin b'acin rai ya kalli tsoho yace " kai miye hakan? Ta yaya zakazo ka samu mutane ka dinga fadamusu zancen banza haka? Kai Allahn masaru ne?" Tsohon ya girgiza kai sannan yace " ko d'aya ba kuma na fada bane dan ranka ya b'aci ba sai dai kanada makiya dayawa na jikinka kuma." Abbas ya kalleshi cikin shakkun kalamansa tabbas yasan yanada makiya amma bayasan aminta da maganan wannan tsohon da ya kai kusan shekara 100. Tsoho ya kalli Ashraf yana murmushi yace " kayi dacen d'a sai dai rayuwarsa zata zama a kewaye take da makiyansa." Abbas da Malam kawai kallan tsoho sukeyi, tsoho yacigaba " sai dai akwai farinciki a rayuwarsa in har ya rike matarsa ta farko, in kuwa ya rabu da ita banaji akwai wani farinciki da zai samu a rayuwarsa." Abbas ya mike cikin mamakin mutumi yace " malam wani irin zance kakeyi haka? Tayaya daga ganin yaro zaka fara cewa wai ba farinciki a rayuwarsa? Kasan me kake fada kuwa?" Tsoho yace " kamar yanda makiyanka na jini basa sanka kana tunanin zasuso d'anka?" Yana kainan ya juya zai tafi sai kuma ya kara juyowa yace " D'anka zai zama abin alfahari ga mutane, matar da zai aura ta farko itace zata zamar mai farincikinsa nan gaba." Yana kainan yai gaba, Abbas ya bishi da kallo kafin cikin tsoro yabi bayan mutumin sai dai babu shi ba alamar sa. Mai gari dake zaune yanajin komai ya kalli Abbas yace " Mutumin nan da kake gani ba wanda ya sanshi, shekararsa kusan d'ari ba aure ba zuri'a ba komai, ba wanda yake kusantar ko da magana dashi ne, sannan abun tsoro ga mutumin in dai ya fadi abu to fa sai dai wani iko Allah, shiyasa muke tsoron harka dashi, wasu sunce maye ne, wasu sunce baiwa gareshi wasu sunce kambun baka wasu sunce aljani ne, a zahirin gaskiya kowa da abinda yake fada sai dai Allah ne kadai masani." Malam ya kalli Ashraf wanda gaba d'aya shi hankalinsa nakan Malam. Malam yai murmushi yace "munyi mamaki kwarai da abin al'ajabi na wannan tsohon sai dai abinda ya tsoratamu shine mun gama sadaka muna kokarin tahowa aka sanar da mai gari mutuwar wannnan tsoho." Idanu Ashraf ya zaro yace " muna garin ya rasu?" Malam yai ajiyar zuciya yace " ban taba ganin abin al'ajabi irin wannan ba." Ashraf yai shiru yana kallan malam. Malam yace " shiyasa dakazomin dazancen rabuwarka da matarka ta farko naki aminta saboda inaji a jikina itace farin cikinka, bawai dan na yarda da abinda wani bawa na Allah ya fada ba sai dai shi dan Adam Allah ne kadai yasan baiwar dayama kowa." Ashraf yai shiru kafin daga bisani yace " to inkuma da ace Anisa na fara aure fa?" Malam yai murmushi yace " shiyasa nacemaka baiwar dan Adam Allah ne kadai yasan yawanta, dama can Allah ya tsara ba ita zaka fara aura ba." Ashraf yai shiru, tunaninsa ya tsaya cak. Malam yace " muje inada gun zuwa." Ashraf ya fito jiki a sanyaye ya shiga motarsa, idanunsa ya lumshe a zuciyarsa yace " kaddarace ta kaini kauyen garinsu, shi dama d'an adam rayuwarsa a tsare take." Sako ne ya shigo wayarsa ya d'aga wayar ya karanta kamar haka " _yaya inasan zuwa gidansu Ferry in ka bani izini, sannan zan kai mata kudin anko_" Kallan sunan daya sa mata yai Baby Feenah, a hankali ya goge sunan ya maidashi Nafisa. Yana kallan sunan daya canza mata ya furta a fili, I Am sorry Nafisa sai dai wannan ce hanya kadai dazaisa inyi fooling din kowa, inhar na sanar dake plan dina ba zakiji pain ba akan abinda zanyi sai dai hakan zai sa a gane ba gaskiya bane. Yai ajiyar zuciya tare da cewa " I am sorry for using u." Mota ya tada sannan yai gaba. Gidansu Habib yai ya tsaya a wajen gidan ya kurama gate din gidan ido, bakincikinsa yanda yakesan Dady da Habib, yanda yakesan kannen Habib, ya kara kallan gidan yace " Dady kaci amanata." Ya dade kafin daga bisani yaja motarsa yai gaba. Gida ya wuce, direct bangaren Umma yai, Umma tanajin sallamarsa mamaki ya kamata cikin zumudi. Bayan ta bud'e ya shiga kamar yanda ya saba fuskarshi a daure. Zama yai sannan ya kalli Umma tare da gaisheta. Umma ta baje baki tace " Ashraf yau da kanka?" Kasa yai dakai yace " Umma hakkinane ai." Ta kara washe baki yace " Anisa fa?" Tace " tad'an fita dazu." Murmushi yai yace " ok ba damuwa bari na wuce." Tace " a'a ka zauna insa a kawoma abinci." Ba musu ya amince da hakan." Da sauri Umma ta fita kamar ya sani sai ta sanar da Mumy, yana zaune kuwa ya fara cin abinci kenan sai ga Afra. Ta gaisheshi sannan yaga ta juya, ya sani mumy ce ta turota akan ta tabbatar ko yana can d'in. Ashraf yai murmushi ya cigaba da cin abincinsa. Ya kusa gamawa sai ga Asim. Asim mamaki ya kamashi cikin tsananin mamaki ya karaso yace " Kai kuma me kakeyi anan?" Ashraf ya kalli Umma. Da sauri Umma tace " ni nace ya zauna yaji abinci." Asim ya mata kallan mamaki, kallansa tai tamai alama da yaje d'akinta. Nan yai gaba ta bishi a baya suka rufo kofa. Ashraf ya mike ya bi bayansu. Asim ne ya kalli Umma yace " Umma meye hakan?" Tai dariya tace " Asim bansan meyasa kanka baya ja ba yaron nan yanzu ya san matsayin Anisa a zuciyarsa baka tunanin lokacine daya kamata muyi amfani dashi dan jansa a jikinmu?" Cikin fada yace " mujashi a jikin mu kamar ya?" Tai dariya tace " yanda zai saki jiki damu har ku gama gano komau kafin musan abinyi akansa." Asim yai dan tsaki sannan yace " Ni Abba ne ke ban haushi sam yana nuna ni ba komai bane." Umma ta kalleshi tace " kamar ya?" Ya kara tsaki yace " share, amma Umma menene a cikin wannan akwatin na kasan d'akin Abba?" "Shiiiiiiii" tamai alama da hannu tace " bakada hankali ne? Sai an jika? Ni kaina saboda wannan akwatin yasa inaji baya barin matansa sudinga shiga mai d'aki, inaji akwai wani sirri babba a ciki." Ashraf ya kalli kofar kafin ya juya yai gaba, akwati???

Table of Contents

Chapters

115 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115