Chapter 30
Chapter 30
" Little wa aka saima kayan nan? " Little ta kalleta rai b'ace tace " Ya Neesa me ya dameki da wanda aka saiwa? " Aneesa ranta ya b'aci ga kawarta a zaune a kusa da ita, tace " mene?" Little a zuciye ta karaso tace " Ya Neesa wai meke damunki ne? Taya zakiga kayan mutane kawai ki zubar a kasa? " Kawar Aneesa ta kalli Little tace " lalai Little yaushe kika zama mara kunya haka? Aneesa ba yayarki bace? Sannan yanzu da kika ganni anan tsara shirye shiryen da za'ai da bikinta da yayanki mukeyi ai ko bata zama matarsa ba ai yayarki ce bare an kusa. " Little ta kalleta a kule sai dai ta kasa magana ta kalli Nafi cikin takaici ta wani takure kanta a kasa zatai magana kawai sukaji ance "Tsugunna ki kwashe kayan da kika zubar. " Gaban Aneesa ne ya fad'i ta juyo a tsorace, ba ita ba Little da Nafi ma kofa suka kalla haka ma kawar. Ashraf ne a tsaya kana ganinsa kasan ba wasa a fuskarsa, Little ta kalli Habib wanda ke tsaye daga kofa, a ranta tace " yaushe ya kira shi? " Aneesa ta kalleshi tace " Yaya.... " Wani kallo ya mata wanda yasa ta had'iye maganar ta cikin tsawa wacce ta razana kowa dake falon yace " Kowa ya fita." Nafi kam jikinta rawa ya kauri dashi, bata tabajin yayi tsawa haka ba, Little ta kamata sukai waje a sukwane itama kawar Aneesa da sauri tai waje ta nufi d'akin Umman Aneesa. Ya rage daga Aneesa sai Ashraf a d'akin, ya kara kallanta yace " ba dake nake ba? " Idanunta na kansa kallan mamakin dizgata dayai take, ta daure tace " Yaya ni zaka wulakanta akan Nafi? " Shi baimasan a hannun Nafi aka anshi kayanba, shidai Habib yace yazo akwai matsala a b'angaren su Little, da ya iso shine yake cemai Mumy ta siyo kaya Aneesa ta zubar. Ashraf ya kara kallanta, idanunta suka ciciko tace " Yaya kana san ka nunamin ka fifita Nafi akaina kenan ko me? " Ashraf ya kalleta cikin tsananin takaici zaiyi magana kawai sai ga Asim da Umma sun shigo cikin masifa........ *THE INNOCENT TEAM* *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* *25* Nafi wacce little ke janta akan su tafi b'angaren Mumy tana ganin Umma da Aslam sunyi b'angarensu a fusace yasa ta turje tare da kallan Little tace " Maryam wannan abun duk laifinane, kina ganin abun nan yana neman ya zama babba? Sannan ni kuma in gudu?" Little ta tsaya itama tare da cewa " Laifinki? Ta ina ya zama laifinki?" " laifinane mana tunda dai a hununa aka amshi kayan." Haushi ya kama Little ta rasa Nafi wace irin yarinya ce, ta kalleta tare da dafata tace " Naji a kaddara laifinki ne mai zakiyi in kika koma?" " Hakuri zan bada mana kina ganin su Umma sun tafi nasan kowa laifin yaya zai gani." Ta karasa maganar cikin rawar murya. Little ta kalleta sai dai ta rasa me ma zata ce mata, gani tai Nafi ta fara tafiya nan ta bita tana mata magiya akan su tafi sai dai itakam gani take gwara taje kawai. A falo kuwa Ashraf ne ya had'e rai kamar zai dake Aneesa ita kuma tana tsaye kyam kusa da kaya, ta kalleshi tace " Yaya nice fa?" Ya buga mata wani kallo yace " kece wa? Ko dama a duniya akwai wanda ya isa inyayi ba daidai ba a kasa hukuntashi?" Daga bayansa yaji ance kwarai kuwa, Asim ne yai maganar ya sani shiyasa kuma bai juya ba, Asim ya karaso rai b'ace sannan ya sa hannunsa ta bayan Ashraf iya karfinsa da niyar kai mai duka, Umma tai saurin rike hannun tare da balamai hararra. Ashraf ya kalli Aneesa yace " idan kika bari na irga uku acikin raina wlh sai kinyi dana sanin wannan ranar." Umma tai charaf tace " ai kuwa sai dai tayi dana sanin dan kaf duniya ba wanda ya isa ya sa 'yata ta kwashi kayan wannan yar kauyen." Ashraf bai kalli Umma ba haka kuma bai bata amsa ba sai Aneesa da yake kallo yace " kin amince da abinda aka ce?" Aneesa ta goge kwallarta tace " yaya me zakayi in na ki kwashewa? Badai cewa zakai ka fasa aurena akan wannan shirman ba?" Ashraf ya saki wani mugun murmushi yace " me? Kina ganin bazan iya ba?" Kallan mamaki sukamai su duka ukun, Aneesa wacce duk ta gama rikicewa tace " Ya Ashraf me kake fada haka?" Ya kalleta yace " in kina tunanin bazan iya ba ki bar kayan nan har na karasa bakin kofa, ni kuma zan nuna miki magana d'aya nakeyi." Nan ya juya Aneesa ko kara wata maganar batai ba ta shiga saurin kwashe kaya kamar zata kifa kansu, Ashraf kam ko a jikinsa ya wuce ta jikin Asim ba tare da ko kallan su yayi ba, bai kuma kara duba Aneesa ba dan yasan tabbas zata kwashe kayan nan. Ana kai kofa, Nafi wacce ke tsaye jikinta sai rawa yake ta kalleshi a tsorace, bai kulata ba yai wucewarsa, Little ta dafa Nafi tace " Nafi jikinki rawa yake." Juyowa Nafi tai cikin tsananin tsoro tace " Maryam wani irin mutum ne yayanki? Da gaske sai ya raba auren nan a dalilin da baikai ya kawo ba?" Little tai shiru dan itama abin ya bata tsoro, Nafi ganin haka yasa ta girgiza kai tace " Maryam yayanki na bani tsoro dan ko Baffa banajin tsoronsa kamar yanda nake jin na yayanki." Little ta dafata tace " yayana yaga rayuwa wanda itace ta maidashi haka, baya tausayin kowa ba kuma ya shakkar kowa, abu d'aya ya tsana kuka bayan wannan banaji akwai abinda ke tab'a mai rai." Nafi tabi bayan inda Ashraf yabi da kallo, ace wacce zaka aura kuma kake so ita zaka dizga haka agaban iyayenta da yayanta? Kuma ya juya ya fita kamar ba abinda ya faru? Little ce ta katseta da cewa "Nafi ina zuwa."ta juya da sauri. A falo kam Aneesa tana ganin fitarsa bayan ta gama kwashe kayan ta tsugunna agun tare da fashewa da wani irin kuka mai ban tausayi, Umma ta karaso kusa da ita jikinta itama a sanyaye ta jawota jikinta. Kuka sosai Aneesa takeyi, Asim ya kalli Umma cikin takaici yace " Umma haka zamu zauna yaron nan yqna ci mana mutunci?" Umma ta kalli Aneesa tace " da kinsani baki kwashe ba inga ta karyar iskanci." Aneesa ta mike daga jikin Umma tace " Umma kamar bakisan Ashraf ba? Kin manta abinda ya faru shekarun baya da suka wuce? Kina sane da ciwon danai tayi a lokacin dayace bazai aureni ba, ya kuma daina kulani." Umma tai shiru, Aneesa cikin kuka tace" alokacin bansan ciwon kaina sosai ba, kina tunanin inya fasa aurena yanzu zan iya rayuwa?" Asim a kule yace " Dalla yima mutane shiru, sai ki kasa rayuwa dan an rabaki da Ashraf?" Aneesa ta harareshi sannan ta mike cikin fushi tana kuka tace " kana tunanin in Ashraf bai aureni ba zai barka a matsayin da kake ne? " Asim yai shiru, Umma tace " ya isa,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115