Skip to content

Chapter 91

Chapter 91

Zuciya Kowa Da Irin Tasa Book One Complete Hausa Novels 1,155 words 0 views Progress saved
Download Book

taga Mumy ta mike tayi waje, ta bita da kallon tausayi. Ta dade a zaune agun kafin ta d'au wayarta ta kira Ashraf, sai dai duk yanda wayar ke ringing bai d'auka ba. Ta ajiye wayar tare da kwantar da kanta jikin kujera. *********** A b'angaren Ashraf kuwa yana azahar ya wuce gidan Uncle bayan sun zauna a falo sun gaisa Ashraf ya kalli Salim yace " Uncle a labarin da ka bani kwanaki banaji kacemin an anso kayan su Dady." Salim yai shiru yana kallan Ashraf. Ashraf ya cigaba " nasan asibiti da makarantar sa na Abba ne amma bansan gidajen hayansa nawaye ba." Salim ya shafi fuskarsa da hannayensa yace " Ashraf you are very smart,ban taba tunanin zakai zargin wani abu ba game da wannan, shiyasa ma ban sanar dakai komai ba." Ashraf ya kalli Uncle yace " me ke faruwa?" Salim yaja numfashi yace " a lokacin da mahaifin Ruma ya rasu bayan an gama zaman makoki Hisham ya shiga gararin rayuwa, kaf kudinsa sun kare bayan rashin kudin ashe har loan yaci a banki wanda ya jinginar da gidansa. Bayan an gama zaman makoki 'yan bankin sukazo amsar kudinsu kamar yanda ya sanar dasu lokacin dazai biyasu. Sai dai a lokacin gidansa abincin ma dazasuci nema yake ya gagaresu. Da yake Ruma na gidan ita ta kira Abbas ta sanar dashi halin da ake ciki nan ya je bankin ya biyasu kudinsu sannan makarantar da yake masifar so ya mallakama Hisham duk dan ya farantamasa, sai dai kwanansa d'aya da bashi makarantar Allah ya d'auki ran Abbas." Ashraf yai shiru kafin daga bisani yace " asibitin fa?" Salim yai ajiyar zuciya yace " Ashraf wannan sai bayan rasuwar mahaifinka sukazo min da takarda akan Abbas ya mallakama Hisham asibitinsa da aka gama ginawa ko fara aiki ma ba'ai ba." Ashraf cikin rashin fahimta yace " ta yaya ya bashi makaranta mai girma irin wannan ya sai mai gida sannan ya kuma bashi asibiti?" Salim ya kalli Ashraf yace " nima da naki yarda da bada takardun asibitin to amma abin mamaki rubutun mahaifinka ne." Cikin fada Ashraf yace " zasu iya sa expert su kwaikwaya ai." Salim yace " yes shiyasa naki yarda sai dai mahaifiyarka itace tace tabbas Abbas ne ya rubuta." Shiru Ashraf yai kafin yace " gidajensa fa?" Salim yace " bansan wannan ba gaskiya sai dai bayan mutuwar Abbas naji jita jita akan bai daina safarar bindigogi ba zai iya yiwuwa da su ya siya ko kuma gadon Ruma ne." Cikin mamaki Ashraf yace " gadon Mumy?" Salim yace " ban tabbatar ba amma tunda kace gidaje dayawa nasan tanadasu dan Abbas tun yana da rai yake siyan gida da sunanta sannan da ya rasu aka bata gadon wasu." Ashraf yai shiru baice komai ba, Salim ya dafashi yace " Ashraf mahaifinka burinshi kai rayuwa mai dadi ba wai ta wahala da kunci haka ba." Murmushi Ashraf yai yace " Uncle kana tunanin zanyi rayuwa mai dadi bayan duk 'yan uwana makiyan Abba da ni suna zagaye da ni?" Salim baice komai ba sai kallan Ashraf dayake yi. Ashraf ya sake murmushi yace " ka binciko min inda Auwal Max din yake?" Salim yace " eh to wanda yake binciken yace yana zariya sai dai yace in kara mai 1day ya tabbatar da shi din ne." Kai Ashraf ya jinjina sannan ya mike yace " kace kafin Abba ya rubutawa matata wasiya munyi tafiya zuwa wani kauye dashi ko?" Salim ya jinjina kai yace " kwarai kuwa saboda bazan manta lokacin ba nayi mamaki kwarai daya kawon wasiyyar da daddare." Ashraf yace " Malam Mahmud ko?" Salim ya daga kai alamar eh. Ashraf yai godiya kafin yai waje. Mota ya fad'a ya d'aga wayarsa sakon Nafi ne yaga ya shigo kamar haka " _Yaya dafatan kaci abinci?_" Ya dade yana kallan sakon kafin ya ajiye wayar ba tare da ya mata reply ba. Makaranta ya wuce, yai sa'a kuwa yana zuwa Malam na kokarin fita, nan ya ajiye mota ya karasa suka gaisa, Malam yai murmushi yace " Muhammad daga ina haka?" Ashraf yai murmushi yace " gaisawa nazo muyi." Malam yai dariya yace " nagode da baka manta da wannan tsohon ba." Nan sukai dariya, Malam yace " Ina Matar taka?" Ashraf yace " tana nan." Malam yace " yarinyar fa nake nufi." Ashraf yadan sosa keya. Malam yai murmushi yace " da alama tana nan." Ashraf ya kalleshi yace " malam tambaya nazo da ita." Malam yace " Allah g yasa na sani." Ashraf ya nisa sannan yace " kafin Abba ya rasu munyi tafiya ni da kai da shi ko?" Malam yace " Hakkun." Ashraf yace " Malam zaka iya tuna abinda ya faru a lokacin?" Malam yai murmushi yace " shekarun da yawa na dai san munje zagaye da taimakon bayin Allah dake da bukata, wannan shine tafiyarsa ta karshe." Ashraf ya jinjina kai yace " ba wani abu na mamaki da ya faru game da ni?" Malam yai shiru kafin yace " tabbas akwai na tuna, abinda ya dade yana bani mamaki." Ashraf ya kalleshi cikin zakuwa da sanjin menene. Malam yace " mu shiga ciki." Nan suka nufi makarantar. ********** Yau Datti yana tsakiyar bacci ya tashi cikin firgice tare da kwallama Nafi kira, sai kuma ya saki wani irin kuka mai ban tausayi. Yayansa ya shigo d'akin a tsorace ganin tsakar dare ne gashi ya tashi mutane da dama. Datti yana kuka yana cewa " a kiramin Nafi dan Allah ku taimaken ku kiramin Nafi." Yayansa ya shiga lalabashi yana cewa kai shiru Datti da alama ka samu lafiya tunda ka fara magana. Sai dai ina Datti kam abin ya canza salo daga kuka sai a kira masa Nafi kawai yake cewa. Nan suka shiga tambayarsa a wani gari Nafin take a kirata?" Kai kawai ya girgixawa alamar bai sani ba. Mamaki da tsoro ya kamasu. Mahaifiyarsa dake kwance ba lafiya tace "kila saidata yai saboda tsabar san kudinsa nikam na shiga uku na." Datti kam cewa yake a kira masa Nafi...... Nace ta yaya kenan?🤔 *#ASHRAFEENAH TEAM* 💞 *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *72* Bayan sun zauna Malam ya kalli Ashraf wanda ya nutsu yana kallansa. Ashraf ganin Malam na kallansa baice komai ba yace " Malam ya akai?" Malam yai murmushi yace " tunowa nai lokacin da mukai wannan tafiyae bakafi dan haka ba " ya fada yana gwada tsayin Ashraf a lokacin. Ashraf yai kasa dakai yana murmushi. Malam yace " A wannan rana munje kauyuka da dama na kusa da na nesa, a karshe muka isa wani gungurmin kauye, wanda 'yan garin kana ganinsu kasan suna cikin tsananin wuya da talauci, nan muka isa gun mai garin aka tara 'yan garin aka fara basu sadaka, kaima kana mikawa. Gun yayi cunkoso wanda ya janyo turereniya agun, wasu suka dinga faduwa saboda karfin da kowa yake gwadawa. Ganinka mukai kabar gun rabon da dan gudunka. Nan Abbas ya leka ya ganka gaban wani bawan Allah, tsoho ne tukuf gaba d'aya gashin kansa fari ne ya tsufa sosai, wanda aka tureshi garin rigima ya fadi kasa. Da saurinka ka karasa kana neman d'aga mutumin,

Table of Contents

Chapters

115 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115