Chapter 66
Chapter 66
ta hakura sai zuwa gobe ta samu yin magana da Ashraf in ma wasa yake to lalai kar ya sake mata irin wannan wasan. Shikam Ashraf hankalinsa a kwance yai baccinsa, itakam Nafi akan sallaya tai bacci tana jiran Little. Little ta shigo taga Nafi na bacci, shiru tai ta tsaya tana kallanta har ta kai hannu zata tasheta ta koma kan gado ko me ta tuna? Sai naga ta fasa, kayanta ta cire tai kwanciyarta. Mumy tana shiga b'angarensu taga Kawu a tsaye sai zirga zirga yake, yanzu in har da gaske Nafi matar Ashraf ce kenan ko sun kawar da Ashraf itama tanada gadonsa? Gadan me? Bayan ba wanda yasan da auren iya kaci su karyata hakan. Ya zarfafa a tunani sam baiji sallamar Mumy ba sai jiyai ta dafashi, kallanra yai sannan ya zare hannunta ya koma kan kujera ya zauna tare da daure fuska, Mumy ta karasa gunsa tace " Me ya faru?" Ya kalleta yace " Abinda yaran nan yai yana matukar damuna, nasan Ashraf bai daukeni a matsayin uba ba sai dai ban taba tunanin zai wulakantani haka ba." Mumy tai ajiyar zuciya tace " nikaina abin nan ya tabani, sai dai ina gani ya fadane kawai, gobe zanje in mai magana ai aure ba hauka bane." Washegari da sasafe su Nafi na bacci sukaji buga kofa kamar za'a b'ala kofar, a razane suka tashi, Little ta bud'e kofar da sauri. Anisa ce a gefenta kuma Umma ce fuskarnan kamar me? Banko kofar sukai tare da shigowa ciki suka gifta Little tare da wucewa gurin Nafi wacce ta mike zaune sai dai kana ganinta kasan a tsorace take, Anisa ta karaso a zuciye ta d'aga hannu zata kifa ma Nafi mari, da sauri Nafi ta rike hannunta duk da tana tsananin tsoron yanda taga fuskokinsu sai dai bazata yarda da duka ba kuma. Anisa ta kalleta cikin tsananin kishi tace " ke har kin......." Umma ce tai saurin kifa ma Nafi wani wawan mari ba tare da ta zata ba, Nafi ta sake hannun Anisa tare da rike kuncinta ta kafe Umma da ido, Umma cikin mamaki tace " ni kike ma wannan kallan?" Nafi ta dauke idanta jitai Anisa ta rufe ta da duka gaba daya hannayenta, Little ta karaso zata tare, Umma ce ta riketa tace "meye naki a ciki? Ke bakya kishin cin mutuncin da akama 'yar uwarki?" Little ta tsaya jiki a sanyaye, Anisa kam ta dage sai sauken takaicin ta take akan Nafi, can Nafi ta mike ta rike hannun Anisa, tace "Yaya Nisa inaji yanzu kin huce ai ko?" Anisa tai sototo tana kallanta, Umma tace " mene?" Nafi wacce taji zafin dukan iya zafi ta daure tace " gani nai dukan ya isa haka inkuma ba kasheni takesan yi ba." Umma a zuciye ta fizgo wayar charger dake jikin socket tai kan Nafi zata daketa, Nafi ganin ba sarki aikam ta sake hannun Anisa tai hanyar waje da gudu, jitai ta bugi mutum, ta tsaya tare da d'agowa ta kalleshi, Umma kuma wacce suka taho itada Anisa rike da bulala zata daketa itama ta tsaya cak. Ashraf ya kallesu, yace " me kuke tunani kuke aikatawa?" Umma ta fara hucci, Anisa kuma kallan yanda Nafi ke tsaye a jikinsa take, Ashraf ya kallesu yace "Umma me kukeyi?" Umma tace " Kai dan marasa tarbiya,kayi kadan ka wulakantamin 'yata akan wata banza yar daji, kuma wlh kaji na fada maka ko ba yau ba sai na mata dukan da sai an kwantar da ita a asibiti kamar yanda aka kwantar da tawa 'yar." Murmushi ya sakar mata wanda ya bata tsoro, yace "Umma kenan banaji ranar da zakiyi hakan 'yarki ma zata kwana a gida." Anisa ta matso cikin takaici tace "Yaya mai kake nufi? In umma ta daketa kana nufin nima dukana zakai ko me?" Hannu yasa ya shafi gefen fuskar Anisa yace " No no no, kinfi kowa sanin banasan harkar duka sai dai ina nufin a ranar zamana dake ya kare." Baya baya ta fara ja, tana girgiza kai, wannan ba Ashraf dinta bane, Ashraf ya kalli Umma wacce ta saki baki tana mai kallan mamaki yace " i tried really hard inga na boye abinda ke raina, sai dai naga alamar bakusan wannan ba, dan haka daga yanzu i won't tolerate anyone ko da kuwa Little ce." Yana kai nan ya kalli Nafi yace " koma ciki ki kwanta zanga wanda zai kara gigin tabaki." Nafi kam yau ta zama kurma, a hankali ta koma ciki, Umma ta kalleta cikin takaici, Ashraf ya kalli Little yace "kin bani kunya." ya juya zai fita jiyai Anisa tace "Yaya karka fita." Juyowa yai ya mata wani kallo yace " a matsayinki na wa?" Tace "ni ai matarka ce." Murmushi yai sannan ya tako a hankali har inda take ya rungumota jikinsa sannan yakai bakinsa kunnenta yace " mata wace take shan maganin hana daukan ciki? Wacce take binciken dukiyar mijinta? Wacce take jiran mijinta ya rasu ta samu gadon sa?" Kallan tsoro tamai, ya matso da fuskarta wajen kuncinta yace " why? Kin dauka duk ban sani ba?" Ya kara mata murmushi sannan ya juya yai gaba, zubewa tai a kasa tama kasa kukan sam, Umma ta matso tace "ke ya ce miki?" Kai kawai take girgizawa, ganin haka yasa umma ta cicibeta sukai waje. Little kam da sauri tabi yayanta. Nafi kam ita kanta a d'aki zaka tai dabas tana mamakin abinda Ashraf yakeyi tun jiya, ita kanta shakkarsa take taya za'ai ya dinga fadar bakar magana hankalinsa a kwance? Bata taba ganinsa a haka ba lalai kenan akwai wani hali nashi da ya boyema 'yan gidan. Ashraf na fita bangarensa ya nufa, yau kam gidan kamar ba safiya ba kowa ya tashi, a bakin kofarsa yaga Mumy hakan yasa ya gaidata kai tsaye ya bud'e kofarsa ya shiga. Shigowa tai itama, guri ya samu ya zauna itama ta zauna a kujerar da ke kallansa, Little ce ta shigo ganinsu tare yasa ta koma gun dinning ta zauna. Sunyi shiru kafin Mumy tace " Ashraf!" Kallanta yai batare da ya amsa ba. Tacigaba "me kake nufi da kalamanka na jiya?" Cikin rashin kulawa yace "me nake nufi kuwa?abinda kikaji shine gaskiya." Ido ta kuramai can tace " kasan me kake fada kuwa? Kasan me ake nufi da aure?" Dariya yai ya kalleta yace "Mumy kenan, na dauka ko dan shekara 18 yasan me ake nufi da aure, sannan banyi tunanin zaki damu ba in nayi aure ba tare da saninki be tunda kika sake aure ba tare da sanina ba sannan kika fita daga harkata tun ina karami." Idanunta ne ya ciciko tace " Nasani i am a bad mother to you, sai dai Ashraf kai kanka kasan ba inda uwa zataki danta." Idanu ya rufe yace "gashi kuwa na gani? Tunda nake dake kin taba tambayata yaya nake?meke damuna?menene matsalata? Banaji tun mutuwar mahaifina kin kara zama dani zama na uwa da danta." Mumy tai shiru, sai idannunta da suka ciciko, Ashraf ya dan rufe bakinsa sannan ya dan sa hannu ya shafi kansa yace " inaji a jikina ba san mahaifina dani kike ba." Yana kai nan ya mike zai shiga ciki, sunansa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115