Skip to content

Chapter 83

Chapter 83

Zuciya Kowa Da Irin Tasa Book One Complete Hausa Novels 1,170 words 0 views Progress saved
Download Book

rasu ba, haka ma Mahaifiyarta bazata kwanta rashin lafiya ba. Sanda Abbas yaje gaisuwa Hashim ya sanar dashi kada ya kuskura yasa a saki kayan basa so sun kuma fahimci abinda yake nufi." Yai dan hucci sannan yace kaji abinda ya faro. Ashraf banda Inalilahi wa Ina ilaihi Raji'un ba abinda yakeyi. Can ya daure yace " Nagode Uncle." Salim har ya bud'e kofa zai fita Ashraf yace " Maganae wasiyae Abba ta matata ta farko fa? Kasan dalilin sa nayin hakan?" Salim ya girgiza kai yace " bansani ba gaskiya sai dai nasan ana gobe zaiyi hatsari kunyi tafiya dakai dashi da malam kunje kauyuka bada taimako, yana dawowa a daren ya bani wannan takardar." Ashraf yai ajiyar zuciya sannan ya kara cewa Nagode. Salim har ya fita ya dawo yace " karfa ka kawo komai a ranka, kasan Hashim na sanka." Ashraf ya daga kai alamar to, Uncle na tafiya ya kwantar da kansa a jikin kujera yana fitar da numfashi sama sama....... *#ASHRAFEENAH TEAM* 💞 *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *65* A hankali yaja mota ya nufi office ji yake numfashinsa na fita da sauri da sauri dole yai parking a gefen titi tare da kwantar da kansa kan kujera, waya ya dauka yama Dan Litti text din inda yake sannan ya maida kansa jikin kujerar. Nafi kam karfe 7 ta tashi saboda tanasan Ashraf yai break kafin ya fita, sai dai me? Bataga kowa a kusa da ita ba hakan yasa ta fito falo da sauri, nan ma ba Ashraf, ta zauna akan kujera tare da kiran numbersa, sai data kusa katsewa sannan taji ya daga cikin wata irin murya mai tsoratar da mai sauraro yace " Hello!" Mikewa tai a tsorace tace " Yaya menene? Me ya sameka?" Sama sama takejin numfashinsa ganin yanda ta rikice yasa yai saurin katse wayar. Zubewa tai a kasa tanajin zuciyarta tana kuna, hawaye ne ya zubo mata ta dafa kanta tace " wannan wani irin masifa ce? Ya Allah ka dubi wannan bawan naka ka sassautamai ka agazamai." Kara kiran wayar sa tai saima tajita a kashe. Mikewa tai da sauri ta nufi bangaren Mumy ba tare da tunanin komai ba. Mumy kam tana zaune kan sallaya tana kallan su Afra sun gama shiryawa zasu tafi makaranta, ta musu sallama sukai waje suna fita ita kuma Nafi tana shiga, Mumy cikin mamaki ta kalleta. Zubewa Nafi tai a gabanta idanunta na zubar da hawaye tace " Mumy dan Allah ki tausaya wa Yaya ki sanar dashi dalilinki nakin shiga harkarsa da kulashi da nunamai soyayya " Mumy ta buga mata wani kallo zatai magana Nafi ta katseta da sauri tare da hade hannayenta cikin sigar roko tana kuka sosai tace " kin taba tunanin yanda yake bacci da yanda yake rayuwarsa? A da na dauka ina cikin bayin Allah wanda suke bukatar a tausaya musu sai dai yanzu na fahimci cewa nice ya kamata in tausayama wasu badai a tausayamin ba, duk wahalar danasha a kauye har yaya ya tausayamin banaji nakai kashe 10 acikin 100 wanda yaya yake fuskanta" Tadan ja hanci sannan ta cigaba " He is so lonely, mutum ne wanda bai yarda da kowa ba sai kansa,Mumy nasan har kasan ranki kina tausayamai sai dai shi akullum kina daya daga cikin mutanen da suke bakin ciki ga rayuwarsa gani yake ba sanshi kike ba, kema kina daya daga kashe 20 bisa 100 na bakin cikin sa da damuwae dake ransa." Nafi ta kara matsowa tana kuka tace " Na rokeki Mumy ki tausayama wannan marayan Dan naki ki sanar dashi dalilinki na mai haka ki kuma ja shi a jiki, mutum ne wanda bai san dadin uwa ba." Idanun Mumy ne suka ciciko, Nafi tai kasa da kanta tare da share hawaye tace "indai nice bakyaso zan bar Yaya har abada zan koma kauyenmu sai dai dan Allah ki duba darajar Allah ki sassautama wannan dan naki, maraya ne shi kice gatansa in har kika nuna bakyasan jininki waye zai soshi? Na rokeki Mumy dan Allah........" Kuka ne ya kufce mata kawai ta kifa kanta akasa tana kuka, da sauri Mumy ta mike tai cikin daki, a bakin gado ta zauna itama tana kuka. Nafi kam ta dade agun kafin ta tashi a hankali tai waje, taje fita daga bangaren sai ga Anisa. Sam bata kula da ita ba saboda hankalinta sam baya jikinta. Ji tai an bangajeta da karfi har tai baya tala tala kamar zata fadi, ta dago idanunta da suka sha kuka ta kalli Anisa. Anisa ta sa hannu ta daki kafadarta da karfi tace " me? Kuka kike dan ance dole ki rabu da mijina? Ko kuwa da kina tunanin banza ta shani ne?" Ran Nafi yakai kololuwa gun b'aci, ta kafe ta da wani mugun kallo, Anisa ta matso tace " ke? Ni kike ma wannan kallon?" ta fada tana kallan Nafi. Nafi ta ki dauke idanta, haushi ya kama Anisa ta daga hannu zata mari Nafi. Nafi ta rike hannun da sauri sannan cikin dakakiyar zuciya tace " kada ki kuskura ki kara tunanin dukana, nice matar yaya ta farko, balle kiyi tunanin na miki kwace, sannan uban me kika tsinana ma Yaya? Bakin ciki? Ko me? Tun da kike dashi kin taba kula da halin da yake ciki? Kin damu da cinsa? Sannan sai anyi magana kice ke matarsa ce?" Ta cillar da hannun Anisa tace " da rashin wayau ne yasa nabar Mijina a kulawar ki sai dai yanzu ni zan kula da abina, ni zan bashi hakkin da mace ke ba mijinta." Tana kai nan tai waje a fusace. Anisa kam kasa motsi tai mamaki da tsoron yanda yarinya karama ta kafeta da ido da kalamai takeyi. Tana shiga d'akinsu ta fada kan gado, Little ce ta shigo rike da flask na abinci a hannunta, Nafi ta kalleta haka kawai taji zafin ganin Little da kular abinci. Ganin kallan da take mata Little tace " Feenah menene?" Nafi ta share kwallar ta tace " Little me yasa bakya jan dan uwanki a jiki?" Little ta mata kallan mamaki tace " wani dan uwana kuma?" Kai Nafi ta girgiza alamar ba komai sannan ta maida kanta kan gado, yau zafin kowa takeji har ita kanta, yanda numfashin Ashraf ke fita da sauri ya kasa barin kunnenta idanu ta runtse cikin kunar zuci tace " Allah ka agazama wannan bawa naka." Nima nace Amin. Ashraf nanan a zaune Dan litti ya iso akan babur. Nan Ashraf ya mike ya matsa daya bangaren shikuma ya shiga. Kallansa Dan litti yai cikin kulawa yace " me ya faru?" Kai Ashraf ya girgiza akan ba komai sannan yace " mu tafi office." Sun isa Ashraf ya shiga office dinsa ya kule kofar tare da ba secretary dinsa umarnin kar abar kowa ya shigo. Takarda ya d'ako babba ya rubuta. ABBAS / | Muktar. | Hashim | / Rumah Auwal Mask??? Shiru yai yana kallab takardar kafin yace " komai yayi connecting da Mumy, yayanta, mijinta nada, mijinta na yanzu." Itama da ita aka dau fansa saboda suna ganin Abba ne sanadiyar mutuwar mahaifinta?? Da sauri ya girgiza kai yace "

Table of Contents

Chapters

115 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115