Chapter 104
Chapter 104
dan murguda baki tace " nidai ban fadi suna ba." Kallanta ya tsaya yi, ta debi ruwa a hannunra ta watsa mai tace " yallabai kallan fa?" Dariya yai yace " fada kikeso?" Ta tsuke baki, shima hannu yasa duka biyu ya riga watsa mata ruwa, nan itama ta dage tana watsa mai, dariya sosai suke yi wanda kana ganinsu kasan suna cikin tsananin kaunar juna. Bayan sun gama wanka, ta jawo towel d'aya ta rufa sannan tace " na fita." Kallanta yai yace " nifa?" Tamai gwallo tace " ka dauka da kanka." Tai d'akinsa tare da zama kan gado tana dariya. Ashraf ya fito yana zuwa ya sa hannu a gugunta ya matse da karfi, wanda ya sa ta saku kara yace " ni kika ki daukoma towel?" Tana ihu da dariya tace " sry Yayana na tuba na daina." Yace " inaa baki dainaba sai na hukuntaki tukun na." Ganin yaki saketa yasa tace " Yaya Nisa?" D'agowa yai da sauri ta mike da gudu tana dariya. Murmushi yai sannan ya mike sambal akan gado tare da rufe idansa. Ahhh na kosa in gama wannan case din in ganni tare da matata kullum. Abinda yake fada kenan a ransa. *#ASHRAFEENAH TEAM* [8/28, 19:57] Umar Dalha: *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *Gareku yan gro din World of Hausa Novel, Mumbari M.Jabo, Maryam mai dala grp na gode kwarai da yanda kuke san littafin nan. ILYSM😍* *81* Washegari da safe bayan Kawu ya fita, Dan Litti yazo ya dauki Mumy da Nafi yai abuja dasu dan tacan zasu tashi gobe. Little kam taji takaici sai dai Nafi tace mata ai ita saboda makaranta, tunda su sai nan da 1mnt akace list dinsu ma zai fito. Ashraf sai dayaga tafiyarsu sannan ya kira Kb yace " a ina kace an samu Dan Siyasan?" Kb yace " yana nan asibitin Murtala ashe bashida lafiya ne shiyasa akaita nemansa aka rasa." Ashraf yai murmushi sannan yace " ganinan zuwa ka turon ward din da yake da number d'akinsa." Nan take Kb yamai Text Ashraf yaja mota yai gaba. Bayan ya isa asibitin ne ya tafi ward din masu cancer sannan ya duba number d'akin. Knocking yai nan akace ya shiga, a hankali ya tura kofar d'akin, wani ne a kwance jikin nan duk ya rame kamar me kanjamau sannan ga wani matashi a kusa dashi a zaune. Jiki a sanyaye Ashraf ya shiga tare da karasawa bakin gadon. Matashin wanda baifi shi ba yace " ban gane ba?" Ashraf yai murmushi sannan ya dauko complimentary card dinsa ya mika mai yace " sunana Ashraf." Kallansa yai, wanda hakan yasa Ashraf yace " ba Dan siyasan dayai House of rep bane da?" Matashin yace " shine." Ashraf ya kalli mara lafiyan yace " Alhaji Uba ka san Mansir?" Kallan Ashraf yai fuskarsa dauke da alamar tambaya, Ashraf yace, " Mansir kanin Abbas marigayi mai A&A Food. Ltd?" Haryanzu dai bai fahimta ba sai dai ya maimaita kalmar A&A?" Ashraf yace " eh wanda yake auren kanwar Hisham." Jin sunan Hisham yasa ya fara kokarin mekewa zaune, hakan yasa d'ansa ya taimakamai ya zauna, kallan Ashraf yai yace " ina Hisham? Ka taimaka ka kiramin shi." Ashraf yace " baya kasar ne yanzu haka ma shiya turoni nadubaka, baisan baka da lafiya ba." Hannun Ashraf ya kama guda d'aya wanda Ashraf ya dana start da d'ayan hannunsa a wayarsa dake aljihunsa. Mutumin yace " Yaro ka ba Hisham hakuri, a zahirin gaskiya nayi laifuka da dama a rayuwata ta duniyar nan, wasu na nemi yafiya wasu kuma banma san inda mutanen dana cuta suke ba, na hau mulki, dadinta yasa na manta da Allah na kwashi dukiyar jama'a sannan na cuci jama'a Hisham na d'aya daga cikin mutanen da bazan taba mantawa ba saboda nine sanadin talaucewarsa." Ashraf yai shiru tausayin mutumin ya kamashi, ita dama rayuwa haka ne, yau in kaine gove ba kai bane. Mutumin ya cigaba, ka san kanin mijin kanwarsa?" Ashraf ya ce "eh shine Mansir din ai.", Mutumin yai ajiyar zuciya yace " kacema Hisham wlh wannan mutumin shine ya sani komai, shawara yazomin da ita ta neman kudi, nikuma alokacin idona ya rufe, zuciyata ta zarme ina ganin zan samu kudi mai yawa da xai sa inyi campaign ba tare da matsala ba, shi yasa na dauki shawararsa, sai dai dalilina yasa aka kama dukiyarsu mai yawa har hakan yakai ga ajalin mahaifinsa, wanda tsoro yasa nakasa fadar abinda ya faru a lokacin, ina tsoron kar nima azal ta fadamin." Kuka ne yaci karfin mutumin ya shiga yin tari a hankali,yace " yanzu gashinan kowa ya gujeni, wannan yaron shi kadai ke taimaka ta, shi kuma ba jinina bane rikonsa nai, nawa 'yayan duk sun gudu sun barni." Idanun Ashraf ne ya ciciko, yasa stop sannan yace "amma wace irin cancer ce ke damunka?" Murmushin yake yai yace " blood, anyi maganin har an gaji shiyasa nace shima yaron nan ya barni kawai a gida in kwanana yazo in tafi." Ashraf ya kalli matashin, hawaye yaga yana gogewa, tausayi ya kara kamashi, ya kalleshi yace " ya sunanka?" "Abdulmalik." Ya fada Ashraf yace " wani aiki kake?" Yace " kasuwanci nake a kwari, inada karamin shago." Ashraf ya kara tausaya mai, yace " aure fa?" Yace " shekarar Alhaji 5 kenan ba lafiya ina ni ina tunanin aure?" Ashraf yai shiru kafin daga baya yace " ka zo ka sameni a address din dake jikin katin, inada sha'awar kasuwanci inyaso sai in bude ma babban shago sai ka dinga mana." Kallan mamaki Abdulmalik yama Ashraf, shikam Uba kuka kawai ya saka yana godiya kamar me, Ashraf yace ba komai, sannan ya ajiye musu kudi dubu 30 ya fita. Yana fita ya runtse ido cikin tsananin tausayi yace " Rayuwa kenan." ********** Kawu ne zaune kusa da Asim ya kalleshi yace " wlh kaji na rantsema yau itace rana ta karshe da zaka ganni anan, in har baka fadamin inda ka samu takardun nan ba." Asim jiki a sanyaye cikin tsoro yake kallan Mahaifinsa. Kawu yace " to shikenan, ka karashi rayuwarka anan ni dakai kuma......" Da sauri Asim yace " Sata nai a d'akin Ashraf." Idanu kawu ya zare cikin tsananin mamaki yace "mene?" Nan Asim ya bashi labarin abinda ya faru. Hannu kawu yasa cikin takaici ya wankama Asim wani wawan mari yace " bakada hankali ne? Me yasa ne nikam kwakwalwar kifi Allah ya d'orama? Kana tunanin Ashraf Shine zai ajiye takardunsa a fili? Yaron da nafi shekara 10 ina sawa a min bincike akan ma yawan dukiyar Abbas daya barmai amma sam hakab ya faskar saboda tsananin wayau da takatsantsan irin na yaron, shine kakeso kacemin ya ajiye takardu a d'akinsa?" Asim yai shiru, Kawu ya naushi iska cikin takaici yace " kana xaune sokon banza ya kamaka cikin ruwan sanyi, kai wannan yaro nikam bansan jakantarka ba." Waje yai da sauri cikin takaici, yana fitowa Anisa ta kirashi tace "Abba nikam Mumy tayi tafiya ne?" Cikin fada yace " kamar ya?" Tace " a'a naga bangarenta ansa kwado ne sannan su Afra sun koma bangaren Little shine dazu da Afra tazo tacemin ai Mumy tayi tafiya."
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115