Chapter 109
Chapter 109
sanda su nemeta. Bayan ta iso ogan cikinsu ya kalleta fuskarnan a hade rike da littafi yace "Ke kika turama Yayanki sako akan kina san ganinsa?" Cikin mamaki tace " a'a." Yace " ina wayarki?" Hankalinta a kwance ta mikamai, ya duba wayar babu sakon, ya kalleta yace " ki tuna sosai ina kika ajiye wayarki? Ko kuma wa kika ba?" Tace " ni ban ajiyeta a ko ina ba, mahaifina dai ya amsh wayar dazu." Kallan juna sukai, yace " mahaifin naki yana nan?" Tace " eh." Yace " kira mana shi." Nan ta tafi bangaren Abba. Yana zaune duk hankalinsa a tashe yaji kwankwasa kofa. Hankali a tashe ya bud'e kofar. Little ta kalleshi tace " Abba ana nemanka." Yace " su waye?" Tace " yan sanda ne, ni kaina bansan me ke faruwa ba." Cikin tashin hankali yace " me kika ce musu?" Tace " tambaya ta sukai a ina na ajiye wayata ko wa naba shine nace kai naba kawai." Hankali Kawu ya kara tashi cikin fada ya kalleta yace " bakida hankaline??me yasa zakice ni kika ba? Ko kema kin hada baki da yayanki ne???" Cikin mamaki tace " me ya faru?" Tureta yai ya wuce cikin takaici yana tunanin me zaice? In ya gudu kuma tabbas yasan zasuyi zargin wani abu. Fitowa yai ya isa gunsu, tare da mikamusu hannu alamar gaisawa. Bayan sun gaisa wannan officer din na dazu ya kalli Mansir yace " bincike mukazo yi." Mansir ya kalleshi, Officer yace " kaine ka amsh wayar 'yarka wato Maryam dazu?" Kawu ya danne tsoro yace " nine, amma menene dan uba ya amshi wayar 'yarsa?" Officer ya kuramai ido kafin yace " kaine ka turama Ashraf sako ta wayar?" Kawu yai alamar mamaki yace " ban gane in turama Ashraf sako ba? Akan me zanyi hakan?" Officer yace " zaka biyomin office da kai da 'yarka dan tsananta bincike." Kawu zai yi magana officer din yace " in har kana san kar a zargeka kenan, in kuma har da abinda kake b'oyewa to." Kawu yace " muje, bari na canza kaya." Nan ya koma bangarensa, ya canza kaya cikin tsananin firgice, tsoro ne fal a cikin zuciyarsa, nan suka taho da Little suka shiga mota suka bisu a baya. Ashraf kam ya ware sai dai yaki yarda a sallameshi, sun hada baki da likitan akan yace har yanzu bashida lafiya. Su Little zaune a station duk tayi tsuru tsuru, shikansa Officer din yasan ba ita bace dan dai ya zama dole ne ayi tambayar nan da ita. Wayarta ta karba ta kira Habib. Ta dade tana ringing kafin ya daga, tace " yaya kana ina?" Yace " ina gida ya akai?" Tace " dan Allah kazo ina police station tsoro nakeji." Mikewa yai daga kwanciyar da yake cikin rikecewa yace " ban gane ba me kikeyi acan?" Alama aka mata akan ta miko wayar hakan yasa tai saurin mai kwatance ta mika musu. Kan kace me sai ga habib ya danno mota a guje da gudu ya shigo cikin station din, sam bai kula da Kawu ba gunta ya nufa da saurinsa ya rike hannayenta yace " Little are u alright?" Kai ta girgiza mai hawaye suka zubo mata tace " yaya ka kira ya Ashraf kaji ko yana lafiya naji ance yana asibiti." Cikin mamaki yace " asibiti kuma?" Kai ta d'aga mai, zaiyi magana suka hada ido da Kawu, wani irin kalli yamai cikin takaici baisan sanda yace " ka gama lalata rayuwar wasu yanzu ta 'yarka kake san lalatawa?" Cikin mamaki Little ta kalleshi, kawu ma kallan mamaki yake mai. Habib ya dauke kai sannan ya matsa gun officer dan jin abinda ke faruwa. Sosai officer yamai bayani, ran Habib ya baci cikin fada yace " Ai ba sai kunyi wani bincike akan wannan baiwar Allahr ba tayayya ma yarinya karama zatai tunanin yin haka? Sannan yayanta ne fa ubansu d'aya banda yanda suke tsananin san juna, shi kuma waccan mahaifinta ne sai dai im shine." Little cikin mamaki ta kalli Habib tace " Yaya ya zaka ce Abba ne? Mai zaisa Abba ya cutar da Yaya?" Habib bai amsa mata ba ya kalli Officer. Kawu kam ya ma rasa mai zaice, aransa yace "like father like son dukansu sai zuciya basu iya controlling din fishinsu ba sam. Sai yamma wanda yaje bincike ya dawo dauke da doguwar takarda, duk abinda ya faru a wayarta ne da wanda aka kira da time din kiran da kuma texts. Kawu kam yana zaune ne kawai. Bayan an kawu ne aka ga tabbas an kira Ashraf bayan kuma texts da akamai. Mamaki ya kama Little duk da Yaya ne yace taba Abbanta wayarta inya tambayeta bata kawo komai a ranta ba. Officer ya kalli Little yace " me zaki iya cewa gameda sako da kuma waya da akai da layinki?" Abbanta ta kalla sannan ta daure tace " nidai wlh ban kira Yaya ba." Officer yace " mahaifinki fa?" Tace " shima nasan bai kira yaya ba, saboda me zaisa ya kira yaya a wayata bayan ga wayarsa? In ma ya kira wani to sai dai in Nafisa ya kira." Officer yai murmushi yace " hakane abinda kika fada me zaisa ya kira yayanki a wayarki bayan ga wayarsa? Wannan itace kalma ta farko da take bukatar bincike." Kawu kam gabansa sai faduwa kawai yakeyi. Officer yace " kuje gida zamuyi bincike zuwa gobe." Habib ya jata suka shiga motarsa sukai gaba. Kawu ya shiga tashi cikin tashin hankali. ************* Datti kam jiki ba dadi da kanshi yake bi gari gari kauye kauye kauye sai dai ba Nafi ba labarinta ba kuma Dan Litti. Hankalin Datti ya kara tashi nan ya fara zuwa gun malamai akan amai addu'a akan yarsa ta fito. Sai dai haryanzu ba labari, Datti duk ya canza magana ma ba damunsa tai ba, ba dukiya, ba 'yarsa dama wadancan sun gudu, duk ya zama abin tausayi. *#ASHRAFEENAH TEAM* *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *SECOND TO THE LAST PAGE* *ILYSM MY FANS* *86* Yau kwanan Ashraf uku a asibiti, 'yan sanda sune suke tsaron d'akinsa sai dai duk abinda ke faruwa Dan Litti na kawo mai rahoto, Little kam tayi kuka sosau ganin yayanta cikin wannan hali, haka ma Anisa, duk yanda taso akan ya barta ta zauna agunsa yaki sai ce mata yai ai Umma ma ba lafiya gareta ba kuma tana bukatar ta. Umma kam neman yanda zata fito da Asim kawai takeyi, sai dai duk inda taje ta nemi taimako akaji wannan uban kudin sai kaga kowa yana dauke kai. Yau da kanta ta shirya tazo gun Ashraf, bayan sun gaisa ta kalleshi tace " Ashraf in har nai abinda kace zakasa a saki d'ana?" Ashraf yace " zan biya kudin da ake binsa zai kuma yi bailing sa " Tace " naji yaushe kakeso in fada?" Murmushi ya mata yace " zan sanae dake lokacin." Cikin damuwa tace " Yaushe to zaka sa a fito da Asim din?" Yace " karki damu saboda ankusa a cikin satin nan ne insha Allah." Nan ta fito tai gida. Dady shima yazo, kuka sosai yai agaban Ashraf magana d'aya yake
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115