Chapter 90
Chapter 90
Kanaso kacemin Ashraf ne yace ma haka?" Da sauri Asim ya daga kai, Kawu ya hade rai yace " ba ka cikin hayyacinka da alama mafarki kai." Asim zai sake magana Kawu yace " mu fita ni." Haushi ya turnuke Asim yai waje a zuciye, har yayi nisa ya dawo gun Kawu yace " Abba me kake nufi dani?" Kawu ya kalleshi cikin mamaki ba tare da ya amsa ba, Asim ya cigaba " menene baka yarda dashi ba game da ni? Ni din ne baka yarda Ashraf yayi acknowledging din aiki na ba ko kuwa baka yarda da zan iya wani abun bane?" Kawu ya kalleshi cikin kulluwa da wannan halin nashi, yace " duka, u always disappoint me." Yana kai nan yai gaba yabar Asim a tsaye a gun. Asim yabi Kawu da kallo cikin tsananin takaici da haushin yanda Kawu yake mai. Kawu kam mota ya shiga cikin takaici. *********** Nafi kam bayan tayi wanka tana zaune a d'aki ita kadai duk abin duniya ya isheta ta kira Ferry a waya nan sukai ta hira har Ferry ta sanar da ita jarabawarsu ta fito. Nafi tace " haba?kin dubo?" Ferry tace " a'a amma ya Nabil yau zai dubo min." Naf tace " kice ya dubo da nawa " Ferry tace " to, amma Nafi karfa ki yaudaren kije ki cike wata makarantar ba BUK ba." Nafi tai dariya tace " karki damu duk inda kike nima ina nan, sai dai in samu ne banyi ba amma ina zani?" Sun dade suna hira kafin suyi sallama bayab sun gama tsara bikin Jibiya da za'a fara nan da 2wks, Nafi tace " Zata kawu mata kudin ankon inyaso sai a musu gaba d'aya komai iri d'aya." Tana kashe wayar tai shiru, a ranta tace " Ferry fa batasan ni matar aure bace fa ko? Ya kamata in sanar da ita kar taji daga baya ta d'auka ko yaudararta nai." ********** Ashraf na zaune a office ya dukufa sosai gun aiki yaji an banko mai kofa, Secretary dinsa yana biye da wanda ya bud'e kofar yana cewa " malan meye hakan?" Ashraf ya kalli Habib yama Secretary din alama da hannu akan yaje. Nan yai gaba, Ashraf ya kalli Habib yace " Habib lafiya naganka haka?" Habib cikin fada yace " Ashraf me ake nufi akan kai mijin Nafi ne?" Ashraf yamai kallan mamaki yace " ban gane ba?" Habib yace " baka gane ba kamar ya? Little tace kai mijin Nafisa ne, ni kuma banaj na taba jin wannan labarin." Ashraf ya koma ya zauna fuskarnan a hade yace " yanzu ai kaji." Habib ya matso cikin tsananin kishi ya kamo wuyan Ashraf yace " how can u do this to me? Kasan kuwa yada nake da burin auren yarinyar nan? Taya za'ai kac......." Ture hannunshi Ashraf yai da karfi yace " kai ko kunyata ma bakayi? Taya za'ayi kazo kanamin zancen wai so bayan kasan kanwata yanda take sanka?" Habib ya kalleshi, Ashraf yai wani murmushin yace " badai cemin zakai baka sani ba? Zan iya aminta inka fadi wani abu amma ba wannan kalmar ba." A hankali Habib yadanyi baya, Ashraf ya sake murmushi yace " mubar wannan maganar, ina Dady?" Jiki a sanyaye Habib yace " yana gida." Ashraf yace " Allah sarki Dady baka gani ya kamata a dan ko karamai girman asibitin nan ko kuma a bud'e mai wani babba?" Habib yai dariya yace " tab lalai, dady din?" Wani irin kallo kasa kasa Ashraf yamai, Habib yacigaba " kabar Dady kawai sani ne bayasan ayi amma yanada kudi sosai inaj fa yanada gidajen haya manya kusan guda goma." Ashraf yai murmushi yace " amma wannan ai mayb daga baya ya saisu." Habib ya girgiza kai yace " a'a wlh, ni fa rannan inajinsa da Mumy yana zancen da gidajen lokacin duniya na kwance basa kawo kudi sosai amma yanzu dayake komai ya tashi kudi suke kawowa sosai." Ashraf yai murmushi, kafin daga baya Habib ya tafi. Ashraf ya d'au waya da sauri ya kira Uncle bayan sun gaisa yace " Uncle nikam kasan komai ma dukiyar Abba kuwa?" yai maganar cikin bugar ciki. Uncle yai dariya yace " a iya sanina nasan komai nashi." Ashraf yai shiru jikinsa ya fara sanyi, can ya daure yace " kasan komai nashi tun kafin ya rasu?" Salim ya sake dariya yace " gaskiya nidai a iya sanina nasan komai." Ashraf yai shiru can yace " shikenan na gode." Yana kashe wayar ya mike tare da zuge glass din window yana kallan titi, a ransa addu'a kawai yake Allah yasa ba haka bane......" *#ASHRAFEENAH TEAM* 💞 *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *71* Nafi tana zaune a d'aki taji ana kwankwasa kofa, a hankali ta mike ta bud'e. Ganin Mumy ce yasa tad'anyi baya da sauri tare da cewa " Mumy sannu da zuwa." Mumy ta shigo ciki tare da zama akan d'aya daga cikin kujeru biyun dake d'akin, Nafi ta zauna daga d'an nesa da ita a kasa tare da gaisheta, Mumy ta amsa sannan ta kalli Nafi tace " Zaman kadaici baya damunki?" Nafi ta girgiza kai alamar a'a, Mumy ta dan yi shiru, kafin ta nisa tace " Nafisa!" Yanda ta kira sunan yasa Nafi ta d'ago a hankali tare da shan jinin jikinta, ta sani cewa zatai tabar gidan. Mumy tacigaba " Ashraf yaro ne wanda baisan farinciki ba, bai san soyayyar iyaye ba, bai kuma san soyayyar 'yan uwansa ba." Nafi tai kasa da kai idanunta suka dan ciciko, Mumy tad'an yi ajiyar zuciya kafin ta cigaba " na sani i am not a good mother to him, ban taba tambayarsa ko da damuwarsa bane bare har inkai ga bin bayansa ko nunamai kulawa." Nafi ta kalli Mumy cikin tsananin tausayin mijinta, Mumy ta d'anyi murmushin takaici, tace " duk kuma da wannan abun danake mai ya nunamin ke a matsayin matar da yakesan zama da ita sai dai shima hakan ban bi bayansa ba." Hawayen da ke kwance a idanta ne ya gangaro, tai saurin sa hannu ta goge su, Mumy ta cigaba "A nawa ganin Ashraf matar da yake bukata itace mai ilimi wacce tasan kanta wacce kuma zata kula dashi." Nafi ta goge hawayenta sannan ta kalli Mumy jin tayi shiru, tace " na fahimceki Mumy na kuma sani ba tun yanxu ba Yaya yafi karfina, sai dai ni na kasa fahimtar ki." Mumy ta kalleta, Nafi ta daure duk da tsoron da takeji tace " bakya gani Yaya na bukatar kulawarki? Ko baki nunamai ba a kalla kya sanar dashi dalilinki na kin nunamai soyayya." Mumy ta maida kwallar ta dake neman fitowa tace " me yasa kike tunanin akwai dalilina nayin hakan?" Nafi tai murmushi tace " Mumy ta yaya uwa zata haifi d'anta tace ba ta sansa? Ta yaya uwa tana ganin danta a cikin wani hali tace ba ta damu ba? Ta ya ya uwa zataki d'anta wanda yake maraya ne? Duk inda nakai ga tunanin zai iya yiwuwa sam zuciyata bata yarda da hakan, ni nasan akwai dalilinki nayin haka, sai dai a gun yaya shidai rashin so ne yasa kike mai haka." Nafi da sauri
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115