Chapter 27
Chapter 27
haka bane Ashraf. " Ya kalleta sannan yai wani murmushin takaici yace " Nafi zata tafi makarantar kwana a satin nan insha Allah. " Mumy bata d'auke ido a kanshi ba tace " amma naga kamar ba tada karatu? " Ya sake yin wani murmushin wanda itakam mumy sam batasan taga yayi saboda bata sani me yake nufi yace "eh hanya za'a mata ta shiga Js ko 3 ne inyaso sai a dinga mata lesson kuma a makarantar. " Mumy ta jinjina kai tace " hakan yayi sai dai baka ganin karatun zai mata wahala? " Ashraf ya d'an tab'e baki yace " wannan kuma ruwanta. " Mumy tace " shikenan in makarantar ta fito sai ka fadamin sai muje a mata shopping Allah ya baka lada ya kuma yi albarka. " A cikin ransa yace Ameen, ta mike tace " bari inje. " Bai amsa ba ko ince tasan ma bazai amsa ba, tana fita yabi bayanta da kallo sannan ya koma d'aki ya d'auko diary d'in mahaifin sa wanda wasiya ce kawai ya barmai. Shafin farko wanda a kullum sai ya karantashi yau ma shi ya karanta " _Ashraf kada ka kuskura kabar mutane susan abinda ke zuciyarka,_ _ka dinga kokarin b'oye bakin ciki ko farin cikin dake ranka, kar ka bari wani yasan sirrinka, wannan ita kadai ce hanyar da zaisa ka kare kanka...ko da kuwa 'yan uwanka ne na jini..._" Ashraf ya share zufar data keto mai duk da sanyin AC d'in da ke d'akin, Murmushi yai wanda kana ganin kasan na bakin ciki ne a fili yace " Dad zan iya jure hakan kuwa? I am really lonely." Ya kwantar da kansa kan gado, kafad'ar sa na masa zugi sai dai zugin dake zuciyarsa tafi karfin wannan....... ¤¤¤¤¤¤ Habib kam da kansa ya samu Abbansa ya mai bayani, Abban Habib na tsananin san Ashraf a lokacin ya kira wayar abokinsa ya sanar dashi, sunyi rashin sa'a matar tashi an mata transfer zuwa Rumfa Collage sai dai ya sanar dasu ai kanwarta ma principal ce ta FGC na kazaure, nan ya sanar musu in suna san can d'in to a yanzu zai kira kanwar matar tasa ya fada mata. Nan Habib ya ma Abba alama da a yadda, sunyi sallama akan zai kira anjima. Ba'a dade ba ya kira tare da sanar dasu ba matsala duk sanda suka shirya ko gobe ne su kaita. Nan Habib ya kira Ashraf yamai bayani. ¤¤¤¤¤ A b'angaren D'an litti kuwa yan sanda sun gaji da ajiyarsa gashi abin haushi bashida alamar sanar dasu Inda Ashraf yake, duk kuwa da dukan da sukamai, hakan yasa haushi ya kamasu suka cilloshi waje tare da kwace wukar dake jikinsa. D'an litti ya sha kuka wiwi gashi ko ficika bashida shi, ga wunya datake damunsa. Dakyar ya mike ya dingisa ya shiga gari, yayi sa'a ya sami wani mutum ya bashi naira d'ari. Nan ya gangara yasai wainar gero kan kace me ya cinye, ta gumi ya baza yace " Oh Ni D'an litti haka rayuwata ta koma? Daga boko sai a nemi halakani? Yanzu ni ina zan nufa in nemo Ashaf d'in? " Ya jingins kansa da bango zafin rana na damunsa. Nace wayyo🤦🏻 *THE INNOCENT TEAM* *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *Fatie Shafi'u ina tayaki murnar kammala Jarabawarki. May Almighty Allah help and protect u.... ILYSM* Washe gari da safe Habib yaje makarantar mahaifinsa yama Nafi takardun karya na primary da kuma Js 1 and 2, sai dai takardun sun nuna sam batada kokari. Nan ya taho da shi gidansu Ashraf. Yau gidan an tashi kowa zuciyarsa ba dadi musamman ma Umma da Aneesa, Little kam ta fita makaranta. Itakam Nafi tana kitchen ta zake sai aikin girki take, sunayi suna 'yar hirarsu da Goggo. Suna gamawa ta fito duk jikinta ya d'an baci Amra ce ta karaso gunta da gudu tace " Wai kizo inji yaya. " Nafi ta kalleta cikin zak'uwa tace " Ya Ashraf? " kai Amra ta d'aga mata ai kam Nafi da sauri ta nufi b'angarensa tana tafe tana gogee fuskarta da hannu, tun jiya takesan ganinshi sai dai ba yanda zatai. Fuskarta a sake ta kwankwasa kofar, ta saba in yana ciki sai dai yace ta shigo in dai har ba makulli yasa ba, sai dai yau gani tai anzo an bud'e da fara'arta ta kalli mai bud'ewa tace " Yaya ina kwa...... "kalamanta ne suka tsaya ganin Habib a tsaye yana mata murmushi. Jin ta tsaya da magana yad'an kanne ido cikin salonsa yace " Haba Nafi ba ni kika so gani bane? " Da sauri ta girgiza kai alamar a'a sannan ta d'ora da cewa " ba haka bane Ya Habib. " Habib ya d'an matso kad'an hakan yasa ta d'an kara matsawa, kara matsowa yai itama ta kara matsawa, sam bata kula tazo karshe ba tayi baya zata matsa kawai taji zata fad'i, da sauri yasa hannu a kugunta ya tarota. Nafi kam har ta runtse idanta kam, jin an riketa yasa ta bud'e ido a hankali, Habib ya sakar mata wani lalausan murmushi, sannan ya matso da fuskarsa yace " Me yasa kika tsaya da maganar ki to? " Yawu ta had'iya da karfi sannan ta d'an motsa baki tace " Ya Habib d'an sakeni. " Jin ta waske bata bashi amsa ba yasa ya d'agota tare da sake cewa " Shikenan na hakura da gaisu.... " Bata jira ya karasa ba tace ina kwana? " Dariya ya d'anyi sannan yace " Nafi kina burgeni na rasa me yasa. " Kasa tai da kai dan itakam tasan wasa ne ace tana burge wani. Ashraf dake zaune a kujera duk yana kallan me sukeyi kasancewar kofar a bud'e Habib ya bata yaja wani karamin tsaki tare da girgiza kai yace " in kun gama sai ku shigo, dan ni inada abinyi. " Nafi ta kalli inda Ashraf yake haka kawai taji gabanta ya fad'i tare da tsananin takaicin ganin ta dayai. Habib ya matso da niyyar rike mata hannu da sauri ta b'oye hannun a baya kallanta yai fuska a sake sannan ya d'anyi gaba yace " Ki shigo. " Da sauri ta shige jikinta duk yai sanyi. Ashraf na zaune yana kallo ta karasa tare da zama a kasa, Habib ya kalleta yace " zauna a kan kujera mana? " Ashraf ya bugamai wani mugun kallo yace " Mu sa'aninta ne? Kai meyasa kake kokarin zubar mana da mutunci agurin yara kanana? " Nafi wacce ko alamar tashi dama batai ba ta d'ago ta kalleshi sai dai zuciyarta ta d'anji ba dadi. Ashraf ya d'auke idansa, Habib ma kasa magana yai, Shiru ne ya d'an biyo baya kafin Ashraf yace " Nafisa! " Gaba d'aya tun daga kan yatsar kafarta har zuwa kanta sai dataji wani abu ya wuce mata, d'agowa tai a hankali ta kalleshi. Ashraf kam ko a jikinsa yace " yau zuwa gobe zakuje da Little da kuma mumy xakuje siyayyar kayan makarantarki. " Kallonsa tai cikin mamaki batasan sanda tace " naam? " Ya had'e fuska sosai yace " bakiji me nace ba? " Tace " Naji kace makaranta. " Yace " eh, in kun gama siyayya da komai zuwa jibi zaki
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115