Chapter 8
Chapter 8
hannunta. D'aki ta shiga ga mamakinta Datti ta gani zaune akan tabirma wanda rabon da ko dakinta ya leka yaga a wani hali take ciki ita kanta ta manta. Shiga tai kanta a kasa, ta gaidashi sannan ta zauna kusa da Maman Hanne. Datti ya kallesu yace " To aure dai an daura sai dai an samu canji daga Ali zuwa wani Ashaf." Cikin tsananin mamaki Nafi ta d'ago ta kalli Baffa tace " Ashaf?" Datti ya jinjina kai yace " Kwarai nikaina nafisanshi akan Ali da alama yana da arziki sannan kuma shi saurayi ne." Maman Hanne ta kalleshi tace " nifa sam ban fahimci me ake nufi ba, banga ne daga Ali ba an koma Ashaf? Meye ma wani Ashaf? Ni bantaba jin sunan ba." Datti ya buga mata wani kallo yace " meye naki a ciki? ' yata ce ba 'yar uban kowa ba sannan in baki tabajin suna Ashaf ba yau ai kinji." Ya mike rai a bace sannan yace " ke kuma ki shirya yanzun nan dan yace ba agarin nan yake ba zaku wuce yanzu." Kallan mamaki kawai take ma babanta ta sani shi dabobinshi su kadai ne abinda ke gabansa kuma suka dameshi sai dai bata taba tunanin zai ma 'yarsa ta cikinsa haka ba, sai kace wata kaza? Ganin kallan datake mai yasa yace " in tunanin sadakinki kikeyi kima manta dan nima na dauki rabona na satar da uwarki tamin, yana kainan yai waje. Nafi kam kuka ma kasa zuwa mata yai jitai idanunta sun kafe kaf, sai dai rigar dake hannunta kawai ta shiga ninkewa jitake zuciyarya kamar zata tsage, Maman Hanne ta kalleta tace " Nafi ki taimaka ki fadamin abinda ke faruwa dan Allah." Nafi ta kalleta tace " Auntu ko na fada miki menene amfani? Tunda aikin gama ya riga ya gama? " Hanne ta mike cikin takaici tai waje. Nafi kam a zaune kawai take tana jiyo muryar Datti yana cewa suyi sauri. Ashraf kam yana tsaye a waje tunani sun taru sun mai yawa, ina zai sa kansa? Mai zai cewa masoyiyarsa kuma 'yar uwarsa wacce saura wata biyu a daura musu aure? Yasan ta sarai yanda take tsananin so da kishinsa lalai zata iya yin komai inhar taji abinda ya faru, kansa ya dafa wanda yakeji yana sara mai. Karar mashin ne yasa ya kalli hanya, Su D'an litti ya hango nan suka karaso D'an litti ya kalleshi yace " yama kace name d'inka?" "ASHRAF. " D'an litti yai murmushi yace " Gaskiya an cucen da aka samin D'an litti sunan ka yafimin dadi." Ashraf yai musrmushi sannan yace " D'an litti kenan." Datti ne ya fito ya tsaya kusa da Ashraf yace " Ashaf gatannan amma ya za'ayi in anaso aje gunta ina zance? " Ashraf ya kalleshi sannan yace " Kano anan garin nake, sannan ai kasan sunana."yai maganar cikin bacin rai. D'an litti ya tafa mai yace " Haba? Living Kano? I also came to kano." Ashraf ya furzar da iskar takaici yace " nikam D'an litti kadingamin hausa banasan turancin nan." Dariya Datti yai yace " gaskiya kam, yanzu kenan in wasu zasuje sai D'an litti ka rakasu ko?" D'an litti yai murmushi tare da sosa keya. Nafice ta fito sanye da lulub'i Hanne da mamanta na gefenta, Hanne ce ta kalli mazan gun su uku, tace waye mijin a ciki? Ta fada tana fatan Allah yasa ba wannan bane dan ya birgeta Allah yasa D'an litti ne." Gani tai D'an litti ya nuna wanda yai masifar burgeta da yatsa, dukda rigar kauye ce a jikinsa kana ganinshi kasan daban yake, tadan yi yake tace " to a rike mana 'yar uwarmu dakyau, amma bamu zamu kaita ba?" . Datti yace " bakiji me nace ba aciki ko kuma wani sabon kinibibi ne hakan? Ai nace su biyu zasu tafi ko?" Mamaki ne ya kama maman Hanne tace " su biyu? Dama abinda kake nufi kenan? Taya zamu bari 'yar mu ta tafi daga ita sai shi? " Datti yace " karki damu D'an litti yasan gidan." Tai shiru, Nafi kam hawaye ne ya fara zubo mata itakam tana ganin rayuwa? Wasa wasa kaza ma ta fita matsayi itakam. Jitai ance " Ina rigata? Ko kin barmin wannan?" D'agowa tai cikin tsananin mamaki, idanunsu ne suka hadu........gabanta ne ya shiga fad'uwa sai dai ta kasa dauke ido daga kansa, ya sakar mata wani sansanyan murmushi........ *THE INNOCENT TEAM* *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *WELCOME BACK ZEE FRESH,* *WE REALLY MISS YOU*😍😘.. 7⃣ Kallansa take cikin tsananin mamaki ya sake murmushi yace " Riga tafa? Ko kin barmin wannan d'in? " Kasa tai da kanta sannan a hankali tace "na d'auka ka tafi ai. " Datti yace " me kuke nufi kenan ka santa dama? Sani bana taimako ba? " Ashraf yad'an yi murmushi dama so yake ya kular da Datti yace " sani kuwa tunda ji jiya a d'akin ta na kwana. " Yai maganar yana kallan Nafi, gaba d'aya kowa ya kalleshi, Datti ya rike haba yace " Kwana? " Ashraf yai wani murmushin rainin hankali sannan ya ya d'aga kai yace " Uhm hum" Hannee da mamanta suka kalli Nafi cikin mamaki, Dan litti shima mamaki ne taf a ransa lalai wannan gayen ashe dan duniya ne? Nafi ce tayi baya da sauri tai cikin gida, kallan kofar data shiga sukai suna tunanin me kuma zatai. Nafi kam tana shiga da sauri tai d'aki tana tafe tana murmushi takasa gane dalilin murmushin nata, rigarsa data ninke d'azu ta dauka abin haushi ba tada turare hakan yasa ta fito, suna tsaye sai gata ta dawo. Datti yai tsaye yace "Gungumar Munafuka ina kika je? " Rigarsa ta mikamai fuskarta a sake tace " danaji bakai min magana ba sai na d'auka tafiyarka kayi. " Ashraf ya amsa yace" ina kuwa zan tafi? Bayan nasan kina cikin wani hali? " Salati Datti yasa yace " yau na shiga uku lalai yarinyarnan ke ba karamar 'yar iska bace, a haka kowa ya ganki sai ya d'auka ke ta Allah ce ba'asan tsantsar munafircin ki yafi na shaid'an ba, yanzu dan iskanci da so kikai ki auri Ali bayan kin gama lalata da wannan? " Cikin mamakin kalamansa Nafi ta dago ta kalleshi, lalata? Me kenan? Maman Hanne ma tace " Gaskiya Nafi kin ban mamaki ban taba tunanin zaki aikata haka ba. " Itakam Hanne harara kawai take makama Nafi. Ashraf ne ya kallesu yace " Gaskiya bakuda adalci, wato kai kana mahaifinta sanda nace ta taimakeni baka shi mata albarka ba ka yabe ta ba, sai yanzu dana fad'i na kwana a d'akin ta kaf cikinku ba wanda yai tunanin lalai kila ba abin banza akai ba. " Ya d'an furzar da iska sannan ya matsa daga inda suke, ta baya ya zaga ya cire rigar jikin sa yasa tashi, tunda ya juyo ya fara tahowa kowa ya kuramai ido, lalai wannan gayen bana karya bane, tafiya yake cikin isa Nafi itama ba'a barta a baya ba gun kallansa, Hanne kam kishi duk ya isheta. Ashraf har ya karaso basu daina kallanshi ba, D'an litti ya dafa yace " Babban gaye me kake tunani ne?
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115