Skip to content

Chapter 107

Chapter 107

Zuciya Kowa Da Irin Tasa Book One Complete Hausa Novels 1,171 words 0 views Progress saved
Download Book

ba. Anisa ta rike hannunsa tace " yaya muje dan Allag ka duba Umma, itama tun dazu take nemanka." Bai musa ba nan suka nufi bangaren Umma. Tana kwance a d'aki tana ganin Ashraf ta shiga kokarin mekewa zaune. Ashraf ya kalleta sannan ya kalli Anisa yace "dan bamu guri ko?" Anisa ta juya ta fita. Umma ta karasa zama sannan ta kalli Ashraf tace " Ashraf ya maganar Asim?" Kallanta yai sannan yace " Asim? Ina zan sani in har ku iyayensa baku sani ba?" Mamaki ne ya kamata tace " Ashraf na rokeka dan Alla......." Ka tseta yai yace " duniyarnan al'amuranta na bani mamaki, har kasan zuciyarki daga ke har dan naki banaji akwai daidai da kwayar zarra da san 'yan uwantaka da kukemin, banda neman halakani da kukeyi, amma wai ko kunya ni kike cewa in taimaki danki?" Umma jikinta yai sanyi dana sani suka ziyarceta tace " Ashraf na sani sai dai......" Katseta ya sake yi yace " ni a wannan lokacin ba abinda zaki fada da zan aminta dashi, abu d'aya nazo fada miki yanzu, in har kinason danki ya fito, sannan kinasan farincikin 'yarki to inaso nima kimin abu d'aya." Da sauri tace " zan maka shi ko menene." Ya kalleta yace "inaso idan na nemi shedarki akan mutuwar mahaifina ki bada shaida yanda kika sani tsakaninki da Allah." Cikin tsoro ta kalleshi tace " Ashraf me kake fada haka?" Yace " wannan ba damuwa ta bace, iya abinda zance da ke kenan, in kuwa har kikaki bada shaida kamar yadda nace to ki jira abu biyu, na farko danki dolene ya ziyarci gidan yari, na biyu kuwa ki jira takardar mutuwar auren 'yarki kinsani sarai yanda Anisa take sona, na tabbata bazata taba yafe miki ba inhar taji kece sanadiyar mutuwar aurenta." Hankalin Umma ne yai mugun tashi,Ashraf yace " sai ki zab'a da mijin da bai taba sanki ba, bai kuma damu da ke ba da 'ya'yan da kika haifa kike sansu kamar ranku suma haka, sai ki duba kiga wanene zai fi miki amfani nan gaba." Yana kaiwa nan yai waje. Hawaye ne ya biyo kuncin Umma lalai yau tana ganin tashin hankali ina zata sa kanta da rayuwarta??????? ************ Dady zaune a d'aki kusa da matarsa cikin kunar rai yake sanar da ita komai, hankalinta yayi tsananin tashi da jin abinda ya faru sai dai abinda basu sani ba, Habib wanda ya taho d'akin, cak ya tsaya jin zancen da sukeyi. Hankalinsa yayi mugun tashi da jin abinda ya faru, muryar mahaifiyarsa yaji tace " Dadyn Habib yanzu ya zamuyi da hakkin maraya da kuma wanda ya rasu?" Dady cikin mamaki ya kalli matarsa yace " dama kin sani?" Kallansa tai cikin kulawa tace " najiku a ranar da abin ya faru da safe kuna zancen, wanda hakan yasa nai saurin kiran Ruma na sanar da ita sai dai bakin alkalami ya riga ya bushe dan alokacin Abbas ma yana cikin mota." Jikin Habib ne ya shiga rawa, muryar Dady yaji yana cewa " Na shiga uku, tunda nake a rayuwata ban taba tunanin zan hada kai in kashe wani ba sai gashi nayi akan mijin kanwata wlh kinji na rantse miki tun bayan faruwar wannan abun duk sanda na kwanta sai nayi mafarkin Abbas yana min murmushi wanda hakab ke kara karyamin zuciya sai dai san abin duniya yasa na kasa yin nadama sai ma tunanin yanda zan kara mallakar wata dukiyar tasa da nakeyi." Gaba d'aya jikin Habib ne ya shiga rawa, da kyar ya iya saukowa daga saman dakin, d'akinsa ya nufa ya zube a kasa sam kwakwalwarsa ta dauke ya rasa ma tunanin mai zai fara abu d'aya kawai yake mai yawo a zuciya mahaifinsa da mahaifin Little sune suka hadu suka kashe mahaifin Ashraf wannan wani irin mugun al'amari ne????? ************ Kawu ne a d'aki sai safa da marwa yakeyi dole yasan matakin dazai dauka akan wannan yaron, dan kuwa baiga mai rabashi da Ruma ba baiga kuma bai rabashi da dukiyarsa ba. Akwatinsa ya dauko na karkashin gado, sai dai ya zaro takardar wasikar da Abbas yamai yaga tagardar ba komai, hankalinsa ya tashi matuka ya fito daga d'akin ya nufi bangaren Umma. Anisa ce kadai zaune a falo, ya shigo kallansa tai tace "Abba kazo duba Umma ne?" Fuskarsa a hade yace " ke kika bud'emin akwatin kasan gado na?" Gabanta ne ya fadi cikin i-ina tace " ba ni bace." Tsawa ya daka mata yace " tun bayan shigarki d'akina ba wanda ya kuma shiga bazaki fadamin gaskiya ba." Shiru tai sai gabanta dake faduwa, jitai yace " Ashraf kika ba?" D'agowa tai ta kalleshi a tsorace tace " wlh ba ruwan yaya ni......" Lebensa ya ciza da karfi yai waje a zuciye. Bangaren Ashraf ya nufa wanda rabansa da bangaren har ya manta. Jin kwankwasa kofa yasa Ashraf ya mike dan dama yana zaune ne tun dazu yana neman wayar Nafi tunda yasa layin Mumy shi ya amsa da kansa to na Nafin kuma sam ya ki shiga. Yana bud'e kofa yaga kawu a tsaye. Ashraf cikin mamaki yace " lafiya?" Hannu kawu ya mikamai yace " bani wasikar daka dauka a d'akina." Ashraf ya mai kallan mamaki yace "wasika?" Kawu yace " wanda kasa Anisa tadaukoma." Ashraf yace " ohhh wannan? Nikaina bansan inda yake ba." Kawu yace " mene?" Ashraf yace " kunya kakeji kayi karya ka b'oye akan Mahaifiya yace karna auri 'yarka?ko kuwa kunyar mai illa dakai kakeyi?" Kawu ya juya bai kara magana ba cikin takaici lalai dole ya dau mataki akan yaron nan dan kuwa da alama ya gama sanin komai. *#ASHRAFEENAH TEAM* *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *84* Rayuwa tayima mutane 4 zafi, na farko Kawu wanda yake tunanin yanda zaiyi ya halaka Ashraf ba tare da sanin kowa ba. Na biyu Habib wanda kunnensa ya jiyomai tashin hankalin dayafi karfinsa. Na uku Umma wacce ta rasa ina zata sa kanta, 'ya'yanta zata ceta ko kuwa mijinta. Sai na karshe Hisham wanda nadamada danasani suka taru suka mai yawa. Yau kwanan su Nafi 4, da barin gari, jikinta dai haryanzu ba wani sauki sai dai ba kamar da ba, yanzu tana dan cin kayan itace (Fruit) Mumy kam ta kasa daurewa ranar suna zaune a d'aki ta kalleta tace " Nafisa anya ba ciki gareki ba? Nafi cikin tsananin mamaki ta kalli Mumy gabanta ya fadi. Mumy ta matso kusa da ita tace " bakida kowa a garin nan da ya wuce ni, shiyasa nima na cire kunyar surukantaka na tambayeki, Nafi a matsayin 'ya na daukeki ba sirika ba, nayi dana sani sosai na kin amincewa dake danai tun farko har nake nuna miki cewa mace mai ilimi itace ta dace da Ashraf." Kan Nafi na kasa ta kasa dagowa. Mumy ta dafata tace "muje asibiti." Da sauri Nafi tace " a'a Mumy." Dariya Mumy tai tace " me? Kunya kikeji?" Nafi tai kasa dakai. Haka Mumy ta matsa mata dole da yamma suka nufi asibiti. An mata gwaje gwaje nan aka tabbatar musu tana da ciki na sati bakwai, farin ciki agun Mumy baya misaltuwa, ta kalli Nafi cikin zumudi tace " kinsanar

Table of Contents

Chapters

115 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115