Chapter 51
Chapter 51
Mansir ni in na tashi da kai zanyi kishi?" Cikin rashin fahimta yace name fa? Ta d'an rangwab'a kai tace "yanda yayanka ke sanka mana, shifa babban burinshi shine yaga ya samu aiki ya fara kula da karatunka da kansa sannan yaga duk wani abu da kakeso a duniya ya maka shi." Mansir jikinsa ya d'anyi sanyi,Ruma kam zuciya d'aya ta cigaba da sanar dashi tsarindaya shirya na ganin ci gaban ka,sam baya tunanina da kansa." Mansir yai shiru, Ruma tace " ya akai bai fad'amin zaka zo ba??" Kallanta yai da sauri yace " shima baisan nazo nan ba" "Why?"ta fad'a cikin mamaki. Ya kara gyara murya yace "garin na shigo shine naga bari nazo mu gaisa, dan banaji zamu had'u da bikinku." Bata gamsu ba sai dai da alama bayasanya fad'i gaskiyar abinda ya kawoshi. Murmushi tai sannan ta mai alama da ta tauke bakinta tace " nima bazan fad'amai ba" Yai murmushi jiki a sanyaye ya mike zai tafi, ya kalleta yace "Me kikeso game da Yaya? Tai dariya sannan tace " Mutum ne mai mutunta na gaba dashi, yanada ilimi,ga addini, gashi bashida kyashi." Shiru yai, a zahiri gaskiya ta fad'a, yasan kuma yaya yafishi da komai,ya saki yake yace "Allah ya baku zaman lafiya." Da sauri tace "Amin." Ya fito jiki a sanyaye. yayan Ruma shine ya nemomusu gidan haya anan kano dan sam Abbas yaki yadda akan ya zauna a d'aya daga cikin gidan Mahaifinta ko na yayan nata. Ranar d'aurin aure da sassafe Mansir yabar garin maiduguri ya shiga motar Jigawa. Tunda Abbas ya tashi yaga ba d'an uwansa ya shiga wani yanayi nan ya bazana naimansa sai dai sam ba Labari, ga duk wayoyinsa a kashe. Har lokacin d'aurin aure Abbas bai dawo ba nan shima aka shiga naimansa a tasha aka ganshi duk ya rikice da naiman kaninsa,da kyar aka samu aka mai dashi aka shiryashi aka wuce dashi gun d'aurin aure. An d'aura aure sai dai ko jira baiyi ayi gaishe gaishe ba ya fita,wannan abu yaba iyayen Ruma haushi, a maiduguri aka d'aura auren gidan yayan babanta, dan dama mahaifinta ne kawai a kano da iyalansa. Mansir kam ya isa kila sai dai yayi dana sai,babu inda zai zauna kakaninsu sun rasu, mahaifiyarsa kuma tana aure a wani gidan tare da yaranta. Haka aka wuce da Abbas kano yana cikin tsananin tashin hankali, a ranar aka kai Ruma sai dai ganin halin da yake ciki yasa itama hankalinta ya tashi,Abbas ya sanar da ita akan gobe dole zaije Kila neman kaninsa, ba tantama ta amince. Abbas ya isa kila yaje gidan mahaifiyar Mansir nan aka kirashi, da kyar Abbas ya shawo kansa ya yarda suka taho, wannan ma sai da Mahaifiyarsa tasa baki,ganin in ya zauna a garin ma a ina zai zauna yasa ya amince suka koma,Abbas ya dage yanata tambayarsa akan menene matsalarsa sai dai Mansir yaki fad'amai, kano suka wuce,Abbas ya roki mahaifin Ruma akan subar Mansir ya zauna a b'angaren baki dake gidan,Abbas ya naimomai Buk. Haka rayuwa ta cigaba, sam Mansir baya sh ga harkar yayansa, har ya gama karatu shima yai aure, a lokacin Abbas ya kara samun matsayi saboda kwazonsa. Ruma har Mansir yai aure ko b'atan wata batai ba wannan abu na tsananin damunta, har matar Mansir ta haihu ta haifi namiji aka samai Asim, shekarar Asim 3 Allah ya ba Ruma ciki, farin ciki kamar suyi ka ka,a kuma wannan lokacin ne Abbas ya Fahimci ashe Mansir matarsa yakeso tun yana Js1, hakan ya faro ne sanda yaji Mansir suna hira da abokinshi wanda suke a maiduguri sai dai yana gama aji uku aka kaishi makarantar kwana, tundaga nan suka rabu sai yau suka had'u shine yake tsokanarsa ina Ruma kuwa? Dafatan ya aureta. Hankalin Abbas ya tashi ya tausayama kaninsa wanda yake gani kamar shine sanadiyar durkushewar farin cikin kanin nasa. Daga sanda Ruma ta haihu alheruruka sukai ta faruwa da Abbas, ansama d'anta suna Muhammad Ashraf. Dukiyar Abbas tayi yawa a lokacin da Ashraf yakai shekara 8 yanzu company ne nasa na kansa, sanda ya gina tafkekn gidan wanda zai ishesu rayuwa duk yawan 'yayan da zasu tara shi da kaninsa. Ashraf ya taso mai tsananin san mahaifinsa, sun shaku sosai, alokacin ne kuma Abbas yake yawan zancen had'in aure tsakanin Ashrafda Anisa wacce take shekara biyu." " Abbas ya sanar da Ruma akan lalai ko bayan ransa karta kuskura tabar gidan nan sanda ta taimakeshi ya cika alkawari na ganin gidan nan ya zauna lafiya." Mansir kam yana kishin yayansa ta harkar komai ganin duk abinda yakeso aduniya daga arziki, ilimi,mata da sauransu Allah yabad'aj uwansa ba shi ba." Little tai ajiyar zuciya tare da share kwallarta tace "a lokacin Yaya na shekara 9 ne Mahaifinsa ya rasu,hatsarin mota yai, sannan Mumy na gama Takaba aka d'aura mata aure da Mansir wanda kowa bai san dalilin amincewarta ba. Har Baban Yaya ya rasu bayan an kaishi asibiti zancenshi d'aya ne akan Mansir ya yafemai. Nafi ta share kwallarta cikin tausayi, chakwakiya kenan, ta fad'a a ranta.......... THE INNOCENT TEAM *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *42* Shiru sukai can Nafi tace " Little to ai shi Mahaifin Yaya bai sani ba na tabbata daya sani da bazai ci amanar kaninsa ba." Little ta kalli Nafi tace " A ido Abbana yana nuna komai ya wuce sai dai daga yanda al'amura suke tafiya a gidan nan banaji har a wannan lokacin da Mumy take matarsa ya yafema Abban Ashraf." Cikin mamaki Nafi tace " To ita Mumy me yasa ta aureshi daga gama takaba?" Little ta d'aga kafada tace " Allahu a'alam shiyasa sam haryanzu Yaya bai sako ba." Nafi tai shiru tana tunani, little tace " kuma kinsan ba wanda ya fad'ama yaya mumy ta auri Abba na? Shikuma a lokacin baiyi hankalin da zai kawo komai ba har sai sanda Mumy ta haifeni, lokacin shi kuma hankali ya fara zuwa mai." Nafi ta zaro ido cikin mamaki tace aikam ba'a kyauta ba, amma meyasa Mumy tai haka?" Little ta girgiza kai alamar bata sani ba." Nafi ta daure tace " To naji ana zancen wasiyya har ga matarsa?" Little ta share kwallarta tace " Feena akwai wani sirrin da Mahaifin Yaya ne kawai ya sani saboda ayanda tarihin yazo shekarar da zai rasu lokacin yaya bai dade da shiga shekara 9 ba Abbas ya canza, shiru zaka ganshi yayi shi kad'ai sannan a wannan lokacin yana yawan zama da lawyernsa wanda yake abokinsa, hatta aiki daina zuwa yai sai dai in Ashraf ya dawo ya sashi a gaba suyi ta hira, in baya nan kuma sai dai kaganshi da diary yana rubutu." Nafi tai shiru, can ta ce " me yake rubutawa?" Little tai d'an dariya kad'an sannan tace " Yaya ne kawai ya sani dan shi yakema rubutun, sai dai ganin yanda Yaya bai tab'a nunama kowa ba sirri ne babba a ciki." Nafi tai shiru mamaki duk ya kamata, a cikin ranta tace " ina mamakin abubuwa guda biyu zuwa uku, na farko me yasa Abbas ya barma Ashraf duk wata kadararsa bayan yana tsananin san kaninsa kamar ransa?q Sannan me nene dalilin yin wasiyyarsa ba rashin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115