Skip to content

Chapter 81

Chapter 81

Zuciya Kowa Da Irin Tasa Book One Complete Hausa Novels 1,168 words 0 views Progress saved
Download Book

nesa. Da gudunta ta karasa gunsa, Ashraf ya kalleta yace " Little!" Cikin haki tace " Yaya Mumy ce." Yace "Mumy?" Ta daga kai tace "Nafisa...." Ai bai jira ta gama ba yai bangarensu da saurinsa. Yana zuwa bakin kofar dayake a bud'e yake yaji Mumy na cewa " Me zaki iyama Ashraf da har kike tunanin zamq matarsa? Ban yarda da wannan auren ba dan haka dole ne gobe ki koma kauyenku." Nafi kam hawaye ne kawai ke zubo mata. Muryar Ashraf ce ta daki kunnuwansu yace " Inji wa kenan?" Mumy ta juyo har zuciyarta sai dataji dan tsoro sai dai ta dake tace " injini ni mahaifiyarka." Ashraf ya karaso ciki yace " Do you hate us that much? Ni da Mahaifina nake nufi?" Idanu Mumy ta zaro cikin mamaki tace " me kake fada haka?" Yai murmushi yace " me? Ba tsantsar tsana bace yasa kike bakin cikin ganin farinciki na? Na sanar dake matatace, na dauka uwa mai san danta zataso farin cikinsa." Ya girgiza kai cikin takaici yace " sai dai me? Ban taba gani kinso abinda nakeso ba tun da na mallaki hankali na, in har nace gabas nake san yi to burinki kice kekuma yamma kikeso nai." Cikin murya mai zafi ya karasa maganar da cewa " inkinsan da haka meyasa kika auri Abba har kika haifine??" Nafi da sauri ta taso tazo kusa dashi ta dan turashi baya, idanunta na zubar da hawaye tace " Yaya me kakeyi hakan?" Mumy kam gaba daya jikinta ya gama mutuwa kamar wacce aka kwarama ruwan sanyi, Nafi ta cigaba da turashi zuwa waje tanacewa " please Yaya ka bari, kar kai fada da Mumy saboda ni dan Allah." Ashraf ya rike hannunta idanunsa suka kada sukai jajawur kamar jan gauta, ya kalli Mumy yace " na tabbata sanda mahaifina ya rasu kina daya daga cikin masu farin cikin faruwar hakan." Nafi kai kawai take girgizawa tana kuka, Ashraf na gama fadar haka ya fara jan hannun Nafi, har sunje bakin kofa ya juyo yace " in har baso kike nabar gidan nan ba kar ki kara shiga harkar matata." Ya ja hannun Nafi sukai waje, zubewa Mumy tai a gun ta rike inda zuciyarta take jin tana mata zafi ta saki wani irin kuka mai kuna. Ashraf kam jan Nafi kawai yake sunje yin kwana sai ga Anisa ta sha gabansu, ya buga mata wani kalli dan yanda yakejin zuciyarsa tayi sa'a ka da bai mareta ba, itama harararsa tai tace "anji kunya wlh kwartanci da ranar Allah, to wlh baku isa ba naga uban da zai maye min gurbina." Ashraf ya kalleta cikin tsananin bacin rai yace " gurbin inaji nine nake rike da ragamarsa ko? To mai zai faru in na sallami mai gurbin?" Idanu Anisa ta zaro tace "mai kake nufi Yaya?" Yace " zaki matsa ko sai na fahimtar dake abinda nake nufi??" Da sauri ta matsa ya ja hannun Nafi sukai bangarensa, bai saketa ba sai da suka shiga d'akinsa ya kalleta cikin tausayi ya runtse idanunsa, ransa na kara soyuwa, baya ya juya mata yana wani hucci da sauri da sauri. Nafi da sauri ta matso ta rungumeshi ta baya, tasa kanta a bayansa tana kuka tace " Yaya please cool down, me yasa ranka zai baci akan abinda baikai ya kawo ba??" Idanu ya runtse yanajin wani abu na tasomai a ransa yace " ina zaki gane bayan wani bangaren na sanar dani harda Mumy a salwantar da mahaifina, tunda nasan abu ya hadasu da danginta." Nafi ta kara kankameshi ta baya tace " Yaya Mumy fa ba wai tsanar ka tai ba, ka taba ganin inda uwa taki danta? Ni inaji a jikina akwai dalilinta na yin haka." Idanu ya sake runtsewa, Nafi ta zagayo ta gabansa ta rungumeshi tace "please yaya kadaina fadamata magana mai zafi haka tun balle in akainane." Hannu yasa ya zareta daga jikinsa yace " Nafisa, kinsan ya nakeji a raina? A duk lokacin da matar nan tamin haka? Tun da nake da ita bata taba san abinda nakeso ba, bata taba yarda da abinda nace ba, bare in nemi kulawarta ko shawararta." Hawaye ne ya zubo mai, Nafi kam hawayenta sai tsananta gudu suke yi, da sauri Ashraf ya juya dan bayasan taga hawayensa. Kara rungumeshi tai tace " Yaya fitar da duk abinda ke ranka, inaji kamar abubuwan da kake hadiyewa sunyi yawa, shi hawaye rahama ne in kayishi yanasa bakin cikin mutum ya ragu, sannan maganar Mumy ni dai inaganin da wani abu." Ashraf ya hadiye hawayensa yabar idanunsa a runtse, Nafi ta dago a hankali ta danyi dage ta sumbaci bakinsa kadan, tace " i am here with u, ka daukeni a matsayin mutum mara ji mara magana, ka fadi duk abinda kake boyewa a ranka ko ka samu sauki cikin ranka, Yaya na kula bacci ma bakayi yanda ya kamata, kuma ni nasan duk saboda abubuwan da kake hadiyewa ne kai kadai." A hankali ya bud'e idanunsa ya jawota ya rungume tsam, yace " Nafisa I really Luv u." Dagowa tai cikin mamaki, ya kara kankameta yace " kece mace ta farko ko ince mutum na farko da nake jin tabbas wannan itace, itace wacce takesona tsakani da Allah, itace wacce ta yarda dani, itace wacce zuciyata ta aminta da ita, itace nakeji in har tana tare dani i can endure everything." Ya dan yi ajiyar zuciya yace " ban taba tunanin zan taba jin mutum haka a raina ba, ban tabaji na aminta da mutum haka ba, Nafisa please don't ever betray me" Wani hawayen dadi ne ya zubo mata kai kawau take girgizawa tace " How can I! How can I......." Sam ta kasa karasawa ya dago a hankali ya kai bakinsa cikin nata...... _Ni kaina idanuna yau sun ciciko, tabbas Ashraf yaga rayuwa ko ince yana gani, babu abu mafi soyuwar zuciya da kunci irin ka rasa wanda zaka aminta dashi, ka rasa wanda zakai shawara dashi, ka dinga ji kamar kowa na kusa dakai nemab ganin bayanka yakeyi_ Allah ya tsaremu daga sharrin mutum domin kuwa sharrinsa yafi na shedan. Ameen *#ASHRAFEENAH TEAM* 💞 *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *64* Kwance suke tare a kan gado tana makale a jikinsa sun shiga bargo, fitilar d'akin a kashe take sai ta gefen gado da take a kunne, sunyi shiru sunajin dumin junansu. Cikin sanyin murya Ashraf yace " Nafisa." Tana kan kafadarsa tace " Naam." Yacigaba " Abba hatsarin dayai a kwai hadin baki a ciki." Da sauri tai nufin mikewa yasa hannu ya maidata yanda take, shiru tai sai dai gabanta sai faduwa yakeyi, yacigaba " bansan takamaimai dalilin dayasa Abba ya tsole musu ido ba ko ince suka tsaneshi ba sai dai gobe nake sa ran tambayar Uncle Salim in har shima bai sani ba sai inyi bincike da kaina." Nafi tai shiru, Ashraf ya cigaba " tun dana mallaki hankalin kaina nakejin komai ba daidai ba a gidan nan, sam na kasa yarda da yanda al'amuran gidan nan ke tafiya." Nafi ta makalo hannunta ta kwibinsa a hankali itama tace " Yaya ni kaina bayan Little taban tarihin gidan nan na rasa

Table of Contents

Chapters

115 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115