Skip to content

Chapter 50

Chapter 50

Zuciya Kowa Da Irin Tasa Book One Complete Hausa Novels 1,177 words 0 views Progress saved
Download Book

Ranar yazo fita ta d'au mayafinta tace " zata rakashi. " Ba musu suka fita tare, wannan fitar itace mafarin soyayya mai karfi data kullu a tsakaninsu, iyayenta sunyi takaici sun kuma so hanata wannan auren ganin ba komai Sale ke da shi ba. Fanna ta dage wanda hakan ya kaisu ga aure. Nan aka gyara mata b'angare anan cikin gida aka mata jere. Shekararsu d'aya da aure Allah ya azurtata da d'a namiji sai dai tana haifarsa Allah ya karb'i ranta. Aka sama yaron Abbas, Sale yayi kuka sam rayuwarsa ta canza kullum yana tare da d'ansa ko gona zaiji haka yake d'aukansa sutafi. Gulmar da ake a kauyen ne yasa mahaifin sa ya d'aura mai aure da Ruma 'yar gidan babban wansu. Ruma na san Sale sosai sai dai shi d'ansa ne kawai a ransa, wanda hakan ne yasa Ruma ta d'au soyayya itama tasama Abbas. Ganin yanda takesan d'ansa ne yasa shima ya fara kulata har Allah ya bata ciki ta haifi namiji itama shine aka samai Mansir. Sun taso cikin kulawar iyaye sai dai kowa yasan sanda Sale yakema Abbas wanda sam baya iya b'oye hakan koda kuwa a gaban waye. Abbas na shekara 8, shikuma Mansir na shekara 5 Allah yama Sale rasuwa. Wannan mutuwa ta girgiza kowa, iyayen Fanna sukazo akan a basu Abbas ya zauna a gunsu. Sai dai Abbas ya tubure akan baza'a rabashi da kaninsa ba, hakanan dole suka had'a da Mansir suka taho maiduguru. A can kuwa kowa yafi nuna kulawa da damuwarsa akan Abbas, dan yana isa garin aka sashi a makaranta, Abbas na kokarin ganin duk abinda aka mai an ma Mansir sai dai duk yanda yaso abu ya faskara. Makarantar kud'i aka sashi aka sa Mansir ta government, sannan kafin asai ma mansir kaya d'aya to Abbas ya tara 5 dan 'yan uwa ma na aikomai, wani sa'in haka zai dau saban kayansa yaba kaninsa. Haka suka taso cikin wannan rayuwa, Mansir yana tsananin kishin kauna da Abbas yake samu ta ko ina, a haka har Abbas ya gams karatunsa ya tafi Buk a kano. Mansir kuma yana aji biyar. Mansir tun yana Js1 ya fara san wata yarinya wacce akama mahaifinta transfer daga kano zuwa maiduguri. Yana tsananin santa sai dai ganin yarinyar bata Shiga harkar kowa yasa ya kasa sanar mata, har shima ya gama secondary ya fara poly dake nan garin Maiduguri. A kullum ya taso daga makaranta sai ya biya ta islamiyar su yarinyar wato Ruma, haka zai tabin bayanta har sai sunje gida ba tare da saninta ba. Kwatsam wani hutu Abbas yazo gida lokacin yana level 4 yaga Ruma, ba tare da gazawa ba yaje gidansu ya sanar da ita soyayarsa, cikin sa'a ta amsa masa, bai sanar da kowa ba saboda Ruma tace bataso a sani saboda mahaifinta yace karatu kawai yakeso. Soyayya mai zafin gaske ce ta shiga tsakanin masoyan biyu, a lokacin da Abbas ya sanar da Mansir akwai wacce yake so shima Mansir din yacemai akwai wacce yakeso sai dai shi kunyar sanar da ita yake. Abbas yai dariya sannan yace " Kanina ai yanzu da zafi zafi ake bugan kirji karka kuskura ka jinkirta soyayyarks kar a maka shigo shigo.... " Wannan kalamai na yayansa sun karfafamai gwiwa bayan Abbas yabar gida Mansir ya bugi kirji yaje gidan su Ruma. Sun gaisa kafin cikin fara'a zai fara koro mata abinda ke ransa ta katseshi da cewa " Mansir ko? Kanin Abbas. " Mansir ya washa baki yace " Eh nine. Ruma ta d'anyi kasa dakai sannan tace "Ai koka yai? " Cikin mamaki Mansir yace "a'a. " Ta d'ago sannan tace " ba wani nan, yace bazai fad'ama kowa muna soyayya ba amma wai bazai min alkawarin kin fadama ba. " Gaba Mansir ne ya fad'i yace " Kinsan yaya ai. " Tai murmushi tace " Yana sanka dayawa komai sai ya ambaceka. " Mansir kam jiyai kafafuwansa suna neman Kasa d'aukansa hakan yasa yace mata kansa na ciwo ya tafi. Mansir ya rame, sam karatun ma ya kasayi, a lokacin ne Abbas ya gama nashi karatun, yama Mansir fada sosai ganin takardunsa ba abin arziki, duk yanda yai akan ya sanar dashi matsalarsa ya ki. Hakan yasa ya zauna da kansa yake koyamai karatu. Sai dai abin mamaki ya kula yanzu sam Mansir baya yarda suyi wata magana mai tsawo. Hankalin Abbas ya tashi, yana tsakiyar wannan kangi mahaifin Ruma aka maidashi kano, sannan mahaifinta yace ta fito da miji. Ruma kam kai tsaye ta gabatar da Abbas, nan aka kai kud'i tare da sa rana." Little tai ajiyar zuciya tare da kallan Nafi wacce tai shiru tana sauraranta, tace " Kinsan su waye mutanen nan uku? Nafi tace " Abbas mahaifin Yaya, Mansir kuma Abban ki ko? " Little ta d'aga kai sannan tace " Ruma fa? " Idanu Nafi ta zaro cikin shakkun abinda yazo ranta tace " Don't tell me???" Kai Little ta d'aga tace " Yes! Mumy ce. " Nafi ta zaro ido sosai cikin mamaki, Little tai yake sannan tace " wannan shine mafarin komai dake faruwa. " Nafi kam baki ta saki tana mamaki wannan sarkakiyar..... Little ta nisa sannan ta cigaba.............. *THE INNOCENT TEAM* ZUCIYA Kowa da irin tasa .. *AYUSHE MUHD* *HASKE WRITERS ASSOCIATION* 41 " Mansir ya shiga wani yanayi ganin anata shirye shiryen auren yayansa da budurwar da yake masifar so, sam ya daina zama a gida wanda hakan ya tada hankalin yayansa. Abbas duk abin duniya ya dameshi ganin kaninsa a wannan hali, ana saura wata d'aya biki Mahaifin Ruma ya nemarma Abbas aiki a wani company na AL-Food.ltd, dan takardun Abbas sunyi kyau sosai. Company ne babba wanda ake ji dashi bama garin kad'ai ba har kasa baki d'aya. Kowa yayi murna sosai da wannan al'amari sai dai wanda ake dominsa sam baya farin ciki, an tsaida bayan aure da sati uku zai fara zuwa aiki a nan garin kano. Saura sati biyu biki Mansir ya shirya bada sanin kowa ba ya tafi kano,address din Ruma daya amsa agun wata kawarta yabi yaje gidan. Ruma kam alokacin ta dawo kenan daga amso dinkunanta na biki ta ganshi tsaye a bakin gate. Fara'arta ce ta karo ta karaso inda yake tace" Mansir yau kaine a garin namu?" Idanu ya kura mata gani yai ta kara wani kyau jiyai santa na kara ratsashi, ita ta katseshi da cewa "Mu shiga ciki mana." Kai ya girgiza alamar a'a, tad'an had'e rai tace "na d'auka mun zama d'aya?" Sun shiga ya fara kallan tangamemen gidansu, lalai yaya ya cuceshi ya kwacemai Ruma sannan an bashi aiki ga iyayenta masu kud'i sosai?auren da yake fata kenan. Falon baki ta kaishi sannan ta shiga gida ta had'omai abinci da drinks. Fita tai ta barshi yaci abinci kafin nan ta koma,suka sake gaisawa sannan tace" D'an lelen Abbas ya akai?" Mansir yasadda kai kasa tare da d'agowa a marairaice yace "Ruma!" Yanda ya kira sunanta yasa jikinta yai sanyi cikin tsoro tace " Badai wani abun ne ya samu Abbas ba?" Kai Mansir ya jijiga alamar a'a tai ajiyar zuciya sannan tace" Kaine ka tsorata ni Mansir." Ya d'anyi yake sannan yace" Wata magana......" Katseshi ta sakeyi da cewa" kasan

Table of Contents

Chapters

115 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115