Chapter 48
Chapter 48
Ashraf ya kalli Aneesa cikin takaici yace " ke bakiji kunya ba??yarinya karama ita take nusar dake nan d'akin aurenki ne ba wai na wani ba? Akan me zatama gyara miki gun da yazamar miki dolenki?" Aneesa wacce idanunta suka ciciko tace " Yaya nikam inaji a jikina kamar ba auren soyayya mukai ba, kamar ni kad'ai ce nake sanka kai kuma sanda kakemin kawai na 'yan uwan taka ne." Idanu ya runtse sannan ya kalleta yace " a soyayyar danasan ina miki da, banaji yanzu ina miki ko rabinta sannan bana tsamannin zaki tambayeni dalili ganin ke kikafi kowa sannin abinda ya jawo hakan." Yana kai nan ya zari makullin mota yai waje. Aneesa ta fashe da wani irin kuka na bakin ciki itama ta fito tai b'angaren Ummanta tana kuka wiwi kamar wacce akama duka. ************* A b'angaren Asim kuwa yana ganin su Ashraf sun tafi yai b'angaren mahaifinsa cikin tsananin tsoro da firgicin kalaman Ashraf. Yana isa ya kwankwasa tare da murd'a kofar ba tare da ya jira an bashi izini ba. Kawu wanda ke zaune gaban wani karamin akwati (kit) yana duba wasu takardu yanajin motsin mutum yai saurin rufe takardun tare da maidashi cikin kit d'in, yana kokarin tura kit d'in karkashin gado Asim ya fad'o d'akin tare da kallan mahaifin nasa. Shikam Kawu da sauri ya karasa turawa sannan ya had'e rai tare da cewa " Kai Asim bakada hankali ne zaka fad'omin d'aki ba sallama?" Asim ya karaso kusa da mahaifinsa tare da tsugunawa a gabansa yace " Abba ya zanyi?" Cikin mamaki yake kallansa yace " Da me fa?" Asim ya share zufa nan ya sanar dashi duk abinda ya faru sai dai ba fad'amai da sanin Umma a harkar ba. Kawu ya kalleshi cikin b'acin rai sannan yasa kafa iya karfinsa ya ture Asim, ya cigaba da magana cikin fad'a, Asim me yasa ne sam bakada hakuri? Banine nace kabar komai a hannuna ba?" Asim ya rusunnar dakai yace " Abba kayi hakuri wlh ni sam banasan ganin yaron ne." Tsaki kawu yaja sannan yace " zancen banza ma kakeyi, yanzu idan wad'anda ka tura sun kama Ashraf kenan 'yan sanda suka zo fa?" Kana tunanin bazasu sanar dasu kaika aikosu ba? Daganan sai me? Kamaka zasuyi a banza." Asim yai kasa dakai cikin dana sanin gaggawar daya aikata, kawu yacigaba " ni nace kabar komai a guna, akan me zamu halakar dashi bayan bamu gama sannin iya dukiyar dake karkashin sa ba?" Asim ya jinjina ma mahaifinsa kai sannan ya bashi hakuri, nan kawu ya sallameshi tare da zama akan gadonsa yai shiru yana tunani, can cikin wata irin murya yace. " Yaya ya zakayi??? D'an da kakeji duk duniya baya shi gashi a tafin hanuna, ya auri 'yata sannan matar fa kake santa kamar ranka ta dawo karkashina." Wata irin dariya ya saki wanda ni kaina saida tsoro ya kamani, da sauri nabar d'akin ina mamakin dama haka mutumin nan yake??? Lalai wata zuciyar akwai hassada da mugunta a cikinta. Asim na fita yai murmushin farin ciki tare da kara kallan kofar d'akin yace " Kai!!!! Amma Abba karshen mugu ne." Ya sa dariya sannan yace " ko menene a akwatin nan???" Kad'a kai yai ya nufi b'an garen Umma, ya shiga kenan ya zauna yana jiran ta fito daga b'andaki sai ga Aneesa ta shigo da kuka. Cikin kulawa ya mike ya rungumota yana tambayarta menene? Aneesa kam kuka take sosai, nan Umma ta fito ta samesu a haka. Itama zama tai suka cigaba da tambayar Aneesa abinda ya sata kuka, Aneesa cikin kuka tace " Umma Ba Ashraf bane ya fifita yarinyar nan a kaina." Cikin rashin fahimta Umma tace " Ban gane ba?" Asim yace " Malama dalla daina mana kuka ki fad'a mana menene ke faruwa." Hawayenta ta share ta shiga sanar da su duk abinda ya faru tun daga farko har karshe." Umma ta mike cikin fad'a tace " Lalai za'ayi tashin hankali a gidan nan." Asim ya mike tare da cewa " akwai meeting dole ne yau ayi taron gaggawa na gida dan kuwa Ashraf yayi kadan ya wulakanta mana ke." A zuciye yai waje...... ***************** Nafi kam tana fita daga b'angaren Ashraf ta nufi nasu b'angaren taje shiga taji ance " Yaya Feena." Juyowa tai tare da kirkiro fara'a tace " My Amrah kece da kanki?" Amrah tai murmushi tace " yaushe kuka dawo?" Nafi tad'an jujuya kai sannan tace " ni kadai na dawo." Amrah tad'an yi hucci kad'an kamar babba, Nafi tai dariya tace " Yaya Amrah ya akai ne?" Tace " Mumy ce tace " in mun dawo daga makaranta muzo gun yaya Little ta mana wanka sannan ta d'auko mana kaya." Nafi ta d'an canza fuska kad'an tace "Amrah naji haushi fa! Wato ni bazan iya muku abinda Little zata muku ba ko me?" Amrah ta matso kusa da ita tace " Yahkuri Yaya Feenah wlh ba haka nake nufi ba." Nafi ta kama hannunta sannan tace " naji muje mu taho da Afrah." Nan suka fara tafiya hannayensu rike da juna. *************** A can kauye kuwa Datti yana cikin tsananin farin ciki da walwala, a 'yan shekarun nan dabobbinsa sun kara bunkasa sosai yazamo kaf kauyen garin ba wanda ya kaishi yawan dabobbi, shi kadai yake rayuwarsa cikin farin ciki ba wanda zai kashema kud'i bare har arzikinsa ya ragu. Sam bai damu da halin da Nafi take ciki ba bare kuma matarsa da d'ansa da suka gudu. Duk sanda aka tambayeshi gidan Nafi sai yace sai dai a tambayi Dan Litti dan kuwa shi bazai iya gane wa ba, hakan yasa duk 'yan garin sun d'auka da gaske yaje gidan 'yar tasa. Sanda Dan Litti yai wata 5 a garin kachako yad'an tara kud'insa ya shiga garin kano neman Ashaf sai dai duk yanda ya nemesu ya kasa samunsu kasancewar garin da girma sannan baisan wani kwatance ba sai Ashaf mijin Nafi, wannan yasa duk inda ya tambaya sai dai amai dariya gani suke kamar shirme yake ko kansa ne ya tab'u. Bayan kud'in hannunsa sun karene ya koma garin kachako ya cigaba da achabar sa har ya d'an samu wasu kud'i, ya sanar da uban gidansa akan zaije kauyensu ya dawo. Mamaki ne ya kamashi ganin kowa ya ganshi sai ya tambayeshi wai 'yar gidab Datti a wani irin gida akai kaita? Wasu ma cewa suke zasuzo ya kaisu. Datti yanajin labarin D'an litti ya dawo ya taho takanas ya tareshi suka keb'e, Datti ya kalleshi yace " ya kaje gidan?" Dan Litti ya girgiza kai alamar a'a, Datti yace " ka taimaken duk wanda ya tambayeka gidan Nafi kace musu munje ka taimaka min." Mamaki ya kama d'an Litti yace " What u say?" Datti yai tsaki yace " malam ni banasan wannan yaren arnan naka kamin hausa." D'an Litti yai saurin rufe baki dan yace ya daina turancin shima. Nan Datti ya lalaba Dan Litti akan yai karya wai sunje gidan Nafi. Shikam d'an litti ko sati baiyi ba ya koma garin kachako ya cigaba da kasuwancinsa, ganin yayi abokai acan ga uban gidansa na sansa sannan can yafi kawo masa kud'i. Wannan Kenan.... To be continue ...... *THE INNOCENT TEAM* ( _Dan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115