Skip to content

Chapter 82

Chapter 82

Zuciya Kowa Da Irin Tasa Book One Complete Hausa Novels 1,168 words 0 views Progress saved
Download Book

dalilin dayasa na kasa fahimtar abubuwa guda uku." Ashraf yace " me da me kenan?" Ta gyara kwanciyarta tace " Mumy inaji a jikina akwai dalilinta na auren kawu cikin gaggawa." Ashraf yai dan karamin tsaki yace "ba wani dalili dama kila can shi takeso ta yaudari Abba." Nafi ta girgiza kai tace " karka bari zuciyarka ta nemi boyema gaskiya." Kai ya dan kawar gefe sannan yace " next." Tace " Meyasa kafin Abba ya rasu yafi zama dakai, naji hatta aiki ba fita yake ba kullum kuna tare dashi, nasan zai iya yiwuwa jikinsa ne yake bashi hakan sai dai yanda baya zama da kowa sai kai yasa nake tunanin da wani abu, ko yasan akwai manakisar da akemai ko kuma akwai wani dalili da mu bamu sani ba." Shiru Ashraf yai yana tunani, Nafi tacigaba " nakarshe karkace kishi ne ko wani abun sai dai inaganin tayaya Abba dayakesan ka auri yaya nisa zai bada wasiyya akan aba matarka ta farko? Indai har yaya nisa yake so ta zama matarka banaji sai yace matarka ta farko sai dai kawai ya bada yace abawa Yaya nisa in aurenku ya tashi." Shiru Ashraf yai yana tunani lalai wannan abun tambaya ne, Nafi tace " nayi mamaki danaji wasiyyar ta kudi ce ganin ba kudi kuka rasa ba,banaji akwai dalilin dazai sa Abba ya bada wasiyyar kudi." Ashraf yai shiru yana tunani, Nafi ta matso da kanta tace " yaya karka damu da abubuwan danace, zargi nane kawai ba wani abu serious ba." tafada tare da kara shiga jikinsa. Ashraf yai shiru yana tunani, ganin haka yasa Nafi tai bacci, sai daya tabbatar tayi bacci sannan ya jawo littafinsa ya zare jikinsa a hankali ya nufi falo. Can tsakiya ya bud'e inda yaga Abba yasa " Baban burina bai wuce naga na hada zuri'a da Muktar ba." Shiru Ashraf yai ya dade kafin ya dawo ya kwanta. Da sassafe kuwa bayan sunyi sallah sun kwanta sai daya jira tai bacci sannan ya zare jikinsa yai waje. Mota ya fada yai waje. Gidan Uncle ya nufa kafin ya karasa ya kirashi a waya yace " dan Allah ya fito waje zasuyi magana ne." Yana zuwa kofar gidan kuwa yaga Uncle a tsaye. Ashraf ya karasa suka gaisa sannan yace " Uncle zaka iya tuna me ya faru tsakanin Abba da dangin Mumy kafin ya rasu." Uncle ya kalleshi yace " Ashraf a ina....." Hannu ya hade gu daya alamar toko yace " dan Allah kafadamin Uncle, nasan ba yanda za'ai case ya hada su da Abba ace lawyer dinsa baisan komai ba." Uncle yai ajiyar zuciya yace " mu shiga motarka." Nan suka shiga, Uncle ya kalleshi yace " Ashraf mai nene dalilinka nasan jin abinda ya riga ya wuce?" Ashraf ya kalli Salim cikin zakuwa yaji yace " ba komai kawai so nake naji ne." Salim ya jinjina kai sannan yace " Mahaifin Ruma ya fara kasuwanci bayan yayi retire, ko da yake ba wai fara wa yai ba dan dama Hashim(mahaifin Habib) dan kasuwa ne, kasuwancinsu ya bunkasa alokacin da Abbas arzikinsa da matsayinsa yai fice a garin nan. Bazan manta ba bayan ka gama nursery ka shiga primary 1 wannan mumunan al'amari ya faru. Hisham da mahaifinsa sukayo dealer din kaya mai uban yawa wanda ya kunshi kusan duk arzikinsu, sai dai kaya aka hanasu shigowa, Customs suka rike musu kaya gaba daya container's dinsu. Ba karamin tashin hankalu suka shiga ba duk yanda sukai a barmusu kayansu su wuce amma ina... Sam abu yaki yiwuwa." Ashraf ya kalli Salim cikin mamaki yace " sunyo order din abu mara kyau ne?" Ajiyar zuciya Salim yai yace " Kwarai kuwa sai dai sun b'oye hakan, ganin ba yanda za'ai kayan su ya fito ga dukiyarsu duk tana ciki yasa mahaifin Ruma ya yanke jiki ya fad'i, tashin hankali ya kara tsananta. A wannan lokacin nan Hashim ya samu Abbas yace ya taimaka suyi cuwa cuwa a sakar musu kayansu, Abbas mutum ne mai tsaurin gaske jin Hashim ya zo mai da wannan uzuri yasa ya mai duban kurila yace " Hashim mai kuka sako a cikin kayanku?" Ran Hashim ya baci yace " ko ma me muka sako ai ya zamarma dole ka taimakemu ganin mune muka samar ma aiki har kakai matsayin da kake yanzu." Abbas yace " bai zamar min dole ba dan kuwa in har abinda kuka d'auko akwai abin cutarwa to wlh ko d'ana Ashraf ne bazan taimaka mai ba." Nan dai suka rabu zuciya ba dadi, bayan Abbas yayi bincike nan ne ya gano mugayen abubuwan dake kasan kayayyakinsu, ciki kuwa har da hodar iblis da 'yan kanananan makamai." Ba karamin tsorata Abbas yai ba ya samu Hashim cikin tsananin fushi yace " Hashim da hankalinka zaka saro wannan mugayen abubuwan?" Hashin cikin zafin rai yace " ce maka akai nawa ne? Na wani abokin Abba ne dan majalisa ne yace mu taho mai da sakonsa." Ran Abbas ya sake b'aci yace " to meyasa shi baiyi magana an sakar muku kayan ba?" Hashim ya dan shafi kansa yace " tun bayan faruwar abin nan yabar kasar ma gaba daya, ba yanda zamuyi mu sameshi." Abbas yace " kanaso kacemin kaf mugayen abubuwan nan ba naka ko na Abba ko daya a ciki?" Hashim cikin hasala yace " akwai mana, bayan yace mu taho mai dashi nima nai tunanin sawa a dan samomin jin yanda suke da tsada sosai." Abbas ya bud'e baki cikin mamaki yace "Hashim kanka daya kuwa??" Hashim ya mike rai a b'ace yace " me? Yanzu dan ka zama babban mutum kana tunanin zaka wulakantamu? To wlh kayi kadan dolene kaje kasan yanda zakai su sakar mana kaya." Yana kai nan ya nufi hanyar waje, daidai nan Ruma na kawo kai, Abbas ya mike yace " ba dole a ciki, sannan tunda dai bakuji kunyar cutar da mutane ba banaji nima ya zamarmin dole na bi bayanku, kasan inka sai da hodar da makaman wadanda za'a cuta dasu? Kasan bayin Allahn daza'a halakar dasu?mai makon ma ka dauki laifinka akan kuskuren dakai sai ma gani kake baka aikata komai ba?" Hashim ya kalli Ruma yace " ke Ruma!" Mumy ta kalli Yayanta cikin tsoro, yace " wuce mu tafi gida, da alama Abbas ba sanki yake ba inhar bazai taimaki mahaifinki dake kwance a gadan asibiti ba saboda wani shirme can da zuciyarsa ke sanar dashi ba." Nan yai waje Ruma tabi bayanshi. Abbas yai shiru yana mamakin wannan al'amari, sai dai tabbas in har zai taimaki Hashim to lalai sai ya yi nadamar abinda ya aikata." Ashraf ya kalli Salim jin yayi shiru, yace " Uncle sai akai yaya?" Salim ya goge gomin daya keto mai yace " anyi haka da kwana d'aya Allah ya dauki ran mahaifin Ruma, wanda kuma shock din mutuwarta ya kwantar da mahaifiyarta ta samu ciwon paralyze." Idanu Ashraf ya zaro tsananin tsoro ya kamashi, Salim yai ajiyar zuciya yace " Abbas yayi dana sani sosai nakin taimaka musu da wuri, shi kuma yana ganin dolene Hashim yayi nadama saboda gaba. Sai dai faruwar wannan mumunan al'amari ya tada hankalin kowa, yayi nadama takin karawa gani yake daya taimaka da wuri Abban Ruma bazai

Table of Contents

Chapters

115 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115