Chapter 6
Chapter 6
garin Jahilai dama ai......" Dan litti yace " me kace?" Kai ya juya batareda yace komai ba. Inya tuna turancin Dan litti kawai sai ya saki murmushi lalai ana kwab'a a kasar nan. Tun yanajin dadin tafiya yana kalle kallen kauye har ya gaji kawai ya zauna yai dif. Yanaji Dan litti nata bashu labarin makaranta, shidai kam jinsa kawai yake fatansa Allah yasa suje su dawo kafin bakin alkalami ya bushe. Sunyi tafiya sosai kafin su isa Gwaram, nan Dan litti ya karasa bakin banki ya tsaya, ya kalli Dan binni yace " Gashi mun iso." Dan binni ya kalli bankin sannan ya kalli ATM din dake gun guda biyu ne a jere saidai mutanen dake tsaye a gun sunfi 20, wata iska ya furzar sannan yace " Dan litti ba wani sai wannan?" Dan litti ya kalli mutanen gun yace " Kasan karshen wata yayi ko munje wani gun ma hakan ne gwara mu tsaya anan." Dan binni ya kalli mutanen gun sannan ya tuna Nafi wacce ake neman ruguza mata rayuwa, takawa yai yaje har ya tsaya a layi yaga abin kamar bazai yiwu ba, hakan yasa ya karasa ya fara neman alfarma, abinda tunda yake arayuwarsa bai tab'a yi ba kenan wai ace shi ne ya rusunar da kai yake neman alfarma gun wasu, ya taso rayuwarsa ba abinda ya rasa, haka ya daure yai ta neman alfarma har ya dawo na 8, suna nan tsaye har aka zi kansa, ya zaro wallet dinsa dake aljihun wandansa ya ciro ATM card dinsa ya sa. Dubu Ashirin ashirn sau biyu ya cira sannan ya ciri dubu goma ya kama hamsin kenan, ya musu godiya ya karasa gun Dan litti, tafi Dan litti yamai yace " Gaskiya ka birgeni yanzu mu tafi?" Dan binni ya kalleshi yace " yunwa dai nake dan ji." Dan litti yace " Ga mai Yam da Egg can muje sai ka siya." Murmushi yai sannan yace " Lalai Dan litti dan boko." Dan litti ya shafa keya yace " Can we went?" Dan binni ya juya kai sannan suka karasa gun mai doya, kashi biyu yace asa musu wato shida Dan litti, har zasu juya sai ya koma yace a kara samai wani daban, haka kawai yaji zuciyarshi ta tuno mai da Nafi. Dan litti ya shiga godiya nan suka ci sukasha leman kwalba sannan suka mike suka juya. ************ A can rigar Datti kuwa Nafi ce zaune a dakinta banda kuja ba abinda takeyi ga bakin cikin auren da za' a mata gana guduwar dan binni, mamaki ne ya kamata dataji mutane suna sallama, nan ta fito dan tasan su ba baki suke ba tunda Baffa baso yake ba, turus ta tsaya tana kallan kanwan mamanta, sai dai ta kasa farin cikin ganinta sam. Ganin haka yasa ta matso tare da rungume Nafi tace " Nafi shine kina ganina zaki shareni? Bayan har da kawarki Hanne nazo miki da ita? " Nafi ta maida hawayenta sannan tace " Aunty nayi mamakin ganinki ne." Tace" ai daga ke har Datti baku kyauta mana ba wau sai dazu aka turo mana almajiri wai yau ake auren ki? Haba Nafi ai ko Datti bai sanar damu ba ke kya fada mana ai." Nafi kam kasa magana tai dan batasan taka maimai mema zata ceba cewa zatai an bada ita biyan bashi ko me? Hanne ce ta matso kusa da ita tace " Nafi ya naga ba kowa a gidan? Kamar ba biki za'ai ba?" Nafi ta share hawayenta tace " eh kinsan Baffa bayasan mutanene shiyasa." Baki Hanne ta tab'e tace " amma dai duk da haka, sannan ke ma kalleki kamar ba Amarya ba ko wanka ma da alama bakiyi ba." Nafi tadan juya kanta gefe, Nan Maman Hanne tasa Hanne ta debo ruwa, da kanta ta tasata gaba sukaje ta wanketa fes, sannan suka fito, kayan Nafi ta kalla sam bana arziki bare aje ga sabo haushi da tausayi suka kamata ta kalli Hanne tace " Hanne da alama ke zaki taimaka ki ciro kayan jikinki ta saka inyaso ke sai kisa nata." Hanne ta kalli Nafi tace " Allah Nafi shi yasa kike ban haushi ke wai bazaki taba cewa asai miki kaya ba? Ko sanda innarku nanan itama banga ta wani damu da miki dinki ba, yanzu dan Allah meye amfanin hakan?" Nafi tai kasa dakai, Hanne taja wani dogon tsaki tace " sam ita wannan a kidahuman ma ita ta dabance, fa tsinanan kawaici da hakuri, wallahi babu inda zakiji ba'a cuce ki ba indai haka zaki cigaba." Maman ta tace " to ya isheni uwar 'yan masifa." Nan Hanne ta cire kayanta tana masifa. Nafi ta saka kayan sun amsheta kuwa nan Hanne ta shafa mata hoda tana shirin yi mata ja gira da kwalli Nafi tace " Bashi Hanne kema kinsan banasan kwalliya." Hanne ta mike cikin takaici tace " ni dai kam ban taba ganin mutum irin ki ba, gaskiya Nafi kina neman addu'a ni wallahi haushi wannan halayen naki suke bani." Tana kainan tai hanyar waje, jitai Nafi tace " kiyi hakuri Hanne ba bata miki rai naso yi ba." Hanne ta kara had'e rai tace " kinganta ko Goggo? Yanzu me tayi na bada hakuri dan Allah?" Tai waje ba tareda ta jira amsa ba. Maman Hanne ta kalli Nafi tace " Nafi kiyi hakuri kinsan kawartaki akwai masifa." Hanne ce ta shigo cikin mamaki tace " Nafi naga sun fara taruwa inaji yanzu za'a daura, ni ko mijin ban gani ba." Gaban Nafi ne ya fadi tanasan yin kuka ba kuma taso su Hanne da mahaifiyarta susan halin da ake ciki, kasa kawai tai da kanta tana karanta Inalilahi a zuciyarta. Ango kam yasha babbar riga haka kuma ya taho da abokanansa dayawa dama yan uwa da makota, sannan sun taho da liman da maroka, Datti ne yashigo gida fuskarsa a sake wasai ko a jikinsa, ya zura riga babba shima, yanajin Mahaifiyar Hanne na gaisheshi ya shareta yai waje. Ta birma manya aka shimfida musu sannan Ali ya taho da goro nan aka ajiye, Aka dan gagaisa sannan aka zauna. A ciki kuwa mahaifiyar Hanne ce ta kalli Nafi tace " Nafi amma an miki komai na kayan daki ko?" Nafi ta kalleta tare da kakaro murmushi kawai amma batace komai ba, hakan yasa itama tai shiru. An gama addu'oi nan aka ce ina Walliyin Alhaji Ali? Wani kanin mahifinsa yace " Ganinan." Akace walliyin Nafi fa? Datti yace gani. Kallan mamaki suka bishi dashi sukace " Dakanka malam Datti? Ai kyanta wani dan uwanka na kusa zaka wakilta." Datti ya hade rai yace " wannan damuwarku ce amma nine zan zama walliyi a auren 'yata ehe." Sunyi shiru, liman ya kalli Ali, kai Ali ya daga mai akan ba komai a kyaleshi, nan liman yace to shikenan yanzu zamu gabatar da......... Ji sukai ance " Ba abinda zaku gabatar domin kuwa ni na hana wannan auren." Gaba daya suka juyo suka kalli inda maganar ke fito wa, ga mamakinsu wani saurayi ne ya sauka daga kan mashin sannan ya fara takowa gunsu cikin isa da takama, basusan fuskarba sai dai Datti yasanshi dan kuwa bai manta shi ba. Dan binni ya karaso
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115