Chapter 63
Chapter 63
yai tace " eh after that, then what?" Ya shafa kansa yace " ban fara wannan tunanin ba." Murmushi tai sannan tace " I am sorry." Kallanta yai yace " for what?" Tace " bazan iya abin da kace ba, me yasa a koda yaushe zuciyarka ita kadai ce mai amfani agunka? Me yasa baka tunanin tawa?" Ya kalleta yace " Me kike nufi?" Kai ta girgiza sannan tace " Ka dinga ajiye matarka akusa dakai ba ni ba, nima daga yanzu zan fitar da wanda naga yana sona inyi aure." Tana kaiwa nan tai waje, kallo ya bita dashi sannan ya runtse ido ya bud'e tare da naushin iska yace " Ashraf meke damunka? Me yasa duk lokacin da ka shirya abu daidai pride dinka ke hanaka???? Wata iska ya furzar ta takaici..... Nafi kam tana fita hawayen datake boyewa suka fara zubowa tafiya kawai takeyi sam bata kula da Asim ba wanda suke zaune suna hira. Shikuma yana ganinta ya mike tare da shan gabanta yace "ke yar iska?" Kallansa tai da jajjayen idanunta, yasa dariya yace "au har kwarton naki ya fara b'ata miki rai? Ki dawo guna ni zankula da ke sosai." Hararsa taicikin takaici tace " ni nafi karfin karuwa kuma inma karuwancin ne mai zanyi dakai? Tana kai nan tai gaba, Asim kam ya kai kolowa gun bacin rai, ya juyo da niyar zaginta yaga wayam, hucci yai yace "lalai za'a kai gawar 'ya garinsu...." Nace hmmmm...... *#ASHRAFFEENAH TEAM* *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 _Godiya gareku 'yan Nice Hausa Novel musamman hajiya admin Aisha Sabi'u Mohd....ILYSM😍_ { *50*} Nafi kam a falo ta zauna ta dafa kanta itakam Allah ya yaye mata wannan abun dan bata ganin akwai riba a cikin wannan san da takema Ashraf. Kwanciya tai daga nan bacci yai gaba da ita akan kujerar. Sai la'asar ta tashi tana shiga taga Little ma bacci take nan tai sallah sannan ta tasheta itama tai, kitchen ta nufa dan kara samun fasaha akan girki. Sai 6 ta fito tana shiga bayan sunyi magrib aka aiko wai ana sallama da ita, mamaki ya kamata ta tsare Little da ido, Little tace " ba Alamin bane Allah dan shi baima san kin dawo ba." Nafi tace "to waye??" Little tai murmushi tace "ki shirya sai ki dubo mana." Harararta Nafi tai tace "wani shiri kuma? Bansan waye ba kawai sai in hau kwalliya sai kace mai neman saurayi?" Little ta sa dariya tace " to da mecece?ai duk budurwa nema take har sai ta samu tsayaye." Nafi ta tabe baki ta zari mayafi tai gaba Little na tsokanarta. Waje ta fita mota d'aya ce a gun hakan yasa ta tsaya daga dan nesa tana tunanin karasawa, fitowa yai tare da zama a saman motar yace "My Feena ko sai na zo da kaina?" Jin muryar Nabil yasa tai murmushi sannan ta karasa, kallansa tai cikin zolaya tace " da alama rashina ya hanaka sukuni?" Ya dafa kai yace "Feenah taba kiji inaji zazzabi ne ke neman kamani saboda missng dinki." Tai dariya tace "Ya Nabil to ya? Nayi mamakin ganinka a daren nan." Ya kalli agogo yace " ko isha'i batai ba shine dare?" Tai dariya sannan tace "Ina Aminiya?" "Tana gida nima wucewa nazo yi nace bari na tsaya mu gaisa." Murmushi ta sakeyi tace "aikam na gode." Ya kalli gidan yace "dama a gidan Marigayi Abbas kike?" Kallan mamaki tamai tace "kasanshi ne?" Dariya yai yace "ina fa mutumin daya rasu kafin muyi wayau." Tace "then?" Yace " A company dinsa dai Dad yai aiki." Cikin mamaki tace haba? Ya daga mata kai sannan yace "Amma tun bayan rasuwarsa shima ya ajiye aikin." Nafi tace "me yasa?" Iska ya dan tara a bakinsa sannan ya furzar yace "bansan dalili ba." Kallo ta tsareshi dashi tace " Kace wallahi." Yai murmushi yace " me nene matsayinki a gidan?" Ta kalli gidan sannan tace "nima bansani ba ganinan ne dai kawai." Dariya yasa yace "ban gane ba." Tace Wallahi dagaske." Kallan mamaki ya mata yace " kiyi a hankali to da irin wannan gidan manakisa da sharrinsu yawa gareshi, dan mutuwar Abbas din........" Bakinsa ya guntse jin yana shirin yin baran barama, Nafi ta kalleshi fuska dauke da mamaki tace " Me? Akwai sa hannu ko me?" Juyar dakai yai yace " Hmm yaushe zakizo gida?" Tace "Ya Nabil?" Kallan gate yai yace "ga wani can ya fito da mota." Nafi ta kalli gun, motar Ashraf ce idanunta ta kaida kan Nabil tace " Ya Nabil dan Allah me ka sani??" Kifta ido yai yace "bazai miki fada ba?" Hade rai tai tace " akan me kenan?" Zaiyi magana yaga an dallesu da fitilar mota wanda sai da Nafi ta juya, ta tabbata so yake yaga waye, shiyasa tana juyawa ta maida kanta gun Nabil. Ashraf kam wanda suka fito shida Anisa. Ya tsaida mota batare da ya kashe fitilar ba, Anisa ta kalleshi ya had'e rai tare da kafe Nafi da ido, mamaki ya kamata. Shikam Nabil kallan Nafi yai yace " Feenah da alama ke ake jira kar inja a miki fada bari na tafi." Da sauri tace a'a yaya taimakamin karka tafi please. Yace "Ba kya tsoro?" Kallansa tai fuska dauke da murmushi tace " mu shiga motarka mudanyi gaba please, sannan banaji zan barka ka tafi baka karasa fadar abinda zaka fada dazu ba." Kallan mamaki ya mata, ta shagwabe fuska tace "please " Sauka yai sannan ya zagaya ya bud'e mata mota ta shiga sannan shima ya shiga tare da tada mota. Anisa ta kalli Ashraf tace "wai me mukeyi anan ne?" Bai ma san tanayi ba dan wani irin abu ne ya tasomai yana ganin sun hau kan titi ai kuwa shima ya taho da gudu da mota ya sha gabansu saura kiris motoci biyun su bigi juna, Nafi kam da Anisa duk sun runtse ido kowa na tsoron abinda zai faru shikanshi Nabil ya tsorata, Ashraf a zuciye ya kashe mota sannan ya fito ko kofa bai rufe ba yazo Kofar da Nafi take ya bud'e da karfinsa. D'agowa tai cikin tsoro tana kallan idanunsa da suka kada sukai ja sai hucci kawai da yakeyi, hannu yasa ya fizgota da karfi, Anisa ganin haka yasa ta fito tare da shan gabansu tace "Ya Ashraf me kakeyi hakan? Ina zaka bayan kasan unguwa zamu?" Kallanta yai cikin idanunsa da sukai ja bai bata amsa ba kawai ya zagaya ta gefe ya sa Nafi a bayan motarsa ya shiga ba tare da ya kuma kallan Anisa ba yai reverse sannan ya ja motar a zuciye. Nabil kam wannan abu ya d'aure mai kai shima a hankali yaja tasa motar yai gaba yabar Anisa wacce ta tsaya kamar gunki. Ta dade agun kafin ta koma gida, gun Umma ta nufa tai sa'a Asim nanan nan ta zayyane musu abinda akai tare da fashewa da wani irin kuka. Umma ta mike tsaye tace " Asim dole ne musan abinyi dan nikam na gaji da wulakancin wannan dan marasa tarbiyar." Asim a zuciye yai waje ya nufi bangaren mahaifinsa...... Shikam Ashraf gudu kawau yakeyi, Nafi kam tayi shiru a baya sai dai har yanzu tsoron
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115