Skip to content

Chapter 88

Chapter 88

Zuciya Kowa Da Irin Tasa Book One Complete Hausa Novels 1,165 words 0 views Progress saved
Download Book

ja mota duk inda kuke in nemeku, nagaji da wannan dadirancin da kukeyi." Umma ta matso itama tace " Kai Ashraf a wani matsayi Anisa take a gurinka? Ka maidata kamar ba matarka ba sam ka daina ko shiga harkarta, kana tunanin mu iyayenta zamu barka ne?" Asim kam kallan Ashraf kawai yake yana hucci. Nafi ta bud'e motar ta fito tana kallan ikon Allah, Ashraf ya zare hannun Anisa daga jikinsa a hankali yace " Nisa calm down wannan fadan fa?" Kallansa tai idanunta ya ciciko tace " yaya bazan iya ba, na san ba sona kake ba, ni kuma wlh bazan iya zama da waccen tsinaniyar ba." Ta fada tana nuna Nafi. Ashraf ya dan kalli Nafi kadan sannan ya maida idansa kan Anisa mayafinta da ya fadi kasa saboda masifa ya tsugunna ya d'auko mata, ba wanda ya zata sai gani sukai ya yafa mata mayafin ya kalleta cikin kulawa yace " Nisa kalleni nan." Jikin kowa ne yai sanyi, Umma a ranta tace " dama ta ina za'ace yaron da suka taso tun suna kanana har yafi san wata wacce basu dade da haduwa ba." Nafi kam jitai wani abu ya tokare mata makoshi, kallansu kawai take tama kasa ko motsi. Asim ma mamakin Ashraf ne ya kamashi. Gogar kuwa duk jikinta ya gama sanyi kallan Ashraf kawai take kamar yanda ya umarceta, Ashraf yace " Nisa!" A hankali tace " Naam." Yai murmushi yace " Yauwa ko kefa." Kallansa ta tsaya tanayi, ya saketa tare da juyawa ba tare da ya kalli Nafi ba zai wuce. Da sauri Anisa ta riko hannunsa tace " yaya nidai wlh ka zaba ko ni ko waccen, banaji zan iya ganin tana zama kusa dakai zuciyata bata fashe ba." Ba tare da ya juyo ba ya had'iyi wani abu sannan yace " Karkisata a ranki u r so dear to me." Yana kaiwa nan ya ja hannunsa yai gaba. Nafi kam bata san sanda taji hawaye ya zubo mata ba tana kokarin mai magana taga ko kallanta baiyi ba yai gaba. Yana tafiya Umma ta matso gunta tana dariya tace " ah ah su Amarsu yanzu kin tabbatar da matsayinki?" Kallansu tai ba tare da ta tanka ba, mamaki take mai ya samu Yaya daga shigowa? Umma tai dariyar mugunta tace " ah to da an fada miki barno gabas take? Shi dama namiji kan ya samu abinda yake so ne zai ta lallabaki amma da ya samu shikenan kin zama kashi." Wani irin kallo Nafi ta kafe Umma dashi, Umma ta wanka mata mari tace " A da in mun barki kinyi iskanci saboda mijinki ya baki matsayine bawai yanzu da kike kamar bola ba." Anisa ta matso tace " ke harkin isa dama kice zaki kwace min miji? Yar kauye dake? Mutumin da na taso dashi tun muna yara ke kuwa yar karo?" Nafi wacce ke rike da kuncinta ta daure tace " wannan kuma tunaninku ne ba na yaya ba." Tana kaiwa nan ta fara dingisa kafa tana gaba. Anisa ta matsa ta fizgota da karfi tace " ni kika fadama magana d'azu ko?" Nafi ta kalleta tare da fincike jikinta ta cigaba da tafiya, Anisa tasa dariya tace " yi maza ki je ki shiya yan kayan da kika samu anan kafin insa a baki takardarki." Nafi bata juyo ba tai bangarensu. Tana shiga ta zauna akan kujera a falo, meke faruwa? Tayaya ya Ashraf zai canza mata lokaci d'aya? Da sauri ta girgiza kai alamar a'a tace " Yanada reason dinsa ni na sani, zanje anjima in ma laifi na masa in bashi hakuri." Da wannan shawara taji hankalinta ya kwanta. Anisa kam tana ganin tafiyar Nafi suka kwashe da dariya, Asim ya matso yace " Anisa ina mamaki fa ya akai hakan?" Anisa ta dan yi fari da ido tace " yaya na sona ni nasani kawai abinda ya faru ne yasa ya shareni." Asim yace " to yanzu kije ki lallabashi ki samu kisan yawan dukiyayonsa da kuma inda takardun suke, karki bari ya gane komai." Kai Anisa ta jinjina alamar gamsuwa tace " karka damu yaya ni nasan ya Ashraf a tafin hannuna yake." Dariya sukai dukansu, Anisa ta wuce bangaren Umma da sauri tai wanka ganin magrib tayi tai sallah sannan ta saka wasu riga da siket 'yan kanti sun bi jikinta sosai. Mayafi ta yafa sannan ta fito tace "Umma ya kika ganni?" Umma ta shiga tafa mata tace " yauwa 'yata sai da safe." Nan Anisa ta fito cikin tsantar farin ciki. Bangarensu ta nufa tare da bud'e kofa. Ashraf na zaune ya baza wasu takardu yana dubawa, jin motsi yasa ya d'ago. Ganin Anisa yasa ya sakar mata sansanyan murmushi. Cikin rangwada ta karaso gunsa tace " yaya shine bakazo biko ba ko?" Kallanta yai bayan ta zauna daf dashi yace " sry Nisa kunya ce ta hanani zuwa." Kankameshi tai tace " yaya nagode da ka nunamin kana sona." Zareta yai daga jikinsa yace " Amma kin dawo kenan ko?" Cikin shagwaba tace " anya kuwa?" tafada tana karema takardun kallo, tace " wad'an nan fa?" Tataresu ya farayi yace " ba komai." ya fada tare da mikewa da sauri Ya nufi d'akinsa." Kallan bayansa tai tace "da alama takardune masu amfani ganin yanda ya kwashesu da sauri, sannan da tana dubawa taga kamar takardun fili." Mikewa tai da sauri tabi bayansa, kofar dama bai rufe taba. Yana kokarin sawa a drawer ta jikin madubi sai ga Anisa. Da sauri ya tura yasa key, ta matso gunsa tare da rungumeshi ta baya tace " ka gama?" Makullin ya bari a jiki ya juyo ya kalleta yace " eh muje falo." Nan ta kara kallan gun sannan sukai falo. zama sukai ta zauna akan cinyarsa tare da rungumeshi ta fara sambatarsa, sam hankalinta ya gama tashi saboda rashinsa datai kwana biyu bataji buga kofar da ake ba. Ashraf ya d'an zareta kadan yana kokarin sauketa Nafi ta turo kofa, tunaninta jin tanata bugawa ba'a bud'e ba mayb yana masallaci sai tai tunanin ajiye masa abinci tai gaba. Cak ta tsaya daga jikin kofa tana kallansu. Anisa kam ganin Nafi ce yasa tai wani dariyar mugunta sannan ta kara kai bakinta cikin na Ashraf tana mai wani saban salo. Nafi kam jitai jikinta yana kakkarwa anan bakin kofar ta ajiye abincin tai waje da sauri. Tafiya kawai take batasan inda take sa kafarta ba sam kuma bata kallan gabanta. Saura kiris ta buge da bango taji an jawota, kallan wanda ya jawota tai, jitai yace " Gimbiya me kike tunani haka?" Kallansa take kamar bata cikin hayyacinta ta kwace hannunta tana kokarin ci gaba da tafiya. Gabanta yasha yace "Gimbiya menene? Baki kula dani bane?" Kallansa tai sannan ta kewayeshi tai gaba. Bin bayanta ya farayi yana mata magana sai dai da alama batama san yanayi ba. Sunje shiga bamgarensu, Little kuma na shirin fitowa. Ganin Nafi yasa ta karaso da sari tace " Ni harzan gudu gun Mumy muyi hira dan nasan ke kuma sai gobe ni da na ganki." Nafi ta kalleta sai dai batace komai ba, muryar Habib taji yace " Princess kece?" Da sauri ta matsa daga gun Nafi ta karasa gun Habib, itakam

Table of Contents

Chapters

115 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115