Skip to content

Chapter 28

Chapter 28

Zuciya Kowa Da Irin Tasa Book One Complete Hausa Novels 1,135 words 0 views Progress saved
Download Book

wuce makarantar kwana dake kazaure. " Nafi kam idanunta ne suka ciciko, wani irin farin ciki ne wanda ita kanta batasan irinshi ba yake ratsata, Ashraf yace " meye hakan? " Hawayenta ta goge wanda suka zubo, ta girgiza kai tace ba komai. Habib cikin damuwa yace " Bakyaso ne? " Kai ta girgiza da sauri tace "a'a ba haka bane. " Ashraf ya d'an kuraa mata ido kamar yanasan gano wani abun, idanunta tai saurin yin kasa dasu tace a hankali tace " Yaya babana fa?" Jiyai ransa ya b'aci ya ce " Bansan inda yake ba, kuma bana fata insani, sannan in har da haka kike tunanin yin karatun to gwarama karkije, dan ni na tsani mutum mai raunanniyar zuciya. " ya mike yai ciki. Kallo ta bishi dashi zuciyarta tana dana sanin tambayar datai, sai dai duk yanda taso da daurewa ai dole ne tai rashin mahaifinta. A ranta ta maimaita Raunanniyar Zuciya? Me kenan? Kamar Habib yasan meke ranta yace " karki damu da fadan Ashraf dan shi yawancin maganarsa haka take. " Nafi tabi d'akinsa da kallo tanasan ta bashi hakuri ta kuma tambayeshi ciwon sa, daurewa tai ta kalli Habib tace " Ya Habib meye raunanniyar zuciya? Ma dai san me zuciya take nufi" Dariya yai yace " rauni fa? " Tace " na sani. " Ya sake dariya yace " to sai ki had'asu guri d'aya ki gani. " Tace " Rauni Zuciya? " Wannan karan dariya sosai Habib yai yace " lalai Nafi inkinje makaranta cikin mutane a hankali zaki fahimta. " Tace to, sannan ta sake kallan d'akin Ashraf sai dai ba yanda zatai, mikewa tai zata fita, Habib yace " aiki kikai ne? Naga kayanyi sun b'aci kamar daga kitchen kika fito. " A'a kawai tace tai saurin fita. Tana gaba kad'an sai ga Aneesa wacce tasha kwalliya tana tafe kamar sarauniya. Idanunsu ne suka had'u, gaban Nafi ne ya fad'i bawai dan tsoro ba a'a sai dan ganin kyan datai, a cikin zuciyarta tace " Dole Ya Ashraf yasoki. " Tun datazo gidan bata taba ganin Aneesa ta d'au kwalliya irin haka ba, ba namiji ba ko mace ce ta wuce dole ne ta kalleta dan tayi kyau sosai, Aneesa wacce takura ma Nafi ido cikin tsananin takaici ta karaso. Kwalliya tai dan taje su shirya da Ashraf amma me take gani haka? A zuciye ta karaso tare da kallan Nafi cikin tsananin takaici tace me kike anan? " Nafi ta kalleta sai dai ta kasa cewa komai, Aneesa ta sake kuluwa tace " ke dan gidan ku ba magana nake miki ba? " Nafi ta daure kawai jitai ta sami kanta da cewa" Ya Habib ne ya kirani. " Aneesa wacce bata gamsu da zancen ba tace " Nafi karkiga jiya nazo da niyyar dukanki ki d'auka wai ko kishi nake dake ko wani abun. " Ta d'anyi dariyar kissa tace " Tausayi kike bani, kinfi kowa sanin ni dake ba d'aya bane sannan ke da kanki zaki iya warewa kisan wa ya dace da Ashraf ko ince wa Ashraf yake so, dan haka ina baki shawara in ma da wani shirme ko yarinta akanki gwara tun wuri ki cireta dan kinsan wutsiyar rakumi tayi nesa da kasa, ke ko masu aikin gidan nan sun fiki daraja. " Ta bangaje ta tai gaba, jitai ranta yayi sanyi ta tuno maganar Umma datace " ki nuna mata ita ba komai bace ta hakan ne inma da wani munafircin a ranta zai sa ta shiga hankalinta."juyowa tai ta kalli Nafi tana nan a inda ta barta, ta sake dariya sannan tai gaba. Nafi kam sai juya kalamun take a ranta, tafi kowa sanin Ashraf yafi karfinta, ta kuma sani ko kata sun kare ba abinda zaiyi da ita sai dai meyasa takejin zuciyarta ba dadi? Wata zuciyar tace kema Nafi kina ganin mai mace kamar Aneesa me zaiyi dake? Jiki duk a rame? Gaki yar kauye wacce ake neman biyan bashi da ita? " Da kyar ta karasa d'aki tai wanka sannan tasa abinci a gaba, da kyar takeci ta rasa me yasa batajin dadin abincin sam. Aneesa kam tana shiga taga Habib zaune a kan dinning yana cin abinci, tai murmushi tace " Yaushe a gari d'an uwan Ango? " Habib ya kalleta yace " Amarya irin wannan kwalliyar kamar yauce ranar? Ko dai anzo seducing d'in d'an uwa nane? " Aneesa ta d'anyi dariya har hakoranta suka fito ta d'an karkace kadan tace " me? Kana tsoro ne? Ko kuwa kishi kake ba kada me ma?" Habib ya rike haba yace " tab lalai d'an uwana yana cikin tashin hankali gwara muyi sauri mu kawoki kafin ki burkice mana d'an uwa." Aneesa ta d'an fara tafiya cikin salo tare da cewa " ah to wayace kukai bikin da nisa?" Habib ya bita da kallo yana murmushi. D'akin Ashraf ta murd'a, kai tsaye ta shiga, Ashraf wanda ke kokarin shiga wanka ya kalli kofar kansa tsaye ya d'auka ko Habib ne, ganin Aneesa yasa ya had'e fuska tamau, ta sakar nai wani murmushi tace " Sorry Hubby ashe wanka zakai. " Ya kalleta yace " Aneesa bakisan ya ake sallama ba ko kwankwasa kofa ba? " Ta shagwab'e tare da shiga ta zauna a bakin gado tace " nida d'akin mijina? " Ya girgiza kai cikin takaici yai hanyar toilet sannan ya tsaya ya kalleta tare da cewa " nine mijin kuma banaji na bada sadaki bare a shafa fatiha, dan haka ki kiyaye shigomin d'aki kai tsaye." yana kainan ya shige toilet. Aneesa ta turo baki cikin jin haushi sai dai ta kasa cewa komai sannan tana kunyar fita kar Habib ya mata dariya...... *THE INNOCENT TEAM* *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *Hajja ce! I Sincerely Dedicate This Page to You... ILYSM😍* *24* Tana nan a zaune jugum har ya fito daga wanka, daga bakin kofa ya kalleta fuskar nan a had'e tam yace" me kikeyi har yanzu? " Mikewa tai ta d'anyi rau da ido tace " Haba Hubby na taya na ciwo kwalliya dan in birgeka zaka dinga wulakantani haka? Tunda kaga nazo ai kasan hakuri nazo in baka. " Ashraf ya wani saki murmushin rainin hankali sannan ya mata wani kallo wanda ita da akawa ita kadai tasan me yake nufi yace " Ko? " Tace " bangane ba? " Ya d'an juya kai gefe yace " ke kina tunanin har kinkai matsayin da zaki tozartani a gaban mutane sannan ki biyo ta baya kice zaki ban hakuri? " Aneesa ta d'an canza fuska kad'an tace " Amma Yaya kasan dai ko waye dole yaji haushi, ko bakasan na dinga kishin ka? " Kallanta yai sannan yad'an girgiza kai na takaici hanyar waje ya nuna mata da yatsarsa yace " yi nan. " Ta kare lagub'e fuska, yace " kinfi karfi? " Juyawa tai a hankali tai waje tana fita yasama kofar makuli, tare da jan tsaki. Nan ya shafa maganinsa sannan ya shiga kokawar sa kaya, bayan yasa ma kwanciyarsa yai a kan gado. Itakam Aneesa tana fita Habib ya kalleta tare da guntse dariyar datake kokarin tahomai yace " Badai fada kukai ba? " Ta kalli Habib kamar

Table of Contents

Chapters

115 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112
  113. 113 Chapter 113
  114. 114 Chapter 114
  115. 115 Chapter 115