Chapter 73
Chapter 73
kalleta yace " kinji haushi ko?" Kai ta jinjina alamar eh, yai murmushi yace " kinsan......" Ta katse shi da cewa " haushi na d'aya kana bacci an tasheka." Kallanta yai tare da murmushi ya jawota jikinsa, sannan ya kamo hannunta sukai toilet. Kallanta yai ya mika mata towel, ta amsa sannan tace " ka fita to." Baya ya juya sannan yace " ki cire a haka dan ba inda zani, ai ba kallanki nake ba." Ta ce " taya zan yarda bazaka juyo ba?" Yai murmushi yace " in ma na juyo ai abuna na kalla ba na wani ba." Juyawa tai da sauri cikin kunya. Da kyar ta cire kayan ta d'aura towel din sannan ta sa kayan a bokiti, tace kazo ka cire naka sai in wanke mana." Murmushi ya mata sannan ya sa wani takalmin ya shiga toilet din. Juyowa tai zata fita ya riko hannunta. Nan ta tsaya ba tare da ta juyo ba, yace " ina zaki??" Kallansa tai da sauri tace "naam?" Yace " ina zaki nake tambaya, dan nasan kinjini." Tace " waje zani in ka...." Hannunta yaja yai wajen sink da ita kallan sa kawai takeyi, gani tai ya d'auko man wanke kai da alama nashi ne ko na Anisa ne ni dai ban sani ba. Ya mata alama data sa kanta. Ta kalleshi tace " yaya me....." Hannu yasa a bakinsa alamar tai shiru sannan ya mata alama data sa kanta. Nan ta sa kanta tana tunanin me bawan Allahn nan yake shirin yi. Ribbon dinta ya zare sannan ya zuba man ya fara cud'awa a hankali, shiru tai tsantsar mamaki ne yake mata yawo a zuciya, dama haka Yaya yake??? Jitai yace " kina mamaki ne?" Cikin rawar murya tace " ni ban ce komai ba." Ya sake murmushi sannan ya sunkuyo saitin kunnenta yace " na dade ina sha'awar wanke kan nan tun kafin ki koma skul, sanda mukaje siyayya." Tai kamar zata d'ago ya maida kanta kasa yace " kina mamaki ne?" Tace " na fahimci me yasa yaya nisa bazata iya rabuwa da mutumin nan ba." a ranta tai maganar batasan a fili tai ba sai jitai yace " da cewa akai zan rabu da ita? Ko kuwa abinda kike so kenan?" Idanu ta runtse kunya ta kamata, da sauri tace " ni na isa? Na san irin san da kuke ma juna??" Murmushi yai a ransa yace " bantaba san wani ba sai a kanki dan ban taba tunanin zan iya yima mace wadan nan abubuwan ba." Anisa kam wacce tazo daukan kaya sam kasa dauka ma tai ta koma bangaren Umma tana zuba kuka kamar ranta zai fita. Umma ta taso da sauri zata mata magana, Anisa tace "kun cuceni wlh ni bada kudin ba bada mijin ba." tai d'aki tana kukan takaici. Umma ta baza tagumi, a fili tace " kai wannan yar bafilatanan anyi tsinanniya, anya kuwa haka ta barshi? Da alama zan fadama Uwarsa dan banaji ta barshi haka, dama ita inaaa sam bata yarda da ita ba. *Dan Allah kuyi hakuri da wannan wlh wani irin mura nakeyi mai hade da ciwon kai, amma insha Allah zuwa gobe in yai sauki zakuga nayi posting, nagode.* *ZUCIYA* _ĸowa da ιrιn тaѕa_ © *na Ayυѕнer Mυнd* ayushermohd.blogspot.com *HASKE WRITERS ASSOCIATION*💡 *Where am i going to started? Ayeesh! U really left me without word, Thanks alot for the dedication of the whole book "Jini D'aya", I really appreciate ur love....May almighty Allah help and guide u through the right path...Ameen* 58 Bayan ya gama ne ya sa mata karamin towel ya sa mata akai sannan ya kalleta yace " zaki fita in watsa ruwa ko zaki zo mu watsa......" Ai bata jira ya karasa bama tao waje da sauri, murmushi yai sannan ya tura kofar. Nafi kam kofar tabi da kallo tace "wato yaya sam bashida kunya ko?" Zama tai a bakin gado littafin nan na diary ta gani a hankali ta zaro shi ta bud'e shafin farko "To My dearest Son Ashraf." Abinda ke rubuce kenan tai murmushi ganin wani d'an karamin hoto ba sai an tambaya bama Ashraf ne, passport ne da alama yana nursery aka d'auka tai murmushi sannan ta bud'e shafi na biyu. _Ashraf Allah baiyi zanga girmanka ba sai dai inaji ajikina ko bani zaka zama yaro na gari, mai san 'yan uwansa da na kasa dashi._ Nafi ta sake murmushi tace "Abba ai d'an naka ne ba a gane cikinsa." Tana bud'e d'ayan page rubutu ne sosai, tana kokarin karantawa taji motsin alama na bud'e kofa, da sauri ta maida littafin sannan ta mike. Ashraf ya kalleta sannan ya karaso inda take, yace "matsoraciya." Kanta ta kawar gefe batace komai ba. Toilet ta wuce da sauri, yabi bayanta da kallo zuwa cinyoyinta da suke a waje, kansa ya shafa sannan ya zura riga doguwa ya fita falo. Nafi kam bayan ta watsa ruwa ta fito tare da tsayawa a d'akin to me ma zatasa? Ina kuma yayan yaje? Rigarsa ta gani t-shirt irin mai dogon hannun nan kawai ta zura sai ta sauke towel din kasa ta d'aurashi kamar zani. Tana d'aura kanta da ribbon Ashraf ya shigo, kallanta yai yadanyi dariya yace " da har ina tunanin d'auko miki kayan yayarki?" Da sauri tace " wacce yayar?" Ya d'an bata rai kadan yace "wace yayar kike da ita a gidan nan?" Baki ta tabe tace " bansa kayanta bama an jikani ina kuma ga ta ganni da kayanta?ai inaji kanazir zata zubamin ta kyasta ashana." Ashraf ya danne dariyarsa yace " ke dai tsoronta kawai kikeji da alama, ko da yake baki da laifi Anisa ai akwai zuciya, ga kwarjini kuma bata da tsoro kamar o'o." Nafi ta d'an harareshi kadan tace " nima ai inada zuciyar kuma ba tsoro garen ba kawai dai raga mata nake nima." Ashraf baisan sanda yasa dariya ba, sai dayai sosai sannan ya kalleta ta wani ci magani yace " ayya bansan raga mata kike ba ai, ashe karamar matar tawa ba tsoro." Nafi ta kara had'e rai tace " ai in aka bi ta gaskiya ma nice babba dan nice uwargida." Baki Ashraf ya bud'e sannan yai dariya yace "Uwar gida?" Ta turo baki tace" to wacce in ba ni ba?" Dariya yasa zai yi magana yaji ana knocking, nan yai waje yana dariya, lalai yarinyar nan, uwar gida??? Ha ha ha ni kaina sai da na sa dariya. Dan liti ne bayan ya shigo ne Ashraf ya kalleshi yace " ya? Ina da ina yaje?" Nan Dam litti yashiga mai bayani, Ashraf yai shiru can yace " shikenan sai zuwa gobe." Dan litti yamai sallama ya fita, Nafi bayan taji rufa kofa ne ta fito, a falo ta ganshi ya zauna tare da sa hannunsa duka biyu akan hancinsa zuwa bakinsa, Nafi ta zauna kusa dashi tace "Lafiya?" Kallanta yai tare da girgiza mata kai alamar ba komai, ya mata murmushi. Itama murmushin tai sannan tace " nikam kun hadu da babansu Ferry ko?" Kallanta yai yace " Inda kikai yaji?" Tai murmushi tace " ka ganshi?" Kai ya d'aga alamar eh, sannan yace " ya akai?" Tace " baka sanshi ba ko?" Kai ya d'aga mata cikin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112
- 113 Chapter 113
- 114 Chapter 114
- 115 Chapter 115