Chapter 98
Chapter 98
“Wai da baki nake san yi” Cikin sakan ɗaya wannan fara'ar da ta ɗauke a ɗazu ta dawo, da rarrafe ta ƙarasa kusa da shi tana ɗora hannayenta a kan cinyarsa. “Da gaske wai?... Yaushe?” Kansa ya girgiza. “Sai bayan kin yi candy” Fuska ta kuma ɓatawa tana ɗaukewa hannunta daga kan cinyarsa, bakinta ta turo gaba tana juya masa kai. “To wai kai sai ka sawa mutum rai a kan abu kuma ka zo ka hana shi” Shi de bai ce mata komai ba, ya ci gaba da kallonta yana murmushi. “Ni dan Alah ka bani yanzu” Ta kuma faɗi tana masa fuskar tausayi. Kansa ya kuma girgizawa yana ɗaga kafaɗarsa. “Dan Allah Love Muffin!” Ta faɗi tana kamo fuskarsa, idonta ya cika da ƙwallar kukan shagwaɓa. “A'a fa?!” “Ni dan Allah ka bani ina so....” Kuliya na dariya yace. “Ba matsala ke kika nema ai!” * “Hafsat!” Kuliya ya ƙara kiran sunanta a karo na barkatai. Mishal dake duƙunƙune cikin bargo tana hawaye ta masa banza tana share hawayen. “Magana fa nake...” Ya faɗi yana taɓota. Hannunsa da ya taɓata da shi ta doke. “Ni ka rabu da ni... Kuma Allah sai ya sakamin... Ashe dama ba kayanka ne baƙaƙe ba ka ɗai, zuciyarka ma baƙa ce” Ta faɗi cikin kuka tana ƙara duƙunƙunewa. Kuliya ya ƙunshe dariya yana faɗin. “To me na yi?... Ke ce fa kika ce kina buƙata” Kuka ta fashe da shi tana rintse idonta gam. “Allah ban yarda ba... Kuma idan muka haɗu da Anti Adawiyya sai na faɗa mata abun da ka min” Dariya ya yi mara sauti yana kwanciya a gefenta. “Ki yi haƙuri to” “Anƙi a haƙura ɗin... Wayyo Allah na Anna... Wayyo Aki... Wayyo Anti Adawiyya!” Ta ci gaba da faɗin abun da take faɗi a ɗazu. “Kuma Allah sai ya mana hisabi, wannan sunansa zalunci, kuma Allah ya hana zalunci...” Juyowa ya yi yana kallonta, duk da tana lulluɓe da bargo. “Wai ba a muku biology ne?... Ya kamata a ce an muku a biology” “An mana ai... Ai an mana, amma ai basu ce da wahala irin haka ba... Wayyo Allahna!” Ta faɗi tana ƙara ƙanƙame jikinta wuri guda, saboda ƙasusuwanta da suke mata ciwo, ga wani zazzaɓi dake shirin rufeta, wani irin sanyi take ji yana shiga ko wace kusurwa ta jikinta. Kuliya ya yi dariya me sauti a wanna karon. “Ai da ma ba za su faɗa muku cewar akwai wahala ba” “Dariya kake min ko?...Ko... Ko?... Ko?” Ta ƙarashe tana fashewa da wani kukan. A hankali ya buɗe blanket ɗin, har ya samu damar ganin fuskarta, ta yi shaɓe-shaɓe da hawaye, ga kuma jan da fuskar ta yi, gashin kanta a yamutse, idon nan ma a koɗe. “Ki yi haƙuri please!... My bad, and I'm truly sorry” Ya faɗi yana rungumeta daga kwancen da take, dukan ƙirjinsa ta shiga yi, dan ita yau gani take nan duniya bata da maƙiyi kamar shi. “I hope we can move past this, ko kina so ni ma na yi kukan?” Sai kuma ta tsaya da dukansa da take, jin yanda muryarsa ta fito a sanyaye. Ta dakata da kukan tana kallon fuskarsa, wadda ya mata yanayin abun tausayi. “To ni ka min alƙawarin ba za ka sake min ba!” Cabɗi jam!, ai wannan ai shi ne wasa farin girki, ya faɗi a zuciyarsa, a fili kuma sai ya kyaɓe fuska yana girgiza mata kai. “Ba zan sake ba” Hanci ta ja tana kallonsa. Yayin da shi kuma a hankali yake motsa babban yatsansa a gefen fuskarta. “I hate you Abu Aswad!” Peck ya mata a goshi. “Mishallyn Aliyu you are the sun, moon, and stars, i love you more than my morning coffee, my heart is pitter-pattering for you” Naushi ta kai masa a ƙirji. “I hate da gaske” “Ni kuka na ce i love you da gasken-gaske... Jikinki akwai zafi sosai, yanzu ki kwanta, gobe sai mu je mu ga likita” Kai ta gyaɗa masa tana lumshe idonta. *T.O.C Douglas Crescent, Kaura District, Game Village, Abuja.* ZAID POV. “Zuwa gobe za a tura takardar ƙara kotu, daga nan za a fara zaman shari'a” Cewar wata garjejeyar murya da ke futowa daga cikin wata ipad dake aje gaban Zaid da Rhoda. A tare Rhoda da Zaid suka dubi juna. Kafin wannan muryar ta kuma faɗin. “A yau aka kamo wasu daga cikin waɗanda Alhaji Bala yake hulɗa da su, dan haka kuna cikin haɗari, fatan za ku kula!” “Ok sir” Suka amsa masa a tare, kuma daga haka wayar ta katse. “Yanzu yaushe za ki karɓi musulunci?” Zaid ya tambaya yana duban Rhoda, a sanda yake rufe ipad ɗin. Rhoda ta yi murmushi. “Zuwa ranar da kotu ta yanke hukunci, kuma daga nan zan je na duba dangin Mom. Sai kuma...” Dariya Zaid ya bushe da ita ganin yau ɗaya Rhoda na kunyar furta masa wani abu. Zaid ya ɗaga kafaɗarsa cikin faɗin: “Iko sai Allah, abun mamaki Rhoda yau ke kike jin kunyata?” Duka ta kai masa tana turo baki. Shi kuma ya yi dariya, dan ya san maganar aurenta take san yi. “Allah Rhoda ke da Ammata kun raina ni, daga na yi abu sai ku kawo min duka... amma ba damuwa, na dena muki wasa” Ya ƙarashe yana haɗe rai kamar gaske. Rhoda ta yi murmushi tana faɗin. “Ba ka ji ne ai” “Ji tsaurin ido, ni fa yayanki ne ba ƙaninki ba?” “Yi haƙuri to” ya yi murmushi uana ci gaba da kallon ƙanwar tasa. “Rhoda ki na san Zakar?” Ya mata tambaya irin wadda ya saba mata a duk sanda magana irin wannan ta haɗosu. Kanta ta gyaɗa masa tana murmushi. “Allah ya tabbatar mana da alkairi Cuzzie” * “Me gida Raja wai ina muka shilla ne?” Cewar Zuzu, wanda ke zaune a back seat na motar Zaid, daga gefensa kuma Jagwado da Alandi ne. A front seat kuma Zaid ne da Rhoda. Zaid ya ɗaga kafaɗarsa. “Ba na faɗa muku cewar aikin mu ya ƙare ba?... To wani wuri nake san kaiku” Daga haka babu wanda ya sake cewa komai cikinsu, har suka ida Rehab, wato gidan da ake kawai mutanen da suke shaye-shaye, ko waɗanda shaye-shayen ya fara taɓawa ƙwaƙwalwa. Su Zuzu ba su fuskanci hakan ba sai da suka ga an shiga da su ciki. *No.86, Garki 2, Abuja...* RABI'A POV. “Ammatan Raja!” Zaid ya kira sunan Rabi, wadda ke kwance a kansa tana daddana wayarta. Yayin da shi kuma yake kwance a kan kujera. Rabi ta ɗauke idonta daga kan wayar da take daddanawa ta kalli fuskarsa. “Au... Ina nufin 'Yan matan Yaya!” Nan da nan Rabi'a ta sha mur, dan ya tuna mata da abun da take san mantawa da shi. Harara ta wurga masa tana juyar da kallonta kan wayarta. Zaid ya yi 'yar dariya. “Wasa nake. Yanzu faɗamin, menene burinki a da, bayan kun yi aure da Yaya?” Sai ta ƙara kallonsa cikin rashin fahimta, kuma tun kafin ta furta cewa bata gane me yake nufi ba yace. “I mean, menene burinki, ko wani fatanki, ko mafarkin da kike, na irin rayuwar da za ki gudanar da shi bayan kun yi aure?” Ba ta yi mamakin sanin Yayan da ya yi ba, dan a yanda
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112