Chapter 67
Chapter 67
san ki ba ni duk wasu bayanai da kika sani a kanta, saboda ina san na fara bincike a kanta, kuma na miki alƙawarin samo miki ita” Farin cikin kalamansa suka sa Mishal miƙewa a kan guwowinta, sannan ba tare da ya shirya ba, ta faɗo jikinsa, tare da saƙala hannayenta ta wuyansa. Be san ya akayi ba, amma ya ji duniyar ta wani iri shiruu, kuma kamar shi ɗaya ne yake jin shirun, sai wata siririyar iska dake wucewa ta gefen kunnensa, ɗumin jikinta dake kama da na me zazzaɓi ya ratsa fatarsa ta cikin sayin acn dake ɗakin, wadda ya haddasa bugawar zuciyarsa fiye da kima, idonsa ya lumshe ya na sauraron nata bugun zuciyar da ya haɗe da tasa. “Thank you Abu Aswad, kai miji na gari ne” Mishal ta faɗi cikin tsantsar murna, hannun Kuliya na rawa ya ɗago shi, tare da ɗorawa a kan bayanta, ya na ƙara matseta a jikinsa, hakan ya sa Mishal ankara da abun da ta aikata, cak wannan dariyar da take ta tsaya, duk wani tunani na cikin kanta ya ɗauke, numfashinta ya ɗan yi nisa, kunnuwanta suka toshe, babu abinda take ji sai yanda ya matseta sosai, ta yanda har tana iya jin bugun zuciyarsa da ya haɗu da nata, nan take sanyi ya shiga bi ta jijuyoyin jikinta, ba shiri ta saki hannayenta dake kewa da wuyansa, amma kuma shi be saketa ba, face ƙara matseta da ya yi. “A... Abu As...as... Aswad!” Ta kira sunan a rarrabe, don ta tuna masa da halin da suke ciki, saboda ta lura da be ma san ya na yi ba, kuma maganar tata ce ta sa shi dawowa hayyacinsa. Ba shiri ya saketa da sauri ya na kawar da kansa gefe, ita ma sai ta ja baya daga zaunen da take, ta jingina da jikin gado, sai meda nunfashi take kamar wadda ta yi gudu a kan keke. “Ki... Kin yi abinci yau?” Ya tambaya ya na miƙewa, kuma ba tare da ya kalli fuskarta ba, da sauri ta gyaɗa masa kai, kuma ya ga hakan ta gefen idonsa. Ba tare da ta ƙara cewa komai ba, ta sauƙa daga kan gadon ta fita daga ɗakin, bayanta ya bi da kallo, kafin shi ma ya fice daga ɗakin. Kitchen ta nufa, hakan ya sa shi kuma ya zauna a falo ya na jiranta ta kawo masa abincin, don yanzu kullum girkinta yake ci, baya cin abincin waje kamar yanda ya saba sai da rana, da ranan ma dan ba ta gida ne, amma duk weekend sai ya dawo gida ya ci abinci. Kansa ya ɗaga ya kalleta a sanda ta aje masa plate ɗin tuwo da miya, alamun dai shi ne ta girka ɗin, ta juya da nufin barin falon, amma sai dakatar da ita ta hanyar faɗin. “Ina zuwa?” Sai ta tsaya ta na kallonsa, kafin tace. “Ɗaki” Sai ya ja plate ɗin da ta aje zuwa gabansa ya na girgiza mata kai. “Ki zauna, magana za mu yi” Sai ta kai hannunta ta ɗauke blanket ɗin da ta rufu da shi ɗazu, ta zauna a kusa da shi. Tambayoyi ya shiga mata a kan Rabi, ita kuma ta na ba shi amsa dai-dau da abun da ta sani, babbar matsalar a nan shi ne, adireshin gidansu, ita kanta Mishal ɗin ba ta san gidansu ba, kawai cewa take a Suleja take. “Na gode Abu Aswad, dan Allah idan ka samo ta ka haɗata da 'yan uwan Ummanta, Wallahi ta na shan wahala a gidansu” Kuliya ya juyo ya kalleta ya na haɗiye abincin bakinsa. “Ke da kika ce kin tsaneni” Mishal ta zumɓuro baki gaba. “To ba kai ne ka min tsawa ba” Ya ɗaga ƙafaɗarsa ta dama. “Ai na baki haƙuri” “To ai ni da ma ban tsaneka ba” Sai juyo gaba ɗaya ya na kallonta. “Me ki ke min to?” Tambayar tasa ta rikita Mishal, to ta ya za ta faɗa masa cewar ta na sansa, bayan shi bai furta mata abun da yake ji a kanta ba, to kuma ma kawai sai ta kalli idonsa tace ta na sansa?, ai abun ma be yi tsari ba. “Hummm?” Ya kuma tambaya ya ka kafeta da manyan idanuwansa, kanta ta sunkuyar ta kasa cewa komai. Kuliya ya juya ya ci gaba da cin tuwonsa, kafin muryarsa ta fito. “Kin tsaneni kenan?” Ta girgiza kanta da sauri, memakon ta ba shi amsar tambayar da ya mata, sai ta mako masa tambayar da ta sa ya dakata da kai lomar tuwon bakinsa. “Kai me kake ji a kaina?!” Juyowa ya yi ya kalleta, sai ya ga ta ƙara girma a idonsa, kamar ba wannan ƙaramar yafinyar da aka aura masa ba, ya kamata a ce ya faɗa mata abun da ke zuciyarasa, zuwa yanzu shi kansa ya san ya na buƙatar matarsa, da ɗin ma ba komai ne ya sa ya rabu da ita haka ba face ganin yarintarta, zuwa yanzu ya san cewa ta nutsu, ta kama kanta, duk da har yanzu ba za'a rasa guntun ɓirɓishin yarintar a cikin kanta ba. Sai de kuma akwai banbanci tsakanin Mishal ɗin da aka aura masa, da kuma wannan wanda yake zaune da ita. “Ni ma ban sani ba. Kawai de na san tun ranar da na fara ganin ki na shiga wani hali, ko me zan yi sai tunaninki ya shigo cikin kaina, ina san na riƙa kallon fuskarki, ina san a kullum ki riƙa zamma kusa da ni kamar da haka... Hafsat akwai wani abu a ƙirjina dake motsawa a duk sanda zan ganki, abubuwa da dama idan kika yi suna burgeni, walau shirme ko shirirta. Wata ƙila za'a iya kiran abun da nake ji a kan ki da SO! Amma ni ban sani ba, ban san menene ba” Ya ƙarashe ya na kallon fuskarta, hannunsa ya wanke a cikin ruwan da ta aje masa, sannan ya goge hannun, kuma har zuwa lokacin Mishal na kallonsa, kenan shi ma ya na santa? Amma me ya sa bai taɓa faɗa mata ba?, ya kamata ace ita ma da kanta ta gano hakan, to yanzu sai me ?, ita ta na san sa, ta san da wannan tun a waccan ranar da kishi ya rufe mata ido har ta aikata aika-aika. Kuliya ya juyo ya kalli fuskarta, tare da kamo hannayenta ya matsesu cikin nasa, hakan ya sa Mishal lumshe idonta, wannan sanyin da ya saba ratsa fatarta a duk sanda zai taɓata irin haka ya shiga aikinsa, ji ta yi jijiyoyin jikinta sun ɗau sanyi, bakinta ya shiga rawa, a sanda ta ji Kuliya ya matso daf da ita, babu wata tazara tsakaninta da shi, hatta da ɗumin numfashinsa a setin fuskarta yake sauƙa. A hankali ta buɗe idonta, sannan ta ɗan ɗaga kanta sama, ta inda za ta samu damar kallon fuskarsa, ba ta san haka ya yi kusa da ita sosai ba sai da hancinta ya gogi nasa, idanuwansu suka sarƙafe a cikin na juna, babu abun da take gani a cikin idanunsa face tsantsar soyyayarta da yake san ya bayyana mata, amma kuma ya rasa hanyar da zai bi ya faɗa matan. Zuciyarsa na bugawa da sauri-sauri, burinsa ɗaya, ya bayyana mata gaba ɗayan abun da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112