Skip to content

Chapter 39

Chapter 39

Labarinsu Book 1 Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

da baƙin ciki da ƙunar zuci Anti Karima ta kalleta tace. “Wai Kuliya aka ɗaurawa aure!” Wani irin duka gaban Siyama ya yi, har ta ji kamar an daki zuciyarta da ƙarfin da aka saka a wuta, kamar da Anti Karuma ta watsa mata barkwano, zuciyarta ta shiga mata ɗaci, wanda ya zagayo har zuwa bakinta. Kuliyanta ?, Kuliya ya yi aure?, wai me Anti Karima ke faɗi ne?, anya ma kuwa tana cikin hayyacinta? Inna! Ba za ta saɓu ba, wannan zancen ƙarya ne, Kuliya na ta ne ita kaɗai, wata mace ba ta isa ta rabata da shi ba, babu wanda ya isa ya shiga tsakaminta da shi. Ba ta san ta fara hawaye ba, sai da Anti Karima ta dafata. “Kada ki damu Siyama, ko wace sh*giya ya aura za mu raba shi da ita, Kuliya naki ne ke kaɗai, dan haka ke kaɗai za ki same shi” Kamar wadda ta bada ajiyar hankalinta haka ta kalli Anti Karima, hawaye na mata zuba. “Anti Karima Wallahi ina sansa... Na rantse miki da Allah ina san Kuliya, na shiga uku ni Siyama! Yanzu wai Aliyuna ne ya yi aure?, Wayyo Allahna, Anti Karima... Anti Karima Ina sansa, I love him Anti Karima... I can't live without him, I can't, i can't...” Gaba ɗaya ta fita hayyacinta, sambatu kawai take tana ƙarawa. Anti Karima ta rungumeta tana bubbuga bayanta. “Ba za mu rabu a su ba, dole sai mun rabasu!...”. Haka Siyama ta ƙarar da yinin ranar kamar mara lafiya, kuka kam ta yi har ta gode Allah. Sai da yamma Anti Karima ta shirya dan zuwa gidan Anna, amma sai wayar Annan ta risketa kan ta yi zamanta ba sai ta zo ba, Kuliya yace zai je ya ɗauko matarsa da kansa. Tun daga lokacin ta riga ta tabbatarwa da kanta ba zata bar wannan auren ya ɗaure ba, sai ta ga bayan wannan auren, ta ko ta halin ƙa-ƙa. *No.234, Efab Estate, Gwarinfa, Abuja.* MISHAL POV. “A gidan Ub*n wa aka ɗaurawa jikar tawa aure?... Tukunna ma ub*n waye ya aurar da ita?!” Jadda kakarsu ce ke magana cike da masifa, a sa'ilin da Ammu Musa ke sannar musu da batun ɗaurin auren Mishal da aka yi, tare da faɗin wai ga mijinta nan ya zo ɗaukanta su tafi. Yau kwana takwas kenan da rasuwa Abubakar, gaba ɗaya ahalinsu na Maiduguri babu wanda bai zo gidan ba, haka aka yi zaman makoki aka share a jiya, sannan kowa ya koma Maidugurin, ban da Jaddan da ta ce ba za ta koma yanzu ba, sai Nimra wadda gidanta ke cikin garin Abuja. To yau ma ita da yaranta gaba ɗaya suna gidan. Mishal dake kwance a kan doguwar kujera ta miƙe zaune, ta na jin wani zance da ba shi da ƙafa bare kai, aure ?, wa aka yi wa auren wai ?, wai ita?, ita akawa aure?, ta na cikin sallalamin rasuwar ɗan uwanta za'a wani zo mata da batun aure?. Duk da ba wani sosai take shiri da yayan nata ba, amma tasan da cewa ya na santa, kuma yana yin duk wata hidima da za ta faranta mata, ba ta yi kuka ba a rasuwar tasa, amma ta shiga cikin ƙinci mara misaltuwa, don ko makaranta ba ta zuwa. Ammu Musa ya sunkuyar fa kansa a gaban matar kawunsu, sannan yace. “Aure Jadda, Abubakar da kansa ya bayar da auren Hafsat ga abokinsa Aliyu! Kuma wannan ɗaurin auren shi ne abu na ƙarshe da Abubakar ɗin ya nema kafin Allah ya amshi ransa!” Ba Jadda kawai ba, hatta da Nimra da kuma Hajjara sai da suka yi mamaki, amma me yasa babu wanda suka faɗawa batun auren har tsawon kwana takwas?. Tun da bakin Ammu Musa ya ambaci sunan Aliyu, zuciyar Mishal ta hasko mata fuskarsa, wannan fuskar me kama da ta Adawiyya, kazalika irin wannan fuskar da take ganin mamallakinta na yawan tsayawa a tsallaken makarantarsu, kenan shi aka aura mata ?, wai tsaya ma, ita Mishal akai wa aure ?, wai har nawa ma take ?, da za'a mata aure, aure fa?. “To Wallahi ba Abubakar ba, ko Muhammad ub*n Abubakar ne zai dawo duniya yau ba ku isa ba, nawa ma yarinyar take ?, duka-duka fa bata fi shekaru 16 ba, shi ne za ku cuci rayuwarta ku mata aure?” Anna ta faɗi tana miƙewa, kamar ta kaiwa Ammu musa bugu haka take ji. “A'a Anna, kin san dai Ammu ba zai miki ƙarya ba, dan haka batun auren nan an riga an ɗaura, kawai dai mu yi wa Mushal fatan alkari, tare da danƙata a hamnun mijinta, kinsan dai Abubakar ba zai taɓa aurawa Mishal mijin da bai dace ba” Cewar Nimar ta na miƙewa tsaye, Jadda ta juyo ta kalleta tare da wurga mata harara. “Ba ke ba, ko Fatima kakarki ba ta isa ta faɗa min haka ba! Kar ki ga ina sakar miki fuska, ki ɗuka cewar za ki iya kawo min raini Falmata, Wallahi ina iya ɓatawa da ub*n kowa a kan jikokina!...” Daga nan Jadda ta shiga buɗe musu wutar bala'i, ta inda take shiga ba tanan take fita ba, masifa kwando-kwando haka ta riƙa sauƙewa. Sai da Nimra ta kira escort ɗinta, waɗanda gomnati ta bata dan kariya, a matsayinta na general, kasancewar a waje suke suna jiranta ba ɓata lokaci suka shigo, cikin su har da yaranta biyu, Ijaz da Arman. Su suka saka bakin Jaddan yin shiru, ba dan ta na so ba a gaban idonta Nimra da 'yarta Iqra suka shiga ɗakin Mishal suka haɗo mata kayanta kaf. Sai da suka so shiryata ma, amma da suka duba kayan nata suka ga babu na arziƙi sai suka barta haka, dan Mishal ba atamfa ko leshi take sawa ba, ita dai barta da ƙanun kaya. Ita kuwa Mishal tun da aka fara wannan dambaruwa ta rasa gane kanta, ba ta ma fahimtar zancen da ake, dan zantukan nasu sun wa ƙwaƙwalwarta girma, wai yau ita aka yiwa aure, ita ɗin da take cewa ko da candy ta yi, ba za ta yi aure ba sai ta fara aiki, ga shi tun ba'a je ko ina ba har zancen ya warware. KULIYA POV. Tsaye yake a harabar gidan Abubakar, ya jingina da jikin motarsa, tunanika iri-iri na kai kawo a cikin kwanyarsa, shi kansa ba zai ce lafiyarsa ƙalau ba, dan yasan ba shi da lafiyar a irin halin da yake ciki. Kuma ba ya jin akwai maganin damuwarsa, komai ya masa duhu, ya kasa gane ainahin kan lamarinsa, shin farin ciki yake don ya samu wadda zuciyarsa ta gama tabbatar masa da sonta yake ?, ko kuma yana alhinin mutuwar amininsa, wanda ya sadaukar da rayuwarsa wurin ceton tasa rayuwar?. Ya kasa ganewa, ya kasa gane dai-dai da akasinta, ya kasa gane duhu da haske, ya kasa gane sarƙaƙiya da warwara. Ba ya fahimtar komai, ya na jin kamar rayuwarsa ce ke tangal-tangal a cikin kwale-kwalen katako, wanda ke tsakiyar tekun dake ambaliya... Tunaninsa ya katse, a sanda ya hangi mutane na fitowa daga cikin gidan, sojoji ne guda huɗu a kan gaba, kowannensu riƙe da akwati, sai mata uku daga baya, sun saka ɗaya tsakiyarsa, wadda yake da tabbacin ita ce Mushal

Table of Contents

Chapters

112 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112