Chapter 96
Chapter 96
san kalar hukuncin da zai musu. Kafin su shiga kotu “Sai yaushe kuma?” Cewar Zaid, yayin da motarsa ta yi parking a farkon lungun gidan su Rabi. Rabi da ta haɗe cikin wani kyakkyawan pink lace da bluen hijabinta ta juyo ta kalleshi. “Sai ka zo ɗauka na mana. za ka je wurin ɗaurin auren ne?” Ta tambaya tana ƙare masa kallo, dan kuwa yau ya fi mata kyau fiye da ko yaushe, sanye yake cikin wata brown color shadda, ga golden hular dake kansa, ya yi kyau kamar wani ango. Zaid ya ɗaga kafaɗarsa ta dama ya na gyaɗa mata kai tare da faɗin. “Insha-Allah. Daga nan ma ai can zan wuce, sai de an jima kawai” Ta gyaɗa masa kai tana shirin fita daga motar, caraf Zaid ya riƙo hannunta. “Tafiya za ki yi ba tare da kin min...” Dukan ta kai masa a baki, ya kaucewa ya na dariya. “Wai ni ko me zan yi sai an dake ni?” Rabi ta watsa masa harar wasa. “Idan baka so ina dukanka ka dena rashin kunya” Ya buɗe baki yana kama haɓa. “Ni ne ban da kunyar?” “To kunyar ce da kai?” “Allah kuwa Ammata ina da kunya sosai, kowa yana darajanta ni, kowa yana bani kima, ina da kwarjini a idon mutane. Kuma duk da haka sai ke ki ce ba ni da kunya?” “To idan baka so ina faɗa maka haka ka dena min irin waɗana zantuttukan” “Wasu zantuttuka ke nan?” Ya tambaya cikin ɗage gira, har da mata alama da hannu, Rabi ta ja tsaki, dan ta lura da yau 'yan neman tsokanar ne a kusa, gwara ta rabu da shi ta yi tafiyarta. “Kin ɗau ba shi, idan muka koma gida sai na fanshe da...” Wani dukan ta ƙara kaiwa bakinsa amma sai ya dafe bakin nasa yana dariya. “Yi haƙuri damisar Raja, takawarki lafiya uwar gidan Zaid, maman Aliyu da Maryam!” Baki sake Rabi'a take kallonsa, wato ita nan har an gama zaɓa mata sunan 'ya'yan da zata haifa?. Kuma maganar tasa sai ta tuno mata da shi, Aliyu, mijin Mishal, ɗan uwansa. Ya kamata ace zuwa yanzu ta san meke faruwa a tsakaninsu, amma ba komai za ta tambaya. Motar ta buɗe ta fita, har ta shige lungunsu Zaid na mata dariya, nan duniya babu abun da ke sashi mishaɗi face zolayarta, in dai zai zolayeta sai ta yi fushi, shi kuma fushin nata me ke mugun aika shi duniyar nishaɗi. Motar tasa ya tayar ya yi gaba, dan masallacin da za'a ɗaura auren a gaba yake. Bayan an ɗaura aure, ya yi wa Abba da Fu'ad barka, ya basu uzurin akwai aikin dake jirans, sannan ya samu ya sulale ya gudu. Gida ya koma ya je ya shirya cikin suit, kai tsaye daga nan ya nufi DSS headquarter. *DSS Headquarter, Maitama Evenue, Abuja.* “Sun yi bayani?” Muryar Zaid ta tambaya, yayin da yake tsaye ya na kallon Usman da abokansu huɗu dake cikin ɗakin horo. Duk sun fita hayyacinsu, dan ba ƙaramin duka suka sha ba. Matemakinsa ya amsa masa da. “A'a Sir, sun ƙi yin magana” Ya juyo ya ɗauke idonsa daga kan glashin da yake iya kallon su Usman ta ciki, ya kalli matemakin nasa me suna Marcus. Sannan ya juya ya kalli Rhoda dake tsaye a ɗayan gefen nasa. “Shi kuma Alhaji Balan fa?” Rhoda ta amsa masa da. “Ya magantu, bugu ɗaya ya ji ya saki baki ya shiga koro bayanai” Kannsa ya gyaɗa yana ci gaba da kallon su Usman, hannayensa rungume a ƙirjinsa. “Ina Joseph?” Ya tambaya ba tare da ya kalli ɗaya daga cikinsu ba, Marcus ne ya amsa masa da. “Sun fita wani aiki...” Bai jira Marcus ɗin ya gama rufe bakinsa ba, ya fara takawa zuwa ƙofar shiga cikin ɗakin horon. Rhoda ta girgiza kanta, dan ta san ba zai ragawa su Usman ba. Ilai kuwa, ya na shiga ya bi ɗakin da kallo, zaratan mazan dake tsaye a ɗakin hannayensu riƙe da sandunan duka suka sara masa. Ba tare da ya amsa gaisuwar tasu ba ya kalli sandar dukan hannun guda daga cikinsu. “Da wannan kuka dake su?” Ya tambaya yana raba idonsa a kansu. Ɗaya daga ciki ya amsa masa da. “Yes sir” Hannun rigarsa ya shiga tattarewa ya na faɗin. “Ina kwa za su yi magana. Wannan ai ba duka suka sha ba... Marcus!” Ya ƙarashe yana ƙwalawa Marcus dake tsaye a waje kira. Da hanzari Marcus ya shiga ɗakin yana amsa kiran. ”A kawo min lantarki!” Cike da iko isa da jzza ya yi maganar, ta yanda babu wanda ya isa ya tanka masa a cikinsu. Marcus ya ammsa yana fita. Shi kuma Zaid ya ja ɗaya daga cikin kujerun ɗakin ya zauna a yana facing su Usman, waɗanda suka jigata sosai, dan ko ɗan yatsa babu wanda ya isa ya ɗaga a cikinsu. Jim kaɗan Marcus ya dawo da wata na'ura, shi da kansa ya jonata a ɗakin, sannan ya miƙawa Zaid wasu abubuwa guda biyu, masu suffar biro, waɗanda ke jone jikin wannan na'urar da ya jona. Yana kallon Usman ya miƙa hannunsa ya karɓa. Sannan ya karawa Usman saitin ƙirjinsa, wata zabura da Usman ɗin ya yi ce tasa sauran ma dawowa cikin hayyacinsu, karkarwa yake kamar wani me farfaɗiya, ga bakunansu a kulle, babu damar magana, ihun ma ba sosai ake jiyowa ba, babu ko ɗugon tausayi haka Zaid ya ci gaba da zona masa shocking ɗin nan a jikinsa, dan babu abun da yake hangowa a idonsa face Rabi'a, sanda ya sameta kwance a gadon asibiti, sai kuma hoton result ɗinta da Huzaifa ya danƙa masa. Kan kace wani wani abu Usman ya suma kusan sau huɗu, sai da ya kusan aika ɗan mutane lahira kafin ya ƙyaleshi, ya dawo kan Jaz, dake kusa da kujerar Usman ɗin, haka ya yi ta gana masa tasa azabar. Sauran tun kafin a zo kansu suka fara shan jinin jikinsu, J boy harda fitsari a wando. Bai ƙyalesu ba saida ya ɗanɗanawa ko wannensu, sannan ya sa aka kawo masa kyakkyawan madoki, ya shiga dukansu yana ƙarawa, saboda gaba ɗaya zuciyarsa ta bushe, ba ya jin ko ɗigon tausayinsu, don suma ba su ji tausayin Adawiyya ba sanda za su haike mata. Ganin Zaid niyyar kashesu yake ya sa Rhoda saurin shigowa cikin ɗakin tare da faɗin: “Ya isa haka Zaid...!” Cak sandar da ha ɗaga dan bugawa Usman a ka ta tsaya a iska, dan niyyarsa ita ce ya masa wani kyakkyawan bugu a tsakiyar kansa, wanda zaisa ya tuno da auren uwarsa. Dan duk cikinsu ya fi jin haushin Usman, saboda shi ya fi kowa irin wannan halin zalincin a cikinsu. A fusace ya cillar da madokin yana huci, idanuwansa sun firfito waje, ya danne haƙwaransa na ƙasa da na saman, kallonsa kawai idan mutum ya yi sai ya bashi tsoro, dan shi sam bai iya fusta ba. Kafaɗarsa ya ɗaga yana sharce gumi. Baya ya juya musu baya yana maida numfashi. Ganin kamar Usman na san magana ya sa Rhoda isa gareshi cikin hanzari, tare da buɗe masa bakinsa. Idanuwansa ya lumshe yana buɗewa, dan sam baya cikin hayyacinsa, ya jikkata sosai ba kaɗan ba. “Wallahi... Mu... Mu ne... Mu... Ne muka... Muka mata
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112