Chapter 13
Chapter 13
da ƙaninsa, ɗan uwansa abokin tagwaitakarsa. Sai ku ma Maman Rhoda, wata mace da ta taka rawa mai makuƙar muhimanci a cikin rayuwarsa. Wani irin wahallallen nunfashi ya ja, ya samu kansa cikin irin yanayin da ya saba shiga a duk sanda zai ga wutar. Duk da yanda yake ta kokawa da tunaninsa kan kada ya koma baya, amma sai hakan ya ci tura. LABARINSA na baya ya soma kunno kai cikin nazarinsa. _“Zaid, ku tafi, kada ku tsaya a nan.....idan kuka tsaya wutar za ya iya ƙona ku....ku tafi na ce!.....” _ Amon wannan sautin nata ya shiga maimaita kansa a cikin tunaninsa, falon ya shiga rikiɗewa yana komawa gidansu, gidan da suka rayu a ciki, gidan da suka ci gaba da kwana a cikinsa har bayan sanda wuta ta gama ɗaita shi, wannan gidan da suka gina yarintarsu shi da ƙaninsa a ciki. Sannan hoton ya sauya a idonsa, ya na ganin yanda take watso musu kayansu ta window, yayin da ƙofar falon take a kulle, ta kasa fitowa bare ta buɗe ƙofar har ta samu damar tsira. Sannan ya kallin kansa da ma ƙaninsa Aliyu dake ta kuka, ƙaninsa me tsantsar kama da shi, dan idan suka kalli juna sai ka ce kansu suke kallo a madubi. Dan kammanin da suke ya ɓaci, tsayinsu ɗaya, farar fatarsu ɗaya, girman idonsu ɗaya, komai na hallitarsu ɗaya ne, in ka ɗauke ƙwayar idon Zaid da ta kasance ash, sai kuma totsiyar karen dake haƙorin Zaid ɗin. Amma hatta wata ɗabi'a ta ɗaga kafaɗa dukaninsu suna yi. “Jagwado menene haka ?, Sarai ka sani cewar Raja ba ya san ganin wuta!” Muryar Rhoda da ke wa Jagwado faɗa ta dawo da shi zahiri. Bai ƙara ce musu komai ba, ya miƙe tsaye, tare da ɗaga kafaɗarsa ta dama, ya yi ɗakinsa, yana jin yanda Rhodan ta balbale Jagwado da faɗa, shi kuma sai aikin bata haƙuri yake. _________________ _To fa.... Bana kuma nan muka leƙo?_ _Na ce ba, wai Rajan ne ko Zaid ne?_ _Dan ni na kasa ganewa, kamar Zaid da Aliyu mutum ɗayane, kamar kuma....._ _Ko da yake, ba sai na faɗa ba ai😂_ #Labarinsu #SalmaAhmadIsah #Taurariwriters °°°°°°°°°°°°°° *LABARINSU* *©SALMA AHMAD ISAH* *TAURARI WRITERS* *04* ~~~ _-*What she really craves is a wild love, from a steady pertner...*-_ *** *1987* Alhaji Ali Wakili, babban mutum ne me tarin arziƙi. Haifaffen garin haɗejia ne, kuma ya ci gaba da zama a cikin garin har bayan lokacin da ya fara tara iyali. Kasancewarsa mutum me nasibi a harkokin kasuwancinsa, ya sa shi gyara gidansu na gado, ya ci gaba da zama a ciki shi da 'yan uwansa. Alhj Ali na da mata biyu, hajiya A'i, yaransu tara da ita mata biyar maza huɗu, matan sun haɗa da Lawisa, Fatsima, Kaltume, sai 'yan biyun gidan, Maryam da Rabi'a, Mazan kuma sun haɗa da, Abdullahi, wanda ya kasance shi ne na farko, sai Mansur, Haladu da lawan Hajiya Kande ita ce matarsa ta biyu, yaranta huɗu da shi, kuma dukansu maza ne, Kabir, Sagir, Jamilu da kuma Jibrin. Duka yaran gidan suna karatu, matansu da mazansu, kuma duk da kasan cewar sun taso a gidan yawa, akwai zaman lafiya a tsakanin yaran ahalin, dan iyayensu jajirtattu ne a kan tarbiyar yaran nasu. Rana ɗaya da gaba ɗaya ahalain gidan ba zasu manta da ita ba ta kasance Asabat, inda labari ya riske su cewar an yi wa Rabi'a 'yar biyun Maryam fyaɗe. Duk wani nau'i na tashin hankali babu wanda bai yi ba a gidan, dan da aka tambayeta ta shin san wanda ya mata fyaɗen?. cewa ta yi bata sani ba, dan hankalinta a gushe yake. Haka aka gama jajjaɓin lamarin kafin aka watsar da zancen, kowa ya ci gaba da lamuransa. Bayan kwanaki da faruwar lamarin, Alhj Ali ya nemawa Maryam gurbin karatu a garin Suleja, dan haka ta tafi can ta ci gaba da karatunta. Watanta ɗaya da tafiya, alamun samuwar ciki suka fara bayyana tattare da Rabi'a. Tun tana ɓoye abun har ya zo ya bayyana, har kowa na gidan ya sani. Alhaji Ali ya yi tsallen albarka ya ce sai dai a zubar da cikin. Itama kuma Rabi'a ta yi tsallen albarka kan cewar ba za ta zubar da cikin jikinta ba, hakan yasa shi kuma yace sai de ta bar masa gidansa. “In dai har ba za ki zubar da cikin jikin ba sai dai ki bar min gidana Wallahi!...” Haka ya faɗi, a ranar da yake watso mata kayanta ƙofar katafaren gidan nasu. Gaba ɗaya mutanen gudan sun firfito, an tsaya a bakin gate ana kallon abin da ke faruwa. Babu yanda yayun Alhaji Ali ba su yi da shi ba kan ya yi haƙuri, amma ya ce Wallahi sai Rabi'a ta bar masa gidansa, dan baza'a haife cikin shege a gidansa ba. Ba zata ɓata masa sunan zuri'a ba. Rabi'a ta tsugunna ta tattare sauran kayan da Abban nata ya watso mata, sannan ta haɗe su a wuri ɗaya, tana ta sharar hawaye. A hankali ta miƙe ta kalli idon Abban nata. “Da na zubar da cikin jikin, gwara na bar maka gidanka Abba.... Ba zan roƙi ka bar ni na zauna a gidan ka ba, abinda ya sameni ƙaddara ce daga Allah, kuma shi ne zai temakeni na iya cinyeta.....Ni dai buƙa tata ita cee ka yafe min Abba!....” Ta ƙarashe tana fashewa da kuka, babu wanda bai ji tausayinta ba a wurin, amma banda Alhaji Ali, wanda ya kawar da kansa gefe, ya gwammace da ya sallamarta, da ta ja masa a bun kunya, ace yau a gidansa aka haifi ɗan gaba da fatiha?, kuma ace 'yarsa ce ta cikinsa?. “Na san ba lalle ka yafe min ba, amma ni dai ina meneman yafiyar taka, zan yi nesa da kai, zan yi nesa da gida, zan je na haife cikin jikina, kuma zan basu labarin abinda rayuwata ta fuskanta sakamakon fyaɗen da aka min ba tare da san rai na ba...Yaran da aka haifesu ba tare da aure ba suma 'ya'ya ne, ƙaddara ce ta hukunta zuwansu ba tare da auren ba!...” Ba tare da ta sake cewa komai ba ta ɗauki sauran kayanta tana ta sharar hawaye, ta kama hanyar barin unguwar tasu. Sai da ta yi tafiya mai nisa, sannan ta ji muryar mahaifiyarta na ƙwalla mata kira. Cike da mamaki ta juya. Da gudu ta ruga wurinta tan kuka, suna haɗewa ta faɗa jikin mahaifiyar tata tana sakin sabon kuka, Ita ma Hajiya A'in kukan take. Kafin ta share hawayenta ta ɗago da 'yarta. Hannunta ta kama sannan ta danƙa mata wata jaka. “Akwai kuɗi, da takardun karatunki a ciki, sannan akwai takardun gidana na kano a ciki... Ban ce ki faɗawa kowa inda za ki ba.... Ni dai ina so ki je ki kafa sabuwar rayuwarki a garin kano, idan zai iyu bayan kin haifi yaranki, ki yi aure Rabi'a!.....” Rabi'a ta ƙara faɗawa jikinta tana sakin sabon kuka. “Aure be dace da ni ba Mama, sanin kanki ne babu namijin da zai auri macen da ta yi ciki ba tare da aure ba” Hajiya A'i ta shiga kwantarwa da 'yarta hankali, tana haɗa mata da nasiha, har zuwa lokacin da suka yi sallama. sallamarsu ta ƙarshe kenan.
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112