Chapter 36
Chapter 36
“To ki sanar mata da ku yi maza-maza ku taho International Hospital, Abubakar ba lafiya!...” Duk rashin hankalinta, da ƙarancin shekarunta a duniya ta san cewa jinya kawai ba za ta saka babban mutum kamar Ammunsu kuka ba, dole akwai wani abu dake faruwa da yayanta mara kyau, kk mutuwa ya yi ?!. RABI'A POV. Kamar yanda ta saba ganinsa jingine jikin gate ɗin estate ɗin nan, yana kallonta da lumsassun idanuwansa. Yau ma haka ɗin ne. A memakwan kullum da ta saba wucewa ba tare da ta masa magana ba, yau sai ta ɗago masa hannu, sannan ta yafito shi. Sai da gaban Raja ya faɗi, ganin yanda ta kira shin, amma sai ya dake, ya fara takawa zuwa gabanta. A lokacin da ita kuma ta hau hanya ta fara tafiya, kamar jiya sai ya fara binta a gefe. “A can kake da zama?” Bayan ɗan wani lokaci ya ji ta tambaya. Sai ya ɗaga ƙafaɗarsa ta dama sannan ya amsa mata da. “Eh, a nan nake da zama” “Wannan ɗayar ƙanwarka ce ?” Ta kuma tambaya, hakan yasa ya kalleta kaɗan, wato jiya shi ya mata tambayoyi, yau kuma ita ce ke masa. Kafaɗarsa ya ɗaga cikin faɗin: “Sunanta Rhoda, kuma ƙanwata ce” Rabi ta gyaɗa kanta tana kallon hanya. “Kai ma Cristian ne ?” Sai da ya ɗan tsaya ya kalleta na 'yan wasu sakkani, sannan ya ci gaba da tafiyar. “Ni musulmi ne” “To miye ma'anar RAJA ?!” Ta tambayi abin da ke mata yawo a ka tsawon lokacin da ya faɗa mata sunansa. Bisa ga mamakinta sai ta ji ya yi murmushi, hakan yasa ta juya ta kalleshi, murmushin kuwa yake, wanda ya ƙara bayyana kamarta da shi. “Raja na nufin Fata, i mean wish, za kuma ki iya kiransa da hope, amma sunana na gaskiya Zaid ne!” Zaid?!, Zaid!?, Zaid?!... Ta maimaita sunan kusan sau biyar a cikin ranta, to Zaid ɗin bai fi ba?, amma ya na wani kiran kansa da Raja. Sai ta tsaya a sanda suka fito bakin titi. Kamar jiya yau ma sai da ya tsaida mata taxi, sannan yace kada a ɗau kowa sai ita. Daga haka ya ɗaga mata hannu, ya koma layin da ya fito. Rabi ta yi murmushi tana kallon hanya. Hirarta da shi na sa ta nishaɗi sosai. *No. 213, Naf Belly Estate, Asokoro, Abuja* KULIYA POV. A hankali ya sako ƙafarsa ta dama cikin falon gidan Anna, wadda take zaune a kan kujera tana tsige zogale. Kanta ta ɗaga ta kalleshi. Ba shiri ta miƙe tsaye, hakan yasa trayn zogalen dake kan cinyarta kifewa a ƙasa, zogalen ya zube. Ba komai ya bata tsoro ba, sai ganin yanda idanuwan Kuliyan suka yi ja, fuskar tasa ma ta yi ja, bisa ga dukkan alamu kuka ma ya yi. Suna haɗa ido da ita ya fashe da kuka, ba ƙaramin razana Anna ta yi ba, sanin halin ɗan da ta rena, Kuliya ba ya kuka a kan abu ƙarami, idan har ka ga ya yi kuka, to abun ba ƙarami ba ne, ita za ta iya cewa ma tun ranar da ta dawo da shi Abuja har wa yau bata taɓa ganin kukansa ba. Da sauri ta ƙarsa kusa da shi, kuma tana zuwa kusa da shi ɗin ya rungumeta yana fashewa da kuka. Anna ta ja hannunsa ta zaunar a kan kujera bayan da ya saketa, da gudu ta shiga kitchen ɗinta, ta ɗauko ruwan sanyi ta ba shi. Sannan ta zauna a gefensa tana shafa kansa. “Me ya sameka Aliyu?” Kuliya ya aje gorar ruwan da ya shanye kusan rabinta, sannan ya share hawayensa. Yana kamo hannun Anna. “Ba na faɗa miki cewar yau za mu fita kame ba ?” Ya faɗi cikin wata murya mai rauni, wadda za ta iya cewa sam ba ta san ɗan nata na da ita ba.Da sauri ta gyaɗa masa kai tana shafa kansa. “To a wurin ne... Ɗaya daga cikin 'yan ta'addan ya yi ƙoƙarin harbi na, shi... Shi ne Abubakar abokina, ya ture ni... Shi... Shi kuma harbin ya same shi!” Annan ta gyaɗa kai, dan tasan Abubakar ɗin. “To yanzu me ya samu Abubakar ɗin ?” Ya haɗiye yawu yana share hawaye. “Shi ne muka kai shi asibiti... Bayan an masa tiyata an cire alburushin... Yace a kira masa kawunsa... Ni da kai na... Na kira kawun nasa, na yi masa kwatance, ya zo ya samemu har asibitin...” Ya kai hannu yana share hawaye, sannan ya ci gaba. “To Kawun nasa na zuwa, yace yana so a ɗaurawa ƙanwarsa aure kafin ya rasu... Da kawun nasa ya tambayeshi waye mijin... Sai... Sai yace ni ne, cewa ya yi ni ne Anna!” Ya ƙarashe a raunane. Anna da ta fara fahimtar inda zancen ya dosa, ta share masa hawaye ta na masa alamun ta na jinsa. Sai da ya ja hanci sannan ya ci gaba. “Yanzu haka an ɗaura mana aure da ƙanwar tasa, Anna wani irin so Abubakar yake min?, da har zai iya kasada da rayuwarsa ya ceci tawa, sannan ya aura min ƙanwarsa da yake ganin ita kaɗai ce ta rage masa!” “Kana da zuciya me kyau Aliyu, duk da kana da saurin fusata, ni nasan kana da kyawawan halayen da za'a so a tare da ɗan adam na gari... Yanzu ina Abubakar ɗin?” Annan ta tambaya tana ƙara share masa hawaye, bisa ga mamakinta sai ta ga ya kwantar da kansa a kafaɗarta yana fashewa da kukan da ya fi na ɗazu, a hankali ya ɗaga kafaɗarsa ta dama. “Anna Abubakar ya mutu!, Muntuna biyar da gama ɗaurin auren ya mutu!, Anna kuma bai mutu ba sai da ya kama hannuna, sannan yace na kula masa da ƙanwarsa, kada na bari ta wahala, Anna ina zan kai wannan nauyin?, Ina zan kai nauyin da ya ɗora min?!” Anna ta rintse ido, a sanda take jin sauƙar hawayensa a kan jikinta, da ƙyar ta daure ta ci gaba da shafa bayansa. “Allah zai temakeka Aliyu, shi kuma Abubakar Allah ya ji ƙansa, ya sa mutuwar ita ce hutu a gareshi, Allah ya baku zaman kafiya da matarka, ya kauda idomln maƙiya daga kanku!...” #Labarinsu #SalmaAhmadIsah #TaurariWriters ••••••••••• *LABARINSU* *©SALMA AHMAD ISAH* *TAURARI WRITERS* *10* ~~~ *Do something for her that no one has ever done, love her for who she is.* *** *Shekara ta 2000.* “Malam Ila ina kwana” Cewar Zaid yana tsugunnawa har ƙasa, a sanda ya shigo shagon Malam Ila, wanda ke saida kayan provision a 'yar ƙaramar containerrsa. Baki washe Malam Ila ya amsa masa, kafin Zaid ya miƙe ya zauna a kan bencin da Malam Ilan ke kai, suka kuma gaisawa, kafin Malam Ilan ya ba shi abincin da ya siya ya aje masa, kamar yanda suka saba kullum. Don a kwanakin kullum idan ya zo sai ya ba shi abinci, karɓa ya yi sannan ya ci, suna 'yar hira jifa-jifa. Kuma a cikin hirar ne Malam Ilan ya sosawa Zaid inda ke masa ƙai-ƙayi. “Ya kamata ka je ka dubo ƙanin naka, ka ga fa yau kusan satinsa ɗaya a can!” Aliyu ya aje kwanon hannunsa sannan yace. “Ai wai kar su ga gaggawata ne shi yasa, amma ina kewarsa, don ba mu taɓa nisa da juna irin
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112