Chapter 103
Chapter 103
ta koma kamarwata wadda sanyi ya taɓawa ƙwaƙwalwa. “Kana ji ko?!” Ta tambaya tana mammarin gefen fuskarsa, idonsa da ya lumshe ya buɗe a kanta. “Kar ka mutu baka haɗu da Zaid ba!...” Kuliya ya ja wani kalar numfashi yana buɗe idonsa da ƙyar, cikin wani irin sauti yace. “A... Ina... Ki... Ki ka san... Za... Zaid?” Ba dan babu sautin komai a ɗakin ba, da balalle ta ji abun da yake faɗi ba. “Yau Anti Adawiyya ta zo makaranta ta same ni, shi ne take faɗamin cewar Zaid ne mijinta, kuma... Kuma da ma ina ganinsa a layin makaranta” Kansa ya kawar gefe yana ƙoƙarin ƙwato numfashinsa da ya nufi wata duniyar. “Zaid ya gudu... Gu... Guduwa aka ce ya y... yi” Da sauri Mishal ta share hawayenta, hakan ya sa gefen fuskarta ɓaci da jinsa. Ta gyara zama ta shiga ba shi labarin da ta sani a kan Zaid ɗin. Duk kuwa da ba ta da tabbacin yana fahimta. Sai de kuma yana fahimtar, dan babu abu ɗaya da ta faɗa wanda bai samu mukkulin kansa ya buɗe ƙofa ya shiga ba, ya ji komai, kuma ya haddace komai. Kallonta yake da idanuwansa da suka kusan lumshewa gaba ɗaya. “Hafsat! Ballale... Na... Na kai gobe ba... Amma idan... Idan kin haɗu... Haɗu da Zaid, ki ce... Ki ce masa ina kewarsa... Sa... Sannan... Sannan kuma ba duk tswon wannan lokacin, ban manta da shi ba... Ki kuma faɗa masa cewar... Cewar ke matata ce, ya kula min dake!” Mishal ta ƙarawa kukanta sauti tana kamo hannunsa. “Aliyu Dan Allah ka dena faɗin haka... Na rantse za ka rayu, Allah na tare da mu... Yanzu Aliyu idan ka mutu ina zan sa kain?... Aliyu ba ni fa da kowa sai kai. Kai ne kawai ka rage min, dan Allah kai ma ka zauna, kar ka mutu ka barni kamar Babana da Mamana da kuma yayana, a ƙalla de ya kamata ace na samu ko da mutum ɗaya ne a cikinku!” Tausayinta ya ƙara kama raunanniyar zuciyar Kuliya, hakan ya sa shi ɗagowa da hannunsa na hagu dake ɓace da jini, ya kama gefen fuskarta, hannun nasa gaba ɗaya karkarwa yake, hawaye na fita daga idonsa, wanda ya haɗe da zufar da yake. Matsowa ya yi da fuskarta dab da tasa, har tana iya jiyo yanda numfashisa ke fita a gurɓace, saboda hancinta da ya kara da nasa, hakan ya sa Mishal lumshe ido tana buɗe wani sabon babin na kuka. “Idan na mutu kar ki yi kuka, na san ma Zaid ba zai bari ki yi kukan ba, amma zan yi kewarki, Allah ya haɗani da ke a aljanna!...” Da sauri Mishal ta kai hannayenta kan fuskarsa tana girgiza masa kai. “Dan Allah kar ka tafi... Allah ina sonka... Wallahi ina sonka” Cikin wani irin ƙarfin hali ya mata murmushi. Da gaske yake faɗa mata cewar ba ya jin zai iya kaiwa safiyar gobe, ba ya jin zai iya ci gaba da rayuwa da ita, haka kuma ba ya jin zai ƙara buɗar idonsa ya ganta kusa da shi. Wasiyya ce yake bata, dan wata ƙila bai sani ba, ko wanna ne kaɗai lokacin da Allah ya ara masa dan ya yi magana da ita ta ƙarshe. “Silly girl... Ki me... Me da hankali kan karatunki, ki zama yarinyar kirki, idan kuma Allah ya sa akwai rabo tsakanina da ke, Allah ya raya mana shi, dan ina zaton kamar na baki baby shekaran jiya, ki kula da shi pleace” Duk da halin da yake ciki sai da ya bawa Mishal haushi, ana ga yaƙi shi ya na ga ƙura, ɗan ƙaramin mari ta masa a kuncinsa, hakan ya sa ya buɗe idonsa da ya lumshe. “I love you Teddy Bear... Mishallyn Aliyu...!” Da sauri ta haɗe bakinta da nasa ta shiga kissing. Kafin a hankali ta saki bakinsa tan kallon idonsa. “I love youuuuu too Abu Aswad!” Murmushi ya mata, yana ɗaga hannunsa ya shafa kanta. Nan take kuma jikinsa ya saki, hannun nasa ya dawo ƙasa yaraf, fuskarsa dake hannunta ta ƙara nauyi, idonsa ya rufe ruf. Daga can wajen gidan kuma, bayan da 'yan ta'addan da suka zo ɗaukar fansa suka gama dube-dubensu a cikin gidan ba su ga kowa ba, sai suka yanke shawarar kiran ogansu dan su sanar masa da su fa basu ga kowa ba. Ogan yace su bar gidan kawai tun da har sun ce sun harbe shi, ko haka ma suka barshi ai shikenan, sun ɗau fansar abin da ya musu, na kama babban ogansu da ya yi. ZAID POV. Da misalin ƙarfe 12:40am, ya fice daga gidansa, yayin da ya bar Rabi kwance tana bacci, shi ba zai iya jira har zuwa gobe da safe ba, dan tun bayan da ta kawo masa maganar Aliyu na raye ya shiga mata tambayoyi a kan Aliyun. Amma sai ta ce masa ita ba ta san komai a kansa ba bayan inkiyarsa, wato Kuliya, sannan kuma ta san cewa ma'aikacin DSS ne. Yanzu haka tafiyar da yake a motar, tunani, ruɗani, jimami da mamaki su ne suka cika kansa taf. Ya rasa ma wani kalar yanayi yake ciki, amma idan ya duba wani ɓangaren sai ya ga cewar kamar mamakin da yake ciki ya fi yawa. Dan ya na mamaki mutuƙa, na yanda Aliyun ya iya tserewa wutar da ta kama a gidan marayu, sai kuma mamakin sanin cewa shi ma SS ne, su na aiki a hukuma ɗaya, amma ba su san juna ba. Sai kuma wani murmushi ya suɓuce masa, tunawa da ya yi da alƙawarin da suke yawan ɗaukawa juna, na idan sun girma aikin SS shi ne za su yi. Wato bai manta ba kenan, tun da ga shi ya cika alƙawari. Hannunsa ya kai ya ɗauki wayarsa, a sanda yake faka motar a gefen hanya. Cikin jerin gwanon lambobin dake wayarsa, ya nemo ta RAM, tare da aika masa kira. Kusan ringing uku ta yi ba tare da an ɗaga ba, har ransa ya soma ɓaci, dan ya san halin RAM ɗin, shi a rayuwarsa sam bai iya zama da waya ba, wayat ma sam ba ta gabansa, mutumin da sai ya yi sati ba tare da ya san inda wayar tasa take ba. Sai a kira na biyar sannan ya ɗaga. Cikin magagin bacci ya soma gaida Zaid ɗin, ya amsashi a dake. “Ina san ka buɗe bayanan ma'aikatan hukumarmu, ka duba min wani wai shi ALIYU ZAID, inkiyarsa KULIYA!” Umarnin ya biyo baya. Daga ɗayan ɓangaren Ram ya miƙe tsaye daga kan gadonsa yana fita daga ɗakinsa, gudun kada ya tashi matarsa a bacci, ya koma falo ya zauna, har zuwa lokacin wayar na kare a kunnensa. Sai da ya murza idonsa kusan sau biyu, kafin ya sosa wuyansa, dai-dai kan wani tatto dake rubuce a wuyan nasa. “Sir a yanzu ba zai iyu na duba bayanan ba, sai de na datsi na'urar, amma ni zan iya baka amsa!” Daga ɗayan ɓangaren Zaid ya gyara zamansa ya na ɗaga kafaɗa. “Umhumm, Ina jinka” Ram ya ɗauko numfashi, sannan ya dire, dan kuwa ya san abun da zai aikata a yanzun, saɓawa ƙa'idar aikinsa ne, ba'a yarda su bawa juna sirrin wasu jami'an ba, amma kuma dole ne
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112