Chapter 37
Chapter 37
haka ba... Tazarar awa ɗaya ne tsakanina da shi a haihuwa, kuma bayan wannan tazarar ba mu sake samun wata tazara ba... A ko da yaushe muna tare” Cike da tausayawa Malam Ila ya girgiza kansa. “Ka ga abun da za ayi shi ne; zuwa gobe sai muje mu duba shi ko?” Cike da zumuɗu Zaid ya ɗagaa kafaɗarsa. “Allah ya kaimu goben, na gode Malam Ila, Allah ya saka maka da alkairi...” Washegari da sassafe Zaid ya dira a ƙofar shagon Malam Ila, ko fitowa ma bai yi ba, haka ya zauna ya na jiran fitowar Malam ilan. Sanye yake da wani farin yadi, wanda Malam Ila da kansa ya bashi, don yace ba ya san ganinsa da wannan uniform ɗin. Kana ganin kayan za ka san cewa ba nasa ba ne, saboda yanda kayan ya masa yawa. Ya na zaune a wurin har Malam Ila ya fito, babu yanda be yi da Malam Ila kan su wuce gidan marayun katsaye ba. Amma Malam Ilan ya dage kan sai ya sai masa abinci ya ci tukunna. Hakan kuwa aka yi, sai da ya sai masa abincin ya ci ya yi taf, sannan suka kama hanyar gidan marayun. “Bawan Allah, Lafiya kuwa na ga kamar gidan marayun nan a kulle, kuma na... Na ga kamar ma gobara aka yi!” Cewar Malam Ila a kiɗime, hankalinsa ya yi wata mummunar tashi, bayan da suka iso gidan marayun, suka ga gate ɗinsa a kulle, kuma ko daga bakin gate din za ka gane cewa an yi gobara a wurin. Mutumin da Malam Ila ya tambaya ya kalle su. “Kwana huɗu kenan da wuta ta kama a gidan, kuma babu wanda ya fita da ransa daga gidan!...” Iyaka abinda Zaid ya iya fahimta kenan a zancen nasa, bai san sanda ya yanke jiki ya faɗi ba. Kwanansa uku a asibiti kafin ya farfaɗo, kuma da ya tashi farfaɗowar ma ba a hayyacinsa ya farka ba. Abubuwa ya riƙa yi kamar wanda ya samu taɓun ƙwaƙwalwa, sai zantuka yake barkatai, an kasa gane kansa. Ganin abun ba na ƙare ba ne ya sa Malam Ila ɗauke shi daga asibitin, don ya ga abun ba na asibiti ba ne. Tashin farko gidansa ya kai shi, amma matarsa tace fafur ba za ta karɓi tsinttaciyar mage ba. “Wa to kai ga ka juju ko?, Ub*n yaye-yaye, to Wallahi ba za ta saɓu ba!, a ina zan saka wannan gardin ƙaton?, A gida ɗaki ɗayan?, Ga ka, ga ni, ga 'ya'yana, to Wallahi Malam da sake!” “Haba Gambo, be kamata kike faɗin haka ba, yaron nan na faɗa miki cewar maraya ne, idan ba ki manta ba; babarsa ce ta ba ni kuɗin da na miki yankan sunan Audu...” “Wallahi ba ka isa ba, wato dan kawai uwarsa ta ba ka kuɗi ka sai mana ragon suna, sai na karɓi ɗanta ko ?, na rantse maka da Allah wannan yaron ba zai zauna min a gida ba!” Duk da Zaid ba ya hayyacinsa sosai, amma yana iya tuna yanda matar kewa mijinta masifa da bala'i, ya na iya tuna yanda ta haƙiƙance kan ba zai zauna da ita ba. Tun bayan da ya fuskanci cewa Aliyun da ya rage masa ya bar duniya, rayuwarsa ta shiga halin ƙaƙa na ka yi. Ya ji gaba ɗaya ya gaji da duniyar, babu abun da ya fi buƙata sama da mutuwar shi ma, ya ji cewar yana son ya mutu kamar Momma da Aliyu, tun da da ma su ne kaɗai gareshi, to ga shi ya rabu da su, to ina zai sa kansa?. Ba dan Malam Ila ya so ba, sai dan babu yanda zai iya, ya ɗauki Zaid ya mayar da shi gidansu na da, amma kullum sai ya kawo masa abinci da ruwan rubutun da yake karɓo masa a gun wani malami mai almajirai da yasa a yi masa, don ya temaka masa wurin dangana da halin da ya shiga ciki. Safe, rana, dare, ba ya taɓa tsallakewa, har takai ga Zaid ɗin ya dawo hayyacinsa gaba ɗaya, amma yanayinsa da ɗabi'unsa duka sun sauya, ba ya son yawan magana, ba ya son fita, ba ya son shiga jama'a. Ya koma rayuwar ƙunci. Ƙarshe ma ya yanke shawarar barin gidan. Rana tsaka Malam Ila ya shigo gidan kawo masa abinci amma ya nemeshi sama ko ƙasa babu alamarsa. Ya ɓata ɓat! Kamar almara. Ranar da ya gudu cikin garin kano kawai ya bazama, ya kwana a titi, kafin da safe ya ci gaba da yawatawa. Har Allah ya kawo shi rumfar wata inyamura me ƙosai, sunanta Ebere, tana da marainiyar yarinyarta Rhoda, da mijinta ya mutu ya bar mata. Ganinta da Zaid na farko Allah ya saka mata tausayinsa, hakan yasa ta kira shi. “Menene sunan ka ?” Ta tambaya cikin gurɓattaciyar hausarta. “Zaid” Zaid ya amsa mata kansa a ƙasa. “Kai maraya ne ?” Sai ya girgiza kansa yana ɗaga kafaɗarsa ta dama. “Ni maraya ne, ba ni da kowa” Maman Rhoda ta waiga ta kalli 'yarta Rhoda dake zaune a raufar ta na wasa. “Za ka zauna da mu?” Zaid ya ɗago da kansa ya kalli matar, sannan ya kalli 'yarta, a take ya ga sun rikiɗa a idonsa sun koma masa Momma da Aliyu. Ba jayyaya ta amince mata, a ranar tare suka wuni a rumfar saida ƙosan nata, bayan dare ya yi ta ɗauke shi da Rhoda 'yarta suka tafi gidanta. Gidan ba wani babba ba ne, amma nata ne, kuma mallakinta, ɗaki ɗaya ta bashi tace masa ya yi zamansa, daga yau shi ma ɗanta ne, kuma ba ta hana shi yin addininsa ba, zai iya ci gaba. Tun daga wannan ranar Zaid ya yi sabin ahali, ga su dai ba musulmai ba, amma sun nuna masa karamci da hallacin da ya kamata a ce 'yan uwansa musulmai ne suka nuna masa. Maman Rhoda ta mayar da shi kamar babban ɗanta, Rhoda kuma ta ɗauke shi a matsayin wa, sai suka koma kamar 'yan biyu, duk da shi Zaid ɗin ya fita shekaru, amma hatta da kaya iri ɗaya suke. Maman Rhoda ta saka Zaid a makaranatar su Rhoda, sannan ta biya masa kuɗin shekarun da zai yi har ya gama makaranatar kamar yadda ta yi wa Rhodan ita ma, don tace akwai mutuwa, ba ta son ta mutu ta barsu cikin wani hali. Kullum da safe Maman Rhoda za ta haɗa kayan ƙosanta. Kuma tare da su Zaid ɗin take tafiya, idan suka je suka aje mata kayanta a rumfar da ta saba yi, sai su wuce makaranta idan a cikin sati ne. Bayan sun taso kuma kai tsaye can rumfar tata za su wuce, ba su suke dawowa ba sai rana, idan sun dawo da rana za su zauna su huta, idan suna da wani aikin yi su yi, idan kuma ba su da shi sai su hau aikin haɗa ƙosan yamma. Yamma na yi za su ƙara komawa, ba sa dawowa sai wajajen sha ɗaya, wani lokacin ma Rhoda tun a can take fara bacci, sai dai Zaid ya goyota su dawo gida. Zaid ya sake da su sosai, ya na rayuwa cikin farin ciki, dan Maman Rhoda ba ta rage shi da komai ba, ko azumi ne zai
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112