Chapter 64
Chapter 64
wanda ya yarda” Har yanzu dai wannan shiriritar na nan, kuma kafin yace a'a, har ta kama hannunsa ta shiga jansa, sai ya riƙe kalamansa ya shiga bin bayanta. “Kai shashashu! Na ce muku an min aure kun musa ko? To ga ku ga mijinawa, sai ku tambayeshi ku ji!” Abun da ta faɗi kenan a class ɗin nasu cikin ɗaga murya, kasancewar lokacin break ne, kowa na harkar gabansa, ido ya dawo kansu gaba ɗaya, sai kallon kallo ake, wasu na mawa mijin Mishal ɗin kallon sani, don ya na musu kama da wannan me sharar, sai masu masa kallon sani, saboda kullum idan an tashi suna ganinsa tsaye a tsallaken makarantarsu, wasu kuwa ma basu san shi ba. *No. 213, Naf belly, Asokoro, Abuja.* “Wallahi Aliyu ba ni da masaniya kan abun da su Karima suka aikata!” Anna ke faɗin hakan cikin hawaye, bayan da Kuliya ya zo ya na sanar da ita haukan da Karima da kuma Siyama suka je gidansa suka aikatawa Mishal. Kuliya ya kamo hannayenta ya riƙe. Bayan ya bar Brickhall kai tsaye gidan Annan ya nufo. “Na sani Anna. Na san ba za ki aikasu su yi wa matata haka ba, amma ina son na sanar da ke da ki jawa kowaccensu kunne, kan kada su ƙara taka ƙafarsu cikin gidana, jiya ma girmanki da darajarki suka ci, ba dan haka ba Wallahi ba zan barsu ba” Anna ta share hawaye. “Ba komai Aliyu, tashi ka tafi aikinka, zuwa yanzu na san ka makara, ka je kawai, ni na san matakin da zan ɗauka!” Ya karkatar da kansa gefe. “Ba za ki dena kukan ba?” Anna ta ɗan yi murmushi tana share wani hawayen. “Na dena, ka je kawai” “Shikenan” Ya faɗi ya na miƙewa, har ya fice Anna na kallonsa, ta san abun da za ta yi. Don ta zubawa su Karima ido suna ta haukansu ba wai don ba za ta iya taka musu birki ba ne, ba ta san cewa haukar tasu ta ƙamari ba, amma ba komai, Allah ya kaimu gobe, za ta yinwa tufkar hanci. *Vinca Hospital, No.12, Remkom street, Kubwa, Abuja.* Da gudu wata nurse ta fito daga wani ɗaki da aka kwantar da wata mara lafiya da ta baƙunci asibitin nasu a safiyar yau, hannunta na dama ɗore a bakinta, a ƙoƙarinta na tare kukan dake son cin ƙarfinta, ta jingina da jikin bango tana kallon ƙofar ɗakin, a hankali ta zame zuwa ƙasa, kukan da take ta yunƙurin riƙewa ya fito da ƙarfinsa. Tun da uwarta ta kawota duniya ba ta taɓa ganin tashin hankali irin wanda ta gani yau ba, ta na jin labarin fyaɗe, amma ba ta taɓa ganin wanda aka yi wa fyaɗe ba sai yau, an ce mata idan ta fara aiki sai ta gamu da abun da zai sa ta kuka, a wancan lokacin da aka faɗa mata dariya ta yi, don ita ba ta hango yiyuwar hakan ba, sai a yau ta yarda da abun da aka faɗa mata, kuka take sosai har ta na dafe ƙirjinta. Ƙofar ɗakin ce ta buɗe, likitan da suka shiga tare da shi ya fito ya na sharar ƙwalla, kafin ya kalli nurse ɗin, shi kansa da ya kwashi tsawon shekaru ya na aikin bai taɓa ganin abu makamancin wanda ya gani yau ba, bare ita da ta ke sabuwa a aikin. “Ke Sakina! lafiyar ki kuwa?” Wata ƙawarta ta tamabaya, a sanda ta biyo corridorn ta ga ƙawar tata zaune a ƙasa tana kuka kamar wadda aka yi wa mutuwa, juyawa ta yi ta kalli likitan, shi ma duk jikinsa ya yi sanyi, kansa a ƙasa kamar da aka ce shi ne ya aikata fyaɗen. Hannunta ta kai ta kamo ƙawar tata tana miƙarta, tare da share mata hawaye, amma Sakinan sai ta ƙwace fuskarta ta na komawa gefe. “Dan Allah Kausar ki bar ni na yi kuka. Bar ni na koka da abin da na gani. Kausar wasu mazan ba su da adalci, ba su da tausayi!” Ta ɗaga hannunta tana nuna mata ƙofar ɗakin. “Shi ga ki ga abun da suka yi wa wata yarinya. A shekaru dai na san yarinyar ba za ta wuce 19 ba, amma ki je ki duba ki ga yanda suka mata fyaɗe cike da rashin imani, mutum biyar Kausar, mutum biyar ko sama da haka ne suka haike mata!.Kuma ba su barta da wannan tambon ba, sai da suka ƙara mata da wasu raunuka a jikinta, gefen fuskarta da kuma kanta duk sun fasa mata, yanzu haka yarinyar ta shiga doguwar suma!” Ita kanta Kausar ɗin sai da gabanta ya buga da mugun ƙarfi, don za ta iya cewa wannan ɗin sabo abu ne da ya shigo asibitin nasu. “Me ya sa Kausar?. Me ya sa mu ba mu da 'yanci?, Kowa sai ya taka mu ya wuce yanda yake so. Me ya sa wasu mazan ba sa ganin mata da kimi?. Me yasa?... Sai zuwa yaushe ne za mu tsira?, sai zuwa yaushe?!”. *T.O.C Douglas Crescent, Kaura District, Game Village, Abuja* RAJA POV. Zaune yake a ɗakinsa, ya yi tagumi da duka hannayensa biyu, abun duniya ya bi ya isheshi, musamman yau da ya ga Rabi'a ba ta zo ba, abun ba ƙaramin ɗaga masa hankali ya yi ba, shi fa burinsa shi ne ya samu ya ganta don ya mata bayani, zai gabatar mata da kansa a ainahin yanda yake, zai faɗa mata gaskiyar komai a kansa, amma yau haka ya ƙaraci tsayuwarsa a ƙofar gate ɗin ba tare da ya ga gilmawarta ba. Ƙofar ɗakin aka buɗe, sannan Rhoda ta shigo hannunta tiƙe da wayarsa. Kansa kawai ya ɗaga ya kalleta ya na ɗaga ƙafaɗarsa ta dama. “Alhaji Bala ne yake ta waya. Yace ya na buƙatar kayansa cikin gaggawa” “Mtswwww!” Ya ja tsakin ya na kawar da kansa, shi ba ta Alhaji Bala yake ba, don matsalar Alhaji Bala sifili ce a wurinsa, babba kuma shirgegiyar matsla gareshi ita ce RABI'A!. Ganin hakan ya sa Rhoda zama kusa da shi, sannan ta dafa ƙafaɗarsa. “Na san halin damuwa da kake ciki, amma ya kamata ace ka sameta ku yi magana, ka faɗa mata gaskiya, wata ƙila ta saurare ka” Fuskarsa ya shafa da hannayensa. “Yau ba ta zo ba fa” Ya faɗi cikin wata murya me sanyi. “Wata ƙila ta zo, ta ɓoye ne kawai dan kada ka ganta” Da sauri ya ɗago kansa ya kalleta, ƙwarai, hakan za ta iya kasancewa, amma me ya sa shi bai yi tunanin hakan ba?. “Ki na ga zan iya shiga cikin makarantar?” “Me zai hana?” Sai ya gyaɗa kansa, ya na hangowa kansa mafita a cikin kalaman Rhoda. *No.181, Guzape, Abuja...* *07:00 PM.* MISHAL POV. Tsaye take a kitchen tana juya stew ɗin da take dafawa, duk da yau girkin a makare take yinsa, saboda makarar da ta yi wurin dawowa gida. Ba tare da ta san lokacin da ya shigo ba, ta ji muryarsa a bayanta. “Ana san magana da ke!” Da sauri ta juyo ta kalleshi, ya na tsaye daga bakin ƙofa, kallonsa da ta yi a yanzu shi ya tuna mata da shirman da ta yi masa yau da safe a school ɗinsu, don haka ta yi ta nuna
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112