Chapter 87
Chapter 87
yake ba, hatta da baccin dare ba ta samu ta yi, ko na rana ma a firgice take yinsa, duk da ba wai haɗuwa suka yi ba, dan tun bayan zuwansa ba su haɗu ba, kawai de ta na jin tsoron abun da zai je ya zo. Ilai kuwa, yau suna zaune sai ga kiran Baban ya risketa, kan ta zo ya na san ganinta, kuma ta na zuwa suka tarbeta da maganar auren Zaid, shi ne ta musu shiru ta kasa cewa komai, to me za ta ce wai?, tace musu shi ɗin da suka ƙwallafa rai a kai ba mutumin kirki ba ne?, ko ta yi wa kanta ƙarya tace bata san aurensa?. Haƙiƙa ta ga farin ciki a idon kakansu, ta ga farin ciki a idon Hajiya, kuma ta ga farin ciki a idon kowa na gidan, don kwana uku kenan da zuwan Zaid ɗin, amma kamar yau ya zo, sai nan-nan suke da shi. Ta tabbatar da idan har ta nuna ƙin amincewarta da auren nan, babu wanda zai ƙara kulata, babu wanda ma zai ƙara yin alfahari da ita a gidan. Kuma ita kanta ta san cewa tan na son Zaid, amma halinsa ne kwata-kwata ba ta so, mutum fa?! Mutum ta ga ya kashe a gabanta, ran mutum ta ga ya ɗauka kamar wani kiyashi. Sai de kuma duk da haka babu komai, za ta jure komai a kan ahalalinta, wata ƙila ita ƙaddararta ce ta zo a haka, Allah ya riga ya tsara cewar har ta koma gareshi ba za ta taɓa jin daɗin rayuwa ba, ko wani jin daɗinta na duniya ƙayadajje ne. Kanta ta ƙara sun kuyarwa kamar ɗazu, ta kasa furta komai, hakan ya sa Baba fahimtar inda ta dosa, tana san auren, amma wata ƙila kunya ce ta hanata furta hakan. “Na gane.... Ki je ki fara shirye-shirye, dan nan da sati huɗu kema za'a ɗaura aurenki tare da na 'yar uwarki Nafisa!” *Bayan sati huɗu...* *Wakili Family House, Unguwar Jama'are, Haɗejia* Ta ko wani ɓangare na gidan a cike yake maƙil da jama'a, ko ina ka kalla jama'a ne fal, kowa sai kai kawo yake ana ta hidimar biki, domin kuwa yanzu-yanzu aka dawo daga ɗaurin auren jikoki uku na gidan, hakan ya sa gidan ya cika fal da jama'a. Saboda wannan aure gidan har sabon fenti aka sake masa, babba da yaro na wannan ahali na cikin farin ciki. Daga can ɓangaren samarin gidan kuwa, Zaid ne tare da samarin gidan, jiko da 'ya'ya, wasu ma bai sansu ba a cikin wata ɗayan, sai yau yake ganawa da su, kuma a yau din ne yake ƙara tabbatar da girma da kuma yawa irin na ahalin nasu. Daga can gefen kuwa Jagwado, Alandi da Zuzu ne sanye cikin manyan kaya, kai ka rantse da Allah na gari ne, yanda suka haɗe cikin manyan kaya sai zare idanu suke, kowa ya zo sai ya tambaya su waye su? Zaid ne yake amsawa da abokansa ne. Allah ya sani, ba ƙaramin farin ciki yake ciki ba yau, a yau din nan ya mallaki Ammata a matsayin matarsa, a yau ɗin nan ya zama cikakken mutum, shi kansa ya kasa yarda, wai shi da ya saba rayuwa shi kaɗai, shi ne yau ya wayi gari ya ganshi kewaye da tarin ahali masu matuƙar ƙaunarsa, banda matar da suka ɗauka suka ba shi, har auren gata suka masa, dan kuwa babu wata wahala da aka barshi ya yi a auren, Baba da su Kawu Abdullahi su ne suka ɗauke masa komai. Lokacin da ya koma Abuja ya siyi wani kyakkyawan madai-daicin gida, wanda yake da niyyar aje Rabi'a a ciki, ya na shirin siyan kayan furnitures Kawu Abdullah ya dakatar da shi da faɗin su ne za su yiwa 'yarsu kayan ɗaki, kuma hakan aka yi, don a jiya aka cika gidan da kayan furnitures da kuma na kitchen, da ma duk wani abu na buƙatar gida. Kuma hatta da sadaki Baba ne ya biya masa, shi kansa ba zai iya misalta kalar farin cikin da yake ciki ba, babu abun da zai ce sai godewa Allah, domin kuwa ita ma Rhoda ya na gab da aurar da ita, saboda sun riga da sun ɗinke da Zakar, hujjojjin dake hannunsa kawai ya rage ya miƙa, da zarar ya miƙa su za'a kama Alhaji Bala, kuma kamar yanda suka yi da Rhoda daga zarar an kama Alhaji Bala za ta musulunta. Sannan sun yi magana da Kawu Abdullah kan daga zarar Rhoda ta musulunta za ayi aurensu da Zakar ɗin. Don haka farin cikin da yake ciki ba me misaltuwa ba ne, baki ya yi kaɗan ya faɗeshi, sai dai kawai ya ci gaba da godewa Allah. RABI'A POV. Daga ɓangaren Ammatan Raja kuwa, duma suna can nasu ɗakin ana wa amaren kwalliya, cikin wata ɗayan ba ƙaramar rama ta yi ba, don har mutanen gidan sun fara zargin ko auren ne ba ta so, amma ta nuna musu ba haka ba ne. A can ƙarƙashin zuciyarta kuwa tunanninnika ne birgit ta ko ina, ita kanta a yanzu ba za ta iya cewa ga takamemen abun da yake damunta ba, amma ta san cewa ba ta jin daɗi, duniyar ba ta mata daɗi sam. Don har zargin wannan auren take, tun bayan rabuwarta da Zaid a Abuja ba su ƙara magana ba, hasali ma rabonta da shi tun ranan da za su islamiyya ta hangeshi shi da su Yunus suna hira, bayan nan ba ta ƙara saka shi a idonta ba, idan za ta ce ga abun da ya ramar da ita to har da kewarsa ma za ta iya shigowa ciki, ta na son ganinsa, ko da faɗa ne ma su ɗan yi, amma wannan zaman nesan ba ya mata daɗi. “Kai! Amma fa kin yi kyau Rabi'a” Cewar Rhoda, a sanda aka gama ɗaura mata ɗankwalin farin leshin da suka yi ankonsa ita da Nafisa, kanta ta kalla a mudubi. Tabbas ta yi kyau, dan hatta da wannan tabon yankan na gefe fuskarta an ɓoye shi da hoda, kwalliyar ta bal'in hawa fuskarta. Hannunta ta kai kan ƙashin wuyan da ta yi a kwanankin, ta ɗan ja guntin tsaki ta na jan wayarta. “Kai ku yi sauri ku fito ga masu ɗaukar hoto nan sun zo” Cewar Jidda, a yayin da take shigowa ɗakin da gudunta, ta ci uwar kwalliya kai kace ita ma amaryar ce. “Dan Allah Ummi ki yi sauri ki gama min” Momi ta faɗa a sigar magiya, ta na kallon me kwalliyar. “To” Me kwalliya ta amsa, a gefe guda kuma Rhoda da Rabi ne suke ɗaukar hoto a waya, daga can kuma Kairiyya ce takewa Nafisa da Kulsum hoto a waya. Haka suka gama shiriritarsu kafin suka fita. Dangi da jama'ar da aka gayyata haka suka riƙa zuba musu ruwan hotuna ana ta Allah sanya da alkairi. Da yamma kuwa walima aka haɗa musu, amma ba su yi dinner ba, dan Baba yace ba za'a yi ba, duk da suna son yi haka suka haƙura saboda babu yanda za su yi. *10:30 PM.* “Ke wai ina za ki kai ni ne?” Rabi ta tambaya tana kallon Jidda dake ta janta tun ɗazu, tafe suke a harabar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112