Skip to content

Chapter 21

Chapter 21

Labarinsu Book 1 Complete Hausa Novel 1,195 words 0 views Progress saved
Download Book

a taƙaice, duk kuwa da yasani ɗin. MISHAL POV. Shekaran jiya suka dawo daga Maiduguri. Kuma a jiya ne Abubakar ya kaita aka cire mata braces ɗin dake haƙwaranta. Ba ƙaramin daɗi ta ji ba a sanda aka rabata da su, don Allah ya sani, ba ta san su, ga shi dai ita ta ce a saka mata su, amma daga baya sai suka gundureta. Zaune take a comound ɗin gidan, suna hira ita da Shatu, yayin da Daala ke zaune a gabanta. Akasarinta hirar tasu a kan Maiduguri ne. Daga can saman benin gidan kuwa, Hajjara ce ke leƙowa ta window tana kallon Mishal ɗin. Cike da tsana da kuma alwashi. Ta ɗaukawa kanta alƙawarin ganin bayan Mishal, ba za ta huta ba sai ta ga tabbatuwar hakan. Ko da za ta ƙarar da duka abun da ta mallaka ne sai ta aikata hakan. Abun da ba ta sani ba shi ne; ƙaddarar da Allah ya hukunta faruwarta ta kusa afkuwa, kuma tun kafin abun da ta tsara ya kai ga gaci komai yake wargajewa. *Unguwar Rafin Cinnaka, Suleja, Niger state* “Yanzu miye abun yi ?” Muryar Habiba ta tambaya, yayin da take zaune a falon gidan yayarta hajiya Inno. Hajjiya Inno ta yi murmushi. “Yanzu abun da ya kamata shi ne kawai ki kawo wani abun, a kai masa a matsayin kafin alƙalami... A fara aiki a kan Saratun, na faɗa miki aikinsa ba ƙaramin ci yake ba... Da zarar ya yi aikin ina mai tabbatar miki da ko sati ba za'a yi ba za ki ga samari sun fara sintiri a ƙofar gidanki...” Habiba ta ɗan yi dariya. “Haka nake san ji, dan Wallahi har ga Allah na gaji da ganinta a gidan nan haka... Ita ma idan ta ɗan samu ta yi auren nan ai yafi ko?” “Hakane” “To sai batun Mama, yarinyar nan so take ta fara fin ƙarfina, wai rannan dan na mata magana kan ta ɗan yafita min wani abu sai ta hauni da faɗa?!” “Mtswwww!, Wallahi kuwa Habiba da kin bada mata, har ita ta isa dan ub*nta ?, Idon ki za ki murje ki nuna nata cewar ke ce uw*rta, ba ita ta haifeki ba!” Habiba tace“Hummm!” cikin taɓe baki. “Gaakiya ba zan iya takurata ba, dan baki san yanda nake san Mama ba ne, sam ba na so ranta ya ɓaci Wallahi, ke dai kawai kawo wata shawarar” Cike da mamaki Inno take kallonta. Can kuma sai ta taɓe baki tace. “To ai ita ma nata lamarin mai sauƙi ne, sai amata na kasuwar samarin, alhajan nan na abuja su yi ta kai kawo a kanta, sannan a rufe mata baki, duk sanda za ki mata maganar kuɗi ta miƙo miki kawai...” Habiba ta saka dariya har da shewa, tana jin wani abu na washewa daga ranta. “Wallahi Yaya Inno abun ne da yawa, kin ga na Zainab ma abun yaƙi daɗi, kar ki ga yanda bawan Allahn nan ke gasa mata aya a hannu” Inno ta kuma yin dariya. “Shi ma nata mai sauƙi ne... Habiba idan fa da kuɗin ki shikenan, duk wata matsala taki ta kau, in dai za ki bada shikenan...” Ta sauƙe ajiyar zuciya. “Sai kuma na wannan sheg*yar yarinyar, kinbga fa duk dan na tagayyara rayuwarta na sa Ɗan Lami ya dawo da ita nan garin, toh!, ta taggayar ɗin, amma ni ba haka na so ba....Na fi so ta ƙare da cikin sh*ge, shi ne fa yasa ma na aikata akatau, amma dai har yanzu shiru ki ke ji...” Dariyar da Inno ta saka ce ta sata yin shiru. “Wai ni Habiba yaushe kika yi sanyi ne ?, ina Habibar da na sani ta da ?, wai duk kin yi sanyi kin zubar da makaman yaƙinki ?, yo in ba haka ba ai wannan ba wata matsala ba ce, ke dai zo ki ji” Ta ƙarashe tana matsawa kusa da Habiban, Habiba ta miƙa mata kunne. A take Habiba ta saka shewa tana tafa hannu, bayan da ta gama sauraron abinda Innon ta raɗa mata. “Ai kuwa ko miliyan nawa zan sadaukar a kan wannan aikin, in dai har... Zan ga bayan jinin Maryam a duniyar nan!” ______________ _Wai Siyama ce take san Kuliya😂... Wani ya bata shawarar kada ta fara tafiyar dare ba maraki, ah to, kar ta ce ba mu gaya mata ba_ _Shin wata ƙaddara ce wannan ke shirin faruwa ?_ _Ya za ta kaya tsakanin RAJA da RABI'A ?_ _Kun ji alƙawarin Hajjara a kan MISHAL?_ _Sannan ga Habiba ma a nata ɓangaren, me kuke ganin tana shiryawa ?_ _Kamar fa an bawa Kuliya assignment ɗin da zai sauya rayuwarsa, sannan Chidera ya ce 'yan dabar yau suka sauƙa a garin abuja....Kada ku ce min su RAJA ne😨...._ #Labarinsu #SalmaAhmadIsah #Taurariwriters °°°°°°°°°°°°°°°°°° *LABARINSU* *©SALMA AHMAD ISAH* *TAURARI WRITERS* *06* ~~~ *The wrong one will find you in peace and leave you in pieces. The right one will find you in pieces and lead you to peace.* *** *Shekara ta 2000* *Kano.....* A hankali Zaid ya juya ya kalli ƙaninsa Aliyu, wanda har zuwa lokacin yake ta risgar kuka. awa biyar kenan da aka kashe wutar da ta kama a gidansu. Wutar da ba ta bar musu komai ba, ciki kuwa harda mahaifiyarsu. Kuma har zuwa lokacin, suna sanye da wannan uniform ɗin islamiyyar, yayin da ƙonnaniyar gawarbmahaifiyarsu ke rufe a gabansu. Zaune suke a ɗakin da aka ajeta bayan da aka samu aka kawota asibiti, kuma tun kafin su kawo asibitin jama'ar da suka ɗaukota ke faɗin ai ta cika. Shi ma kansa Zaid ɗin so yake ya yi kukan, amma ya kasa. Bai san ina za su je ba, bai san ina za su koma ba, bai san kowa nasu ba, kuma Momman nasu ko ƙawa ba ta da ita, bare su ce za su je wurinta. Hatta da asalinsu basu sani ba, bayan ce musu da ta yi ita 'yar haɗejia ce, ba ta ƙara ce musu komai a kan asalinsu ba. “Aliyu....” A hankali nitsataiyar muryarsa me cike da kamewa ta kira sunan, yayin da lumaassun idanuwasa masu ɗauke da gray ƙwaya suke kallon Aliyu. Aliyun ya juyo ya kalli yayansa. Kuma har a lokacin kuka yake. Lokacin ƙarfe takwais na dare da ɗorariya, jama'ar da suka kawo su asibitin ma tafiyarsu suka yi bayan an tabbatar musu da rasuwarta. “Ba mu yi sallar magrib ba... Ga isha ta kawo kai” Da ƙyar sautin muryar tasa ke fita, don mai sauraro ma zai iya tsintar ɗacin da muryar tasa ke ɗauke da shi, ba zai ce ya gama mallakar hankalinsa ba, amma ya san cewa duk wanda ya mutu ba ya dawowa. Ya san cewa yanzu su da ganin Mommansu wata ƙila sai a lahira, sun zama marayu, yanzu su marayu ne waɗanda basu da kowa sai junansu. Babu wanda zai taya su kukan rashin da suka yi. Ba tare da Aliyun yace komai ba ya miƙe tsaye, shi ma Zaid ɗin miƙewar ya yi, ya dafa kafaɗarsa suka fara tafiya zuwa waje. Kuma har lokacin Aliyun na kuka, shi kuma Zaid ɗin sai rarrashinsa yake. A masallacin asibitin suka yi sallah. Sannan suka fita wajen asibitin. Dan Zaid ɗin ya tuna da ɗari biyun da

Table of Contents

Chapters

112 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112