Skip to content

Chapter 81

Chapter 81

Labarinsu Book 1 Complete Hausa Novel 1,205 words 0 views Progress saved
Download Book

kasa ganin gaskiya?. Wani abun farin cikin ma shi ne; da bata faɗa masa cewar shi ɗan uwanta ba ne, wannan shi ne kaɗai arziƙin da aka yi. Ta raya hakan a ranta, don ita ta manta da maganar da ta faɗa masa a sibiti. Haka suka yi kiɗansu suka yi rawarsu, amma ba ta ƙara cewa kanzil ba, har suka babbata haƙuri, kawu Abdullahi ne yace ta shirya zuwa gobe zai kaita a mata gwaje-gwaje, sai a lokacin ta yi magana, ta sanar masa da cewar duk wasu gwaje-gwaje da suka dace babu wanda ba a mata ba, amma yace shi bai yarda ba, kawai ta shirya zai kaita a sake mata wasu, ba ta ƙara masa musu ba tace to, sannan ta miƙe ta koma cikin gidan. Kai tsaye ɓaangaren kakarsu ta yi, inda ta san 'yan matan gidan suna tare a can, dan a dai-dai lokaci irin wannan a can suke taruwa. Kuma kamar yanda ta ayyana a ran nata sun taru a can ɗin. 'Yan mata shida ne sa'o'inta a gidan, Momi, Nafisa, Fati, Jidda, Kulsum da Kairiyya, su na ganinta su ka yi shiru, kowa ya zuba mata ido ya na kallo, dan kaf cikinsu babu wanda ya san da zuwanta, a sanda ta shigo garin ma suna islamiyya. Gaba ki ɗayansu so suke su ganeta, kammaninta na musu kama da na wata da suka sani, kallon ƙurillar da ta ga suna mata ya sa tace. “Ya da kallo haka 'yanmatan Waliki family?” Kusan a tare suka fashe da dariya suka iyo kanta. A dai-dai wannan lokacin kakarsu ta fito daga ɗakinta ta na ɗingisa ƙafa, kujera ta samu zauna ta na kallonsu. “Rabi'a?, wai yaushe ma kika zo garin?” Cewar Kulsum ta na dariya. Rabi ta zauna a kujera ta na faɗin. “Ɗazu da yamma, kuna islamiyya lokacin” “Wayyo Allah, wallahi na ji daɗin zuwanki, kusan shekara biyar fa rabonmu da ke” Cewar Fati ta na matsawa kusa da ita. “Ke Allah ya yi da ke kina nan za ayi bikin Nafisa” Kairiyya ta faɗa, baki buɗe cike da mamaki Rabi ta kalli Nafisan da ta kawar da kanta, saboda Hajiya kakarsu dake wurin. “Wai dan Allah?” “Wallahi kuwa, nan da wata ɗaya da sati ɗaya” Jidda ta amsa mata. “Ke Rabi a ina kika ji wannan raunin na fuskarki?” Momi ta tambayeta, Rabi ta kai hannu ta shafa gefen fuskarta na hagu, sai da ta haɗiye wani abu sannan tace. “Haɗari ne... Kai ni yanzu ku ba ni labari, ya ake ciki ?” Daga haka suka shiga hira a kan batun bikin, suna bawa Rabin labarin yanda suka tsara bikin, da yanda zai kasance, har kusan ƙarfe goma suna can, dan abincin dare ma tare suka ci. Kasancewar 'yan matan su duka ɗakinsu ɗaya, ya sa ita ma ta kwana a cikinau, dan dana tun can tare auke kwana, gadon Rabin ma na da yana nan, kuma yanzun ma a kansa ta kwana. *T.O.C Douglas Crescent, Kaura District, Game Village, Abuja.* RAJA POV. _🎶It was just two lovers..._ _Sitting in the car, listening to blonde_ _Falling for each other_ _Pink and orange sky_ _Feeling super childish_ _No donald glover🎶..._ Waƙar dake tashi kenan a cikin sifukun gidan, wanda Raja ya ƙure volume. Tsaye yake daga gaban mirror, ya na taje sumar kansa, sanye yake cikin wata ash shadda, a hankali bakinsa ya ci gaba da biya waƙar Golden hour ɗin dake tashi a falo. “I was all alone... With the love of my life... She's got glitter for skin... My radiant beam in the night... I don't need no light to see you... Shine... It's your golden hour...” Sai kuma ya yi shiru ya na kallon kansa a mirror, yayin da ya aje matajin hannunsa, bayan wani lokaci me tsayi yau shi ne sanye da manyan kaya, ya daga kafaɗarsa ya na murmushi, ya gyara wuyan rigar jikinsa, ya ƙara fesa turare a jikinsa, sannan ya finciki hularsa ya fito. “Huh?! Dude? Yau ina zuwa?” Cewar Rhoda kenan, yayin da ta fito daga kitchen, hannunta na dama riƙe da plate, Raja ya kama kumatunanta ya na ja. “Zance zan je” Rhoda ta shafa kumatunta da ya saki da hannunta na hagu. “Guys, ku shigo ku ga ikon God!” Kiran da ta ƙwalawa su Jagwado ne ya sa suka afko cikin gidan babu shiri. Kallon Rajan su ma suka tsaya suna yi, a karo na farko tun bayan saninsu da Rajan da kuma Rhoda, ba su taɓa ganinsu da mabanbantan kaya ba, a ko da yaushe kaya kala ya suke sawa, sai yau. “Allah de ya biya oga Raja, ina za ka fasa haka?” Alandi ya tambaya. “Zance zan je” “Kutumar dumadu, Kaga Oga Raja namu, Allah ya biya, gayu, oga fa ya rufta ramin ƙauna Allah Wallahi” Cewar Zuzu ya na wani ɗaɗɗaga hannu. Raja ya yi murmushi ya na girgiza kansa. “Wai Zuzu ban hanaku magana irin haka ba?” Zuzu ya shafa kansa ya na kallon ƙasa. “Sabo ne oga Raja, amma za mu dena da yardar me duka” ya faɗi muryarsa babu wani banbanci da ta ɗazun. “Ku fa?” Raja ya tambaya yana kallon sauran. “Aah, ai muma hakan take oga, ko ya kuka ce gayu?” Alandi ya faɗi ya na kallon su. “Haka ne” Jagwado ya amsa. “Na zo na raka ka?” Rhoda ta faɗi ta na aje plate ɗin hannunta, wanda ke ɗuke da alale. Raja ya maka mata harara. “Wa za ki bi?... Kama hanyar ki can joo!”. *Unguwar Madallah, Suleja, Niger State.* Da gudu Fatima ta shigo gidan har tana bangaje Saratu da ta fito daga banɗaki. “Ke Fatima mi ye hakan?” Inaa, sam ba ta tsaya ba sai da ta dangana da ɗakin Habiba. “Ke dallah mi ye hakan za ki faɗo kaina?” Habiba ta tambaya ta na miƙewa. Fatima ta dafe ƙirji ta na zaro ido, hannunta ta ɗaga tana nunawa Habiban ƙofar ɗakin. “Wa... Wani na... na ga a waje... Kamarsu ɗaya da... Da Rabi!” Wani irin juyi kayan cikin Habiba suka yi, don a sanda fatiman ta ambaci kamar mutumin da ta gani da Rabi, ƙwaƙwalwarta ta hasko mata 'yan uwan Maryam na Haɗejia. To ko su ne suka zo kamata ?, wata ƙila Rabi ta sanar musu da duk irin abubuwan da ta mata, shi ne suka zo dan su kamata. Muƙut!, ta haɗiye yawu, tunawa da ta yi da labarin irin kuɗin baban Maryam ɗin da aka bata. Ba shiri gumi ya shiga tsatsafo mata, cikinta har wani ƙugi yake. Sallamar da Saratu ta ji a waje ya sa ta leƙa, kasancewar akwai hijabi a jikinta. Ita kanta sai da ta firgita, ganin wani mutum sak Rabi, tsaye a soron gidan nasu, amma sai ta ɓoye tsoronta ta amsa sallamar tasa. Ba tare da ta tambayeshi wa yake nema ba, ta masa lamini da ya shigo cikin gidan. Wata kujerar roba ta bashi, tace ya zauna a kai. Ya na zama a kan kujerar Habiba ta bankaɗo labulai ta fito, Fatima na biye da ita. Curko-curko suka yi daga bakin ƙofar ɗakin Habiban suna kallon ikon Allah. Saratu ce ta kawo masa ruwa, sannan ta zauna suka gaisa. “Am... Rabi'a nake nema” Wani irin ƙara cikin Habiba ya saki, da saida

Table of Contents

Chapters

112 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
  112. 112 Chapter 112