Chapter 20
Chapter 20
da rannan Habiba ke sanar mata da cewa Babansu ya siyar da shi. Don wasu daga cikin kadarorin mahaifiyarta da aka raba gado aka bata, 'yan uwan mahaifyarta suka danƙa su a hannun Ɗan Lami, sauran kuma suna wurin dangin nata. “Ke!, me ki ke a nan ?! Bar nan dallah!” Muryar ɗaya daga cikin masu gadin makarantar ta katseta a tsawace. Shikenan kuma, da ma ta jima da sanin cewa shi talaka ba a bakin komai yake ba. Ba shi da wata kima ko dajara a idon mutane. Ba ta ce masa komai ba, ta juya ta fara tafiya. Ko jikin store ɗin da ta sabba zama ba ta kai ba aka kaɗa ƙararrawar tashi. Hakan yasa ta fasa zuwa store ɗin, kai tsaye ta yi hanyar fita daga makaranatar. Tun da an tashi to ita ma babu abun da za ta zauna ta yi. Tana tafiya ta na kwatanta yanda wasan da Yaya ya bata labarin za'ayi zai kasance, yace mata yau akwai wasa tsakanin arsenal da fc Barcelona. Shi yasa take ta kwatanta yanda wasan zai kansace. Ba tare da ta an kara ba wani me mota ya iyo kanta, ƙiris ya rage bai kaɗeta ba, amma duk da haka sai da ta faɗi. RAJA POV. A yau suka sauƙa a garin Abuja, bayan duk wasu maganganu da suka yi da Garuje, sai yau Allah ya hukunta tahowar tasu. Duk da ba shi kaɗai ya taho ba, ya taho ne tare da duka yaransa, Rhoda, Alandi, Zuzu da Jagwado. Dan su ɗin na amana ne, ba zai iya zuwa ko ina ba tare da su ba. _🎶.....It's something that i never, ever, ever had _ _I have never needed somebody🎶_ _But i wannan spend sleepless nights, and sleepy days with you.._ _With you, with you, you make me speechless...🎶_ A hankali waƙar sleepless nights ta Armaan Malik ke tashi a cikin motar tasa ƙirar Jeep. Raja ne ke tuƙa motar, yayin da Rhoda ke zaune a gefensa, Alandi, Zuzu da Jagwado na gidan baya. Rajan na sanye cikin wani blue jeans, da farar shirt dake ƙasan baƙar denim jacket ɗin da ya ɗora a saman rigar. Kuma sak kalar kayan dake jikin Rhoda ne. Don ita ce ta zame masa kamar abokiyar tagwaitakar tasa, abu ne mawuyaci su saka kaya da ban da ban. Kaya kala ɗaya suke sakawa, size ne kawai ke banbanta. Shi da Rhodan ne ke bin waƙar, Raja na yi yana murmushi, a hankali ya ɗaga kafaɗarsa ta dama. Kuma a lokacin abun ya faru. A lokacin ƙaddarar da ke jiransa a garin Abuja ta auku, wata ƙaddara da za ta tarwatsa komai, sannan ta saita wasu lamura. Kan motar ya juya dan shiga layin gidan da ya kama a KAURA DISTRICT.Wata yarinya ce tafe a gefen hanya, ba ya ce ya iya ganin fuskarta ba. Sai ganin wucewar wata baƙar mota ya yi da gudu, wadda ta so ta kaɗe yarinyar, duk da bata kaɗetan ba, sai ta kaɗata gefen hanya. Ba shiri ya taka birki. A firgice ya fice da ga motar, su Rhoda suka bishi da kallo su ma suna fitowar. Da gudu ya yi inda yarinyar take, sannan ba tare da jiran komai ba, ya kama hannun yarinyar ya ɗaga ta. “Sannu kin ji” Ya faɗa yana san kallon fuskarta, kuma sai aka yi sa'a ta ɗago da fuskar tata ta kalleshi. A lokaci guda zuciyarsa ta yi wani irin tsalle a ma'ajinta. Kamar zata fito daga bakinsa. Ba komai ne ya jawo hakan ba, face wata fuska da ya gani, fuskar sak irin ta mahaifiyarsa, fuskar sak irin ta ƙaninsa Aliyu, sannan fuskar sak irinta ce a tare da shi. Amma ta ya hakan za ta faru ?, ya aka yi yarinyar ke kama da su ?, wacece yarinyar ma ?, daga ina take ?. Kusan ƙamewar muntuna shida Rabi ta yi, a sanda ta kalli fuskar matashin da ya temaka ya ɗago da ita bayan kifawar da ta yi. Mamaki ne bayyane a fuskarta ita ma, kamar yanda yake kwance a tasa fuskar. Za ta iya rantsewa da Allah ta ga gilmawar mamakin a cikin idanuwansa. Ba ƙaramar kaɗuwa ba ta yi ita ma, ba dan kada ta yiwa kanta ƙarya ba, da sai ta ce wannan ya fi kama da mahaifiyarta fiye da ita. Dan ya fita farin fata, saboda ita ba wata fara ba ce sosai, ta ɗan kwaso baƙin Abbansu. Amma Ummansu fara ce sosai, kuma farinta sak irin na wannan bawan Allan ne, kusan rabin idanuwansa a lumshe suke, sannan ya kafeta da ƙwayarsu wadda ta kasance gray color. Ta sani cewa ko cikin 'yan uwanta na haɗejia babu mai kaka da wannan, duk da ba za'a rasa ba, amma dai wannan ba daga can yake ba, to kenan waye shi ?, daga ina yake ?, me yake a nan ?, kuma me yasa yake kama da Ummansu ?, don sai dai ta dangana kamar tasa da ta Ummansu ba tata ba. Mafarin komai kenan😎. *DSS Headquarter, Maitama Evenue, Abuja* KULIYA POV. “Aliyu, this will be your next assignment, ina so ka yi ƙoƙarin yinsa cikin taka tsan-tsan da kula, ka sani kuma nima na sani, a halin yanzu akwai masu farautar rayuwarka... Dan haka ka kula, coz this was the most dengerous assignment ever. Dan haka sai ka kula....” Chidera Kinsily ke koro masa wannan jawabin, yayin da yake miƙa masa wani file. Hannu bibbiyu yasa ya karɓi file ɗin. File ɗin da zai kai rayuwarsa zuwa wani mataki, file ɗin da zai sauya rayuwarsa, file ɗin dake ɗauke da matakin farko na sauyawar ƙaddararsa. Ƙaddarar da za ta tarwatsa komai, sannan ta gyara wasu lamuran. Chidera ya ci gaba da faɗin. “Case ne a kan wasu manya-manyan 'yan ta'adda da suka yi wa garin Abuja tsinke a yau ɗin nan... Ba ma so abun ya tafi da nisa, wannan file ɗin ɗauke yake da bayanin kowannensu, don haka kasan abun yi... Sannan idan kana so za ka iya neman temakon abokin Abubakar” Kuskure mafi girma kenan da ya zama sanadiyyar faruwar wannan ƙaddarar. Wata ƙaddara mai cike da tarin abubuwa, masu daɗi da akasinsu. A hankali Kuliya ya ɗaga kafaɗarsa ta dama, sannan ya ce. “Zan san abun yi sir” Kuskure na biyu kenan, wani babban kuskure da zai yi nadamarsa da farko, sannan daga baya ya dawo ya yi farin cikin ɗaukarsa. * “Shigo!” Muryar Abubakar ta faɗi daga cikin office ɗin. Bayan da aka buga ƙofar office ɗin nasa. Kuliya ya murɗa ƙofar office ɗin, sannan ya shiga ciki. A hankali Abubakar ya ɗago da kansa ya kalle shi. Kamar kullum sanye yake cikin baƙar suit, sai dai babu suit ɗin, waist coat ce kawai a saman baƙar oxford shirt ɗin dake jikinsa. Hannunsa na dama riƙe da file ɗin dake ɗauke da ƙaddararsu. Ƙaddarar da za ta sauya LABARINSU. “Sabon assignment ne, idan babu abun da za ka yi, sai ka taya ni...” Wannan dakkakiyar Muryar tasa ta faɗa. Kuskure na uku kenan. Abubakar ya yi murmushi yana aje ipad ɗin hannunsa. “Babu damuwa Dude, ai duk assignment ɗinka nawa ne... akan miye ?” Kuskure na huɗu kenan. “Ban sani ba, dan ban duba ba” Ya amsa shi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112