Chapter 86
Chapter 86
zuwan wannan Zaid ɗin yanayin ki ya sauya” Rabi ta sunkuyar da kanta tana kallon yatsun hannunta, amma ba ta ce komai ba. “Menene yake faruwa?. Ko bakya sonsa kamar yanda Hafiza tace?” Rabi ta yi saurin girgiza kanta tana faɗin. “A'a, ba haka ba ne. Ina sonsa, kawai de wata matsalar ce da ban” Jidda ta gyaɗa kanta tana dafa kafaɗarta. “Na gane, to Allah ya kawo miki mafita, ke de kawai ki yi addu'a... Kin ji?” Sai ta gyaɗa kanta kawai. Jidda ta ƙara dafa kafaɗarta, sannan ta miƙe ta koma gadonta. Rhoda dake kwance a gefen gadon Rabi ta yi murmushi ta na gyara kwanciyarta. #Labarinsu #SalmaAhmadIsah #TaurariWriter's ••••••••••• *LABARINSU* *©SALMA AHMAD ISAH* *TAURARI WRITERS* *22* ~~~ *Keep on letting your love shine...* *** RAJA POV. Zaune yake a falon kakansu wanda mutanen gidan ke kiransa da Baba, Baba Munzali da kuma Kawu Abdullahi ne tare da Baban. Kawu Abdullahi ne ya masa tambayoyi kan yanayin yanda rayuwarsa take a can garin Abuja da ya faɗa musu ya na da zama, sun masa tambayoyi sosai, kafin suka tambayeshi alaƙarsu da Rabi'a. “Na gamu da ita ne a hanyar makarantar da take zuwa aikatau, kuma daga haka ne muka soma soyyaya, har muka fahimci juna, giftawar wannan iftila'in ne ya kawo mana tsaiku” Kawu Abdullahi ya gyaɗa kansa a sanda Zaid ɗin ya kai ƙarshe a maganganunsa. “Ke nan ka san abun da ya faru da ita?” Kansa a ƙasa ya gyaɗa shi. “Na sani Kawu, dan ni ne ma da kaina na yi jinyarta a asibitin da aka kwanatar da ita” Baba Munzali ne yace. “Kuma kai yanzu kana santa a hakan?” “Sosai ma kuwa Baba, ina san aurenta a yanda take, abun da ya faru da ita ƙaddara ce,wadda ta wuce fata, kuma san aurenta da nake ne ya sa na biyota har nan...” Ko kafin wani a cikinsu ya sake cewa komai, wayar Zaid ɗin ta yi ringing alamun shigowar kira. “A min afuwa...” “Ba damuwa za ka iya ɗaga kiranka” Kawu Abdullahi ya amsa masa. Kansa ya gyaɗa ya na ɗaga kiran. “Ok” Kawai yace sannan ya katse kiran, cikin WhatsApp ya shiga, ya buɗe chat ɗin wani contact, a inda aka turo masa wani vedio, buɗe vedion ya yi, kafin a hankali ya matsa ya miƙawa Kawu Abdullahi wayar. “Ka duba ka ga” Kawu Abdullahi ya karɓa cike da mamaki, kafin ya danna play, vedion ya buɗe, sannan hoton Habiba dake garƙame a cell ɗin 'yan sanda ya bayyana, fuskarta ta ji duka ba na wasa ba, muryarta ce ta shiga fitowa raɗau daga cikin wayar. Hakan ya sa Kawu ya karkata fuskar waya zuwa ga su Baba dan su ma su gani. “...Ni ce na yi wa Maryam asirin da ya sa Ɗan Lami ya saketa, kuma ni ce na yi mata asirin da ya sakata jinya, har ta kai ga mutuwa, har ila yau ni na saka Ɗan Lami ya karɓo min Rabi daga wajen 'yan uwan Maryam. Har ta dawowa wuri na da zama, kuma... Kuma ni ce na yi wa Rabin asirin da zai sa idolan wani namiji ya kalleta zai ji sha'awarta, har aka samu wasu suka mata fyaɗe!...” Daga haka vedion ya tsaya cak, alamun dai ya ƙare ne. Cike da mamaki ko wannensu ya kalli Zaid ɗin dake durƙushe gabansu. “Kun gane ta?” Ya tambaya ya na kallonsu, don ya ga kamar ba su fahimci zancen da ake ba. Baki buɗe Kawu Abdullahi yace. “Na ganeta. Habiba ce... Abokiyar zaman Maryam” Zaid ya gyaɗa kansa. “Ƙwarai ita ce... A lokacin da na rasa Rabi'a, na sa aka kamata, don ta mana bayanin inda take, a memakon mu samo bayani kan inda Rabi'a take, sai muka samu wannan bayanin” Baba ya share ƙwalla ya na kallon jikansa, jini ba ƙarya ba, hatta da yanayin maganarsa irin na mahaifiyarsa ne, shi yanzu ba shi da wani fata godewa Allah, da kuma neman yafiyar Allah, kan zunubansa na baya. “Matso nan jikana” Zaid ya ɗaga kafaɗarsa ta dama ya na matsawa kusa da Baban da ya kira shi, kansa ya shafa ya na faɗin. “Allah ya mamka albarka, Allah ya ji ƙan mahaifiyarku.... Kuma ni da kaina na baka auren Rabi'a, ba za'a ɗau wani dogon lokaci ba, akwai bikin ɗaya daga cikin ƙannen naka da za ayi nan da sati huɗu, dan haka in Allah ya yarje mana tare za ayi da naku!” Wani abu ne ya shiga ratsawa tun daga kan Zaid har zuwa ƙafafunsa, farin ciki ya buɗe ƙofar zuciyarsa ya rufta, ƙaunar 'yan uwansa ta ƙara kama shi, a hankali ya kwanta a jikin kakansa ya na nemawa Momma da Aliyu rahamar Allah. * “Bros” Cewar Zakar ya na duban Zaid, wanda ke cire takalman kafarsa bayan da ya dawo daga wurin su Baba. Zaid ya amsa ya na cire takalman ƙafarsa. Tare da shigowa ɗan madai-dai cin falon samarin, ya zauna a kan kujera yana dubansu. “Ya ake ciki ne?” Sani ya tambaya. Zaid ya yi murmushi. “Baba ne ya bani aure...” Zakar ya aje mug ɗin hannunsa ya na zaro ido. “Ikon Allah... Wai da gaske?” Zaid ya yi murmushi ya na shafa kansa. “Da gaske ne mana, kuma kun san wani abun farin cikin ma?, tare da na ɗayar ƙanwar tawa za ayi!” “Wai auren Nafisa?” Auwal ya tambaya ya na zaro ido. “Ban san sunanta ba. Kawai de yace auren nan da wata ɗaya ne” “Gaskiya muna taya ka murna, amma ai kana nan har zuwa lokacin bikin?” Cewar Yunus. Zaid ya girgiza kansa. “Akwai wani aikin da ban ƙarasa ba a Abuja. So dole zan koma, amma biki saura sati biyu zan dawo” “Ni fa ɗan uwa, ina san wannan ƙanwar taka da kuka zo tare!” Zaid ya yi shiru ya na kallon Zakar dake wannan batu. “Rhoda?” Ya tambaya dan tabbatarwa. Zakar ya gyaɗa kai. “Of course ita, ina santa, and i mean it” “She is not musulim, ka bari ta musulunta tukunna” “Wai har sai ka jira?. To tun da me ya sa bata musulunta ba ?” Auwal ya ta baya ya na gyara zama. “Akwai abun da muke jira kafin faruwar hakan, amma ina da tabbacin lokacin shigarta musulunci ya kusa” “To Allah ya tabbatar, amma dan Allah kar ka bari a yanka ni, dan Wallahi ina santa” Zaid ya yi dariya ya na ɗaga kafaɗarsa ta dama. “Idan an yi auren Abuja za ka bita?” “Abuja kuma?” Zakar ya tanbaya ya na kallonsa. Zaid ya gyaɗa kansa. “Ƙwarai Abuja, ma aikaciyar DSS ce” “Jar uba! Kace ƙanwar taka me zafi ce” Zaid ya ɓata fuska, ya na kallon Yunus. “Ban san irin wannan abun Yunus” “Allah baka haƙuri, wasa ne” “Rabu da shi sirikina, zan maka maganinsa” Zakar ya faɗi yana hararar Yunus. “Har mun zama surukai kenan?” Zaid ya tambaya. “Eh mana, na ga dai kai ma ƙanwarmu zaka aura, ni ma kuma ka ga zaka bani ƙanwarka, mun zama surukai” Gaba ɗayansu suka sa dariya. RABI'A POV. “Kin yi shiru?” Cewar Baba ya na kallonta, ɗagowa ta yi yo da kanta ta kalleshi, yayin da take zaune a ƙasa daga gefensa. Allah ya sani tun bayan zuwan Zaid gidan nan hankalinta ba a kwance
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111
- 112 Chapter 112